Sashe 25
Juyin KwaÉ—o Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
“Lokacin da aka sanar mana da cewa mahaifina ya mutu ji na yi kamar ni ma zan mutu na bi shi. Har ina jin kamar na samu Safraz da Ammi Anser (Kawuna Anser) na ce da su su kwashe komai da muke da shi, amma su bar min Abi. Na ji haushi sosai lokacin da na fuskanci cewar a kan kujerar mulki suka kashe min mahaifina. Bayan kuma sun fara shirin ƙwace abin da yake nawa sai na ji cewar na rasa komai, wannan kujerar ita ce kaɗai abin da nake ganin cewa Abi ya bar min... Lokacin da ya mutu ina ƙarami sosai, amma duk da haka ba na mancewa abubuwan da suka shefi shi, a ko da yaushe yana yawan cewa babu wanda ya dace da zama sarkin Mamlakatul Afsah bayan Uwais!...”
Ya ɗan yi fasali yana murmushi me ciwo, ya shafa kansa sannan ya ci gaba da faɗin.
“Ashe hakan ba zai zama gaskiya ba, ashe wani bayan ni ne zai zama sarkin! Ashe ba ni da rabon gadar mahaifina...”
Lokacin da ya kai ƙarshe duk hankalin Adam da Ivana na kan Arman da jikinsa ya yi sanyi, ba komai yake tunowa ba face Abby. Ta wani ɓangaren zai iya cewa rayuwar Uwais na kamanceceniya da tasa rayuwar. Idan aka kwatanta Anser da Ammu Anwar, Safraz kuma da Faisal, Malik Dhaakir kuma da Abby, Uwais kuma a matsayin shi!... Ke nan son abin duniya zai iya sawa Ammu Anwar da Faisal su haɗa hannu wurin kashe Abby?...
“Arman!”
Kiran da Ivana ta masa ya katse masa tunani, sai ya kalleta, sannan ya gyara zaman glasses ɗinsa.
“Lafiya?”
Ta tambaya tana taɓa shi, ya girgiza mata kai, sannan ya miƙe ya nufi cikin daji, sai da ya yi nesa da su sosai, sannan ya jingina da jikin wata bishiya, kewar ahalinsa na mamaye masa ruhi. Wayarsa ya ɗauko, ya buɗe, sannan ya shiga gallery, ya dubo hoton da suka ɗauka shi da Immi ranar da zai gudu daga gida.
Ƙwalla ya ji na taruwa a idonsa, hakan yasa ya kai hannu ya cire glasses ɗinsa, sannan ya goge idonsa, ya mayar da glasses ɗin, kana ya dubo hotonsu shi da Abby, wani tsohon hoto da aka daɗe da ɗaukansa...
“In Allah ya sa ba ni da rabon dawowa gida ina fatan ka yafe min Abby, idan kuma har Allah ya nufi dawowata ina me baka tabbacin zan yi abin da kake so, zan karɓi shugabancin da ake fata da tuƙuburin na karɓa... Domin a yanzu na gane cewa kuskure ne bijire maka da na yi ta yi a baya, ka yafeni Abby!”
Ya furta wani hawayen na zubo masa. A dai-dai lokacin kuma ya ji ihun Ivana, hakan tasa ya buɗe idonsa da sauri, sannan ya juya yana kallon bayansa, domin ta nan ya jiyo ihun.
*
“Kamar akwai abin da yake damunsa!”
Cewar Uwais lokacin da Arman ya tashi daga wurin. Adam ya girgiza kansa.
“Ta wani ɓangaren rayuwarka da tasa tana kamanceceniya. A zamaninmu mahaifinsa babban ɗan kasuwa ne, sannan yana da manyan kanfanunuwa, kuma shi mahaifin nasa yana da ɗan uwa, wanda yake da ɗa namiji, shi ma ɗan nasa yana da burin zama shugaban kamfanin. Kasancewar shi Arman na da nakasar gani ya sa kawun nasa ya yi amfani da wannan damar wurin cusa masa ƙiyayyar shugabancin kamfanin. A halin yanzu kuma mahaifinsa ya fara gazawa, tsufa ya fara masa sallama, yana buƙatar Arman ya maye gurbinsa, amma sam Arman ya ƙi aminta da hakan... Hatta da wannan tafiyar da muka yi ta samo asali ne daga gujewa karɓar shugabancin kamfanin!”
“Abin tausayi!”
Cewar Uwais.
“Me ya sa yake saka wani abu a saman idonsa?”
Sana ta tambaya. Adam da Ivana suka yi dariya.
“Glasses ake kiransu, kuma su ne suke taimaka masa wurin gani, ba tare da su ba ba zai iya ganin ko da tafin hannunsa ba!”
“Na gane!”
Cewarta tana waigawa tare da kallon hanyar da ya bi.
“Adam taimaka min na miƙe!”
Cewar Ivana, Adam ya taimaka ya ɗagata.
“Ina za ki je?”
Ya tambaya ganin ta yi hanyar kogin dake gefe da su, Ivana na ɗingisa ƙafa tace.
“Zan wanke fuskata ne”
Da haka ta ƙarasa bakin kogin, ta tsugguna ta fara wanke fuskarta, sai da ta gama ta miƙe, tana shirin komawa inda su Uwais suke ta ga wani abu ya faɗo gabanta tim!. Razana ta yi ta ja baya tana ƙarewa budurwar da ta faɗo gabanta kallo. Kafin ta yi wani yunƙuri budurwar ta ruƙo wuyanta, sannan ta buɗe fuska-fukanta ta tashi sama da ita, hakan yasa ta ƙwala ihu domin naiman ɗaukin abokanta.
Lokacin da Su Adam suka iso bakin kogin har budurwar ta yi nisa da ita a sama.
“Ivana!”
Cewar Adam cikin matsanancin tashin hankali.
“Me ya samu Ivana?”
Cewar Adam da ya ƙaraso wurin da gudu, shi ma kuma sai a lokacin ya lura da Ivana dake sama.
“Wace ce waccan?”
Arman ɗin ya tambaya yana kallon budurwar dake tare da Ivana. Kafin wani ya amsa masa Uwais ya buɗe nasa fukafukan zai tashi sama, Arman ya dakatar da shi.
“Uwais! Zan tafi tare da kai!”
“Zo mu je!”
Kawai Uwais yace, sannan ya riƙe hannun Arman ɗaya, ya tashi sama da shi, suka bi bayan budurwar da ta ɗauke Ivana.
...End of book 1...
____________________
_Humm! Shin wacece wannan wadda ta sace Ivana?_
_Shin kuna ganin cewa Uwais da Arman za su iya cetonta?_
_Wata ƙiyayya ce tsakanin Eid da Malik Cangaz?_
_Wani abu ne ya samu matar Eid da ahalinsa da har ta kai ga yana son ɗaukar fansa!_
_Me Malik Safraz yake shiryawa?_
_Wani ƙudiri ne ya sa Sana matar Malik Wasimudeen shigowa cikin ADVENTURERS?_
_Shin kuna ganin dakarun Malik Cangaz za su iya riskar ADVENTURERS?_
_Mece ce makomar auren da Malik Cangaz yake shiryawa?_
_Yaushe ADVENTURERS ɗinmu za su riske ƙofar Malik Cangaz?. Shin za su iya samun nasarar buɗe ƙofar? Shin za su koma gida ko a'a?_
Domin ci gaba da karanta book 2 za ku biya ₦400 for regular group. ₦800 for VIP to.
5487270431
Salma Isah
Monie point
Shaidar biya kuma ta 08130172702.
Sannan za ku samu complete book one and 2 on Arewabooks, kada ku manta ku yi following ɗina domin samun notification da zarar na yi update.
Ina me tabbatar muku da book 2 is giving 🔥🔥🔥. A har kullum, godiya ta musamman zuwa ga masoyana a duk inda kuke. I ❤️ like WUJIGA-WUJIGA 💋. See you in book 2.
Best regards
Salma Ahmad Isah ✍️
A.k.a Candy🦋
A.k.a Bahaɗejia🐎
2024...
Ya ɗan yi fasali yana murmushi me ciwo, ya shafa kansa sannan ya ci gaba da faɗin.
“Ashe hakan ba zai zama gaskiya ba, ashe wani bayan ni ne zai zama sarkin! Ashe ba ni da rabon gadar mahaifina...”
Lokacin da ya kai ƙarshe duk hankalin Adam da Ivana na kan Arman da jikinsa ya yi sanyi, ba komai yake tunowa ba face Abby. Ta wani ɓangaren zai iya cewa rayuwar Uwais na kamanceceniya da tasa rayuwar. Idan aka kwatanta Anser da Ammu Anwar, Safraz kuma da Faisal, Malik Dhaakir kuma da Abby, Uwais kuma a matsayin shi!... Ke nan son abin duniya zai iya sawa Ammu Anwar da Faisal su haɗa hannu wurin kashe Abby?...
“Arman!”
Kiran da Ivana ta masa ya katse masa tunani, sai ya kalleta, sannan ya gyara zaman glasses ɗinsa.
“Lafiya?”
Ta tambaya tana taɓa shi, ya girgiza mata kai, sannan ya miƙe ya nufi cikin daji, sai da ya yi nesa da su sosai, sannan ya jingina da jikin wata bishiya, kewar ahalinsa na mamaye masa ruhi. Wayarsa ya ɗauko, ya buɗe, sannan ya shiga gallery, ya dubo hoton da suka ɗauka shi da Immi ranar da zai gudu daga gida.
Ƙwalla ya ji na taruwa a idonsa, hakan yasa ya kai hannu ya cire glasses ɗinsa, sannan ya goge idonsa, ya mayar da glasses ɗin, kana ya dubo hotonsu shi da Abby, wani tsohon hoto da aka daɗe da ɗaukansa...
“In Allah ya sa ba ni da rabon dawowa gida ina fatan ka yafe min Abby, idan kuma har Allah ya nufi dawowata ina me baka tabbacin zan yi abin da kake so, zan karɓi shugabancin da ake fata da tuƙuburin na karɓa... Domin a yanzu na gane cewa kuskure ne bijire maka da na yi ta yi a baya, ka yafeni Abby!”
Ya furta wani hawayen na zubo masa. A dai-dai lokacin kuma ya ji ihun Ivana, hakan tasa ya buɗe idonsa da sauri, sannan ya juya yana kallon bayansa, domin ta nan ya jiyo ihun.
*
“Kamar akwai abin da yake damunsa!”
Cewar Uwais lokacin da Arman ya tashi daga wurin. Adam ya girgiza kansa.
“Ta wani ɓangaren rayuwarka da tasa tana kamanceceniya. A zamaninmu mahaifinsa babban ɗan kasuwa ne, sannan yana da manyan kanfanunuwa, kuma shi mahaifin nasa yana da ɗan uwa, wanda yake da ɗa namiji, shi ma ɗan nasa yana da burin zama shugaban kamfanin. Kasancewar shi Arman na da nakasar gani ya sa kawun nasa ya yi amfani da wannan damar wurin cusa masa ƙiyayyar shugabancin kamfanin. A halin yanzu kuma mahaifinsa ya fara gazawa, tsufa ya fara masa sallama, yana buƙatar Arman ya maye gurbinsa, amma sam Arman ya ƙi aminta da hakan... Hatta da wannan tafiyar da muka yi ta samo asali ne daga gujewa karɓar shugabancin kamfanin!”
“Abin tausayi!”
Cewar Uwais.
“Me ya sa yake saka wani abu a saman idonsa?”
Sana ta tambaya. Adam da Ivana suka yi dariya.
“Glasses ake kiransu, kuma su ne suke taimaka masa wurin gani, ba tare da su ba ba zai iya ganin ko da tafin hannunsa ba!”
“Na gane!”
Cewarta tana waigawa tare da kallon hanyar da ya bi.
“Adam taimaka min na miƙe!”
Cewar Ivana, Adam ya taimaka ya ɗagata.
“Ina za ki je?”
Ya tambaya ganin ta yi hanyar kogin dake gefe da su, Ivana na ɗingisa ƙafa tace.
“Zan wanke fuskata ne”
Da haka ta ƙarasa bakin kogin, ta tsugguna ta fara wanke fuskarta, sai da ta gama ta miƙe, tana shirin komawa inda su Uwais suke ta ga wani abu ya faɗo gabanta tim!. Razana ta yi ta ja baya tana ƙarewa budurwar da ta faɗo gabanta kallo. Kafin ta yi wani yunƙuri budurwar ta ruƙo wuyanta, sannan ta buɗe fuska-fukanta ta tashi sama da ita, hakan yasa ta ƙwala ihu domin naiman ɗaukin abokanta.
Lokacin da Su Adam suka iso bakin kogin har budurwar ta yi nisa da ita a sama.
“Ivana!”
Cewar Adam cikin matsanancin tashin hankali.
“Me ya samu Ivana?”
Cewar Adam da ya ƙaraso wurin da gudu, shi ma kuma sai a lokacin ya lura da Ivana dake sama.
“Wace ce waccan?”
Arman ɗin ya tambaya yana kallon budurwar dake tare da Ivana. Kafin wani ya amsa masa Uwais ya buɗe nasa fukafukan zai tashi sama, Arman ya dakatar da shi.
“Uwais! Zan tafi tare da kai!”
“Zo mu je!”
Kawai Uwais yace, sannan ya riƙe hannun Arman ɗaya, ya tashi sama da shi, suka bi bayan budurwar da ta ɗauke Ivana.
...End of book 1...
____________________
_Humm! Shin wacece wannan wadda ta sace Ivana?_
_Shin kuna ganin cewa Uwais da Arman za su iya cetonta?_
_Wata ƙiyayya ce tsakanin Eid da Malik Cangaz?_
_Wani abu ne ya samu matar Eid da ahalinsa da har ta kai ga yana son ɗaukar fansa!_
_Me Malik Safraz yake shiryawa?_
_Wani ƙudiri ne ya sa Sana matar Malik Wasimudeen shigowa cikin ADVENTURERS?_
_Shin kuna ganin dakarun Malik Cangaz za su iya riskar ADVENTURERS?_
_Mece ce makomar auren da Malik Cangaz yake shiryawa?_
_Yaushe ADVENTURERS ɗinmu za su riske ƙofar Malik Cangaz?. Shin za su iya samun nasarar buɗe ƙofar? Shin za su koma gida ko a'a?_
Domin ci gaba da karanta book 2 za ku biya ₦400 for regular group. ₦800 for VIP to.
5487270431
Salma Isah
Monie point
Shaidar biya kuma ta 08130172702.
Sannan za ku samu complete book one and 2 on Arewabooks, kada ku manta ku yi following ɗina domin samun notification da zarar na yi update.
Ina me tabbatar muku da book 2 is giving 🔥🔥🔥. A har kullum, godiya ta musamman zuwa ga masoyana a duk inda kuke. I ❤️ like WUJIGA-WUJIGA 💋. See you in book 2.
Best regards
Salma Ahmad Isah ✍️
A.k.a Candy🦋
A.k.a Bahaɗejia🐎
2024...