Sashe 14
Juyin KwaÉ—o Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Faɗin Arman yana gyara glasses ɗinsa, Adam ya soma ja da baya, sannan cikin karkarwar hannu ya ɗaga ɗan yatsansa, ya yi nuni da bayansu, hakan ya sa cike da mamaki Ivana da Arman suka dubi juna, kafin Ivana ta juya tana faɗin.
“Wai me ka gani da ka...”
Haɗiyewa sauran kalaman ta yi, tare da binsu da yawun bakinta tana zaro ido, kamar yanda ta yi kyakkyawan gani haka shi ma Arman ya yi, dan yana juyawa suka yi ido huɗu da Cheetah ɗin dake saman dutsen da yake zubar da ruwa.
Ba su tsaya ɓata lokaci ba suka ce ƙafa me na ci ban baki ba? Kowa a cikinsu ya ranta a na kare, gudu suke Cheetah ɗin na binsu, Adam ya fi koea ruɗewa, dan a gudun ma shi ne a kan gaba, dan tun da ya zo duniya bai san wani abu da ya firgita shi sama da wannan ba, sanin cewa Ivana me rauni ce ya sa Arman ya ruƙo hannunta yake janta suna gudu tun ƙarfinsu.
A yunƙurin ceton rayukansu suka faɗa cikin wani kogo dake bayan dutsen da Cheetah ɗin take, kuma suna shiga cikin kogon ba su tsaya wata-wata ba wurin naiman maɓoya, Arman ne ya fara ganin wata tsohuwar ƙofar katako dake cikin kogon, dan haka ya yi azamar saka duka hannayensa biyu, tare da ƙarfin da Allah ya wadata shi da shi ya buɗe ƙofar.
“Ku zo ku shiga”
Ya faɗa ba tare da ya tsaya duba abin da yake a bayan ƙofar ba, ya janyo hannun Ivana ya turata, an ce idan ka ga mutuwa idonka rufewa yake, tabbas idanuwansu sun rufe, domin har suka gama shigewa ƙofar sam ba su lura da ina suke shiga ba.
Abin da zai biyo bayan shigarsu wannan ƙofar sai ya fiye musu su tsaya wannan Cheetah ɗin da ta biyosu ta cinye naman jikkunansu ɗanye. Domin masifa da bala'in da zai biyo baya babu hankali ko tunanin da zai iya hasaso shi...
Yanzu ne labarin zai soma, sai a yanzu ne za mu kama ainahin hanyar da labarin yabi, yanzu ne muka saƙo zaren labarin, domin gane warwararsa, sai kun ji abin da ya biyo bayan shigewarsu cikin wannan ƙofa...
*Wani Zamani...*
Wani zamani na nufin zamanin da ya shuɗe kafin samuwarmu, ko kuma wanda zai zo bayan wanzuwarmu, zamani na zuwa ya wuce kamar wucewar damina da rani... Sannan zamani ya kan shuɗe, har a manta shi a duniya, matsawar babu masu bada labarin wannan zamanin... Sunan zamani na wakiltar shekaru 100 da suka suɗe a baya, ko waɗan da za su zo a gaba... A kan iya gane bambancin zamani ta hanyar tufafinsu, abincisu, gine-ginensu da kuma kalar yarensu...
*
Wani kyakkyawan daji ne, ko ina ka kalla koren ganye ne ke kaɗawa a cikin iskar Allah, dogayen bishiyu da ciyayin da suka ƙawata ƙasa su ne a ko ina. Kuma duk girman dajin babu komai cikinsa sai ginin wata bukka ƙwara ɗaya tal, wadda aka yi ta da busasshiyar ciyawa. (Budu)
Daga bayan bukkar, wani farin dattijo ne durƙushe, yana tsinkar 'ya'yan itaciyar da suka nuna har suna faɗowa daga jikin bishiryarsu. Wasu kayan saƙi ne sanye a jikinsa, wanda za su shaida maka daga zamanin da yake, gashin kansa dogo ne, domin har ya sauƙa gadon bayansa, duk da rawanin da ya yi a kansa.
Wata iska me matuƙar ƙarfi ce ta fara kaɗawa a dajin, hakan ya sa dattijon ya miƙe tsaye yana kallon dogayen bishiyun dake wurin, waɗan da ke kaɗawa da ƙarfi, sakamakon ƙarfin iskar da ake. Kansa ya juya ta ɓarin damansa kaɗan, nan ya ga wani jan kyalle dake ɗaure a saman bukkarsa na shirin sulmiyewa ya faɗo.
Hakan ya sa ya firfito da idonsa cike da abin da ya zarce a kira shi da mamaki. Bakinsa na rawa ya juya ya shiga bin dajin da kallo, amma bayan iskar dake ƙara ƙarfi babu kowa babu komai. Mamaki bai ƙara kama shi ba sai da ya ga jan ƙyallen ya kunce ya faɗi ƙasa...
A nan ne ya tabbatar da wani abu guda, lalle ranar da ya daɗe yana jiran isowarta ta zo, ranar da ya shafe sama da shekaru ashirin na rayuwarsa yana rayuwa a wannan dajin domin ta zo, ranar da za a yi wasu baƙin matasa uku, daga wani zamanin zuwa nasu...
“Tabbas! Baƙin matasa uku sun samu shigowa duniyarmu. Domin zama silar kawo ƙarshen mulkin zalunci. Sun zo domin tada gagarumin yaƙi da yake dai-dai da yaƙin duniya... Ƙaddara ba ta da siffa, ta kan juya rayuwar ɗan adam ta ko wace siga, sannan ta kan iya maida sama ta dawo ƙasa cikin abin da bai fi ƙiftawar ido ba. Lalle ƙaddara ita ce ta zamto silar wanzuwar waɗannan matasa a wannan duniya tamu... Wannan ƙaddara ita ce ta yi JUYIN KWAƊO da rayuwar waɗannan matasa, daga zamaninsu zuwa namu...”
Kwandon kayan marmarin dake hannunsa ne ya suɓuce ya faɗi, yayin da ya ga haske ya fara mamaye dajin, saurin durƙushewa ya yi a ƙasa yana me godiya da mai duka...
*
Yashe suke a kan ciyayin dake kusa da wata ƙatuwar bishiya, idan ka musu kallo ɗaya sai ka ce a mace suke, amma kuma ba a macen suke ba, wani dogon bacci suke me kama da suma. Arman ne ya fara motsawa, kafin ya buɗe idonsa yana dafe kansa da ya sara lokaci guda.
Idonsa ya rufe ya sake buɗewa, amma saboda glasses ɗinsa a fashe suke ya sa ba ya gani da kyau, a daddafe ya miƙe zaune yana yarfe hannu, saboda Adam da ya danne masa hannun nasa, glasses ɗin ya cire, ya kamo ƙasan rigarsa ya goge shi, sannan ya mayar idonsa, a nan ne ya gane cewa glasses ɗin ne ya fashe. Tsaki ya ja, dubansa na kaiwa kan Adam dake kwance, ya sake jan wani tsakin tare da saka hannunsa ya ɗaka masa duka.
“Mun mutu... Damisa ta cinyemu!”
Ya farka da wannan batu a tsorace, amma ganin Damisar ba ta cinyesu ba ya sa ya fara son kwantar da hankalinsa, kusan a tare suka dubi Ivana dake can nesa da su, hakan ya sa Arman ya miƙe ya nufi inda take, ita ma ya tasheta.
“Wai a ina muke ne?”
Adam ya tambaya yana miƙewa tsaye, yayin da Arman ya cillar da tsohon glasses ɗinsa da ya fashe, Ivana kuma ta ba shi wani domin ya saka, sai da ya saka glasses ɗin sannan shi ma ya tsaya ƙarewa wurin kallo, daji ne fetal, ba gida gaba ba gida baya.
“Kai! Ina ƙofar da muka shigo?”
Cewar Ivana tana waige-waige, amma sam babu alamar ta a wurin, shi ko Arman shiru ya yi yana wani lissafi a cikin kansa, idan zai iya tunawa bayan wannan Cheetah ɗin ta biyosu sun buɗe wata ƙofa sun shiga, bayan da suka shiga ƙofar kuma ba su iya ganin komai ciki sai haske, sai wani abu me kama da iska da suka ji ya kwashesu, to daga nan ne ba su sake sanin me ke wakana a duniya ba sai yanzu...
“Arman a ina muke ne?”
Adam ya tambaya yana riƙo Arman, shi kansa Arman ba shi da wannan amsar, domin bai san a ina suke ba, bai san ya aka yi suka zo nan ba. A hankali ya ɗan matsa bayan bishiryar da suke kusa da ita, nan ya hangi wata bukka guda ɗaya tal.
“Ga wani ɗaki can, mu je mu duba”
Ya faɗa yana ɗaukan jakarsa, tare da goyata a bayansa. Suma nasu kayan suka ɗauka, sannan suka bi shi, shi dai Adam ya san cewa ɗakin bukka ce, su kuma sauran ba su san wani abu me kama da hakan ba. Shi ya sa tun kafin su ƙarasa kusa da bukkar suka fara taradaddin a duniyar da suke.
Ko da suka iske bukkar sai aka tsaya kallon-kallo, dan ba su san me za su iske a ciki ba. Arman ne ya fara ƙundun balar nufar ƙofar, yana taku a hankali, hannunsa ya sa ya ɗaga wani abu me kama da labule da ya saya ƙofar, hakan ya ba shi damar ganin cikin ɗakin.
Babu komai a ciki face tarin littattafai irin na da, da kuma wasu takardu da aka yi su da fatar dabbobi, sai wani gadon ciyawa dake a gefe, sannan wani gajeren teburi, wanda a kusa da shi wani farin dattijo ne zaune.
“Barka da zuwa JAGORA”
Su ne kawai kalaman da dattijon ya furta yana ɗora ido a kan Arman. Shi kuma Arman tsaye ya yi yana kallon tufafi da kayan ɗakin mutumin, ko kusa ko alama bai yi kama da wanda yake rayuwa a zamaninsu ba, mutumin ya fi kama da irin mutanen da suka rayu a baya.
Shiru suka yi su ukun, yayin da suke zaune gaban dattijo, banda kallonsa ba abin da suke, suna jiran ya amsa musu tambayoyin da suka soma masa, shi kuma sai murmushi yake musu, kamar wanda ya san da zuwansu.
“Ina ne nan?”
Arman ya sake nanatawa datijjon tambayar da Ivana ta fara masa tun ɗazu. Kuma sai yanzu ya samu damar ba shi amsa.
“Hayy al- Umda!”
Arman Ivana da Adam suka dubi juna cike da kokwanton da ya zarce na da, su har yanzu sun kasa gane abin da yake faruwa, amma Arman ya fara fuskantar wani abu guda...
“Ban taɓa jin sunan dajin nan ba, kuma mu a Bavarian forest muke ba Hayy al- Umda ba”
Cewar Ivana. Dattijo ya yi murmushi, sannan cikin larabcinsa me matuƙar daɗi da bawa ko wani harafi hakkinsa yace.
“A halin yanzu kun bar zamaninku matasa, a yanzu kuna zamaninmu ne, a ƙalla shekaru 1000 baya!”
“Wai me ka gani da ka...”
Haɗiyewa sauran kalaman ta yi, tare da binsu da yawun bakinta tana zaro ido, kamar yanda ta yi kyakkyawan gani haka shi ma Arman ya yi, dan yana juyawa suka yi ido huɗu da Cheetah ɗin dake saman dutsen da yake zubar da ruwa.
Ba su tsaya ɓata lokaci ba suka ce ƙafa me na ci ban baki ba? Kowa a cikinsu ya ranta a na kare, gudu suke Cheetah ɗin na binsu, Adam ya fi koea ruɗewa, dan a gudun ma shi ne a kan gaba, dan tun da ya zo duniya bai san wani abu da ya firgita shi sama da wannan ba, sanin cewa Ivana me rauni ce ya sa Arman ya ruƙo hannunta yake janta suna gudu tun ƙarfinsu.
A yunƙurin ceton rayukansu suka faɗa cikin wani kogo dake bayan dutsen da Cheetah ɗin take, kuma suna shiga cikin kogon ba su tsaya wata-wata ba wurin naiman maɓoya, Arman ne ya fara ganin wata tsohuwar ƙofar katako dake cikin kogon, dan haka ya yi azamar saka duka hannayensa biyu, tare da ƙarfin da Allah ya wadata shi da shi ya buɗe ƙofar.
“Ku zo ku shiga”
Ya faɗa ba tare da ya tsaya duba abin da yake a bayan ƙofar ba, ya janyo hannun Ivana ya turata, an ce idan ka ga mutuwa idonka rufewa yake, tabbas idanuwansu sun rufe, domin har suka gama shigewa ƙofar sam ba su lura da ina suke shiga ba.
Abin da zai biyo bayan shigarsu wannan ƙofar sai ya fiye musu su tsaya wannan Cheetah ɗin da ta biyosu ta cinye naman jikkunansu ɗanye. Domin masifa da bala'in da zai biyo baya babu hankali ko tunanin da zai iya hasaso shi...
Yanzu ne labarin zai soma, sai a yanzu ne za mu kama ainahin hanyar da labarin yabi, yanzu ne muka saƙo zaren labarin, domin gane warwararsa, sai kun ji abin da ya biyo bayan shigewarsu cikin wannan ƙofa...
*Wani Zamani...*
Wani zamani na nufin zamanin da ya shuɗe kafin samuwarmu, ko kuma wanda zai zo bayan wanzuwarmu, zamani na zuwa ya wuce kamar wucewar damina da rani... Sannan zamani ya kan shuɗe, har a manta shi a duniya, matsawar babu masu bada labarin wannan zamanin... Sunan zamani na wakiltar shekaru 100 da suka suɗe a baya, ko waɗan da za su zo a gaba... A kan iya gane bambancin zamani ta hanyar tufafinsu, abincisu, gine-ginensu da kuma kalar yarensu...
*
Wani kyakkyawan daji ne, ko ina ka kalla koren ganye ne ke kaɗawa a cikin iskar Allah, dogayen bishiyu da ciyayin da suka ƙawata ƙasa su ne a ko ina. Kuma duk girman dajin babu komai cikinsa sai ginin wata bukka ƙwara ɗaya tal, wadda aka yi ta da busasshiyar ciyawa. (Budu)
Daga bayan bukkar, wani farin dattijo ne durƙushe, yana tsinkar 'ya'yan itaciyar da suka nuna har suna faɗowa daga jikin bishiryarsu. Wasu kayan saƙi ne sanye a jikinsa, wanda za su shaida maka daga zamanin da yake, gashin kansa dogo ne, domin har ya sauƙa gadon bayansa, duk da rawanin da ya yi a kansa.
Wata iska me matuƙar ƙarfi ce ta fara kaɗawa a dajin, hakan ya sa dattijon ya miƙe tsaye yana kallon dogayen bishiyun dake wurin, waɗan da ke kaɗawa da ƙarfi, sakamakon ƙarfin iskar da ake. Kansa ya juya ta ɓarin damansa kaɗan, nan ya ga wani jan kyalle dake ɗaure a saman bukkarsa na shirin sulmiyewa ya faɗo.
Hakan ya sa ya firfito da idonsa cike da abin da ya zarce a kira shi da mamaki. Bakinsa na rawa ya juya ya shiga bin dajin da kallo, amma bayan iskar dake ƙara ƙarfi babu kowa babu komai. Mamaki bai ƙara kama shi ba sai da ya ga jan ƙyallen ya kunce ya faɗi ƙasa...
A nan ne ya tabbatar da wani abu guda, lalle ranar da ya daɗe yana jiran isowarta ta zo, ranar da ya shafe sama da shekaru ashirin na rayuwarsa yana rayuwa a wannan dajin domin ta zo, ranar da za a yi wasu baƙin matasa uku, daga wani zamanin zuwa nasu...
“Tabbas! Baƙin matasa uku sun samu shigowa duniyarmu. Domin zama silar kawo ƙarshen mulkin zalunci. Sun zo domin tada gagarumin yaƙi da yake dai-dai da yaƙin duniya... Ƙaddara ba ta da siffa, ta kan juya rayuwar ɗan adam ta ko wace siga, sannan ta kan iya maida sama ta dawo ƙasa cikin abin da bai fi ƙiftawar ido ba. Lalle ƙaddara ita ce ta zamto silar wanzuwar waɗannan matasa a wannan duniya tamu... Wannan ƙaddara ita ce ta yi JUYIN KWAƊO da rayuwar waɗannan matasa, daga zamaninsu zuwa namu...”
Kwandon kayan marmarin dake hannunsa ne ya suɓuce ya faɗi, yayin da ya ga haske ya fara mamaye dajin, saurin durƙushewa ya yi a ƙasa yana me godiya da mai duka...
*
Yashe suke a kan ciyayin dake kusa da wata ƙatuwar bishiya, idan ka musu kallo ɗaya sai ka ce a mace suke, amma kuma ba a macen suke ba, wani dogon bacci suke me kama da suma. Arman ne ya fara motsawa, kafin ya buɗe idonsa yana dafe kansa da ya sara lokaci guda.
Idonsa ya rufe ya sake buɗewa, amma saboda glasses ɗinsa a fashe suke ya sa ba ya gani da kyau, a daddafe ya miƙe zaune yana yarfe hannu, saboda Adam da ya danne masa hannun nasa, glasses ɗin ya cire, ya kamo ƙasan rigarsa ya goge shi, sannan ya mayar idonsa, a nan ne ya gane cewa glasses ɗin ne ya fashe. Tsaki ya ja, dubansa na kaiwa kan Adam dake kwance, ya sake jan wani tsakin tare da saka hannunsa ya ɗaka masa duka.
“Mun mutu... Damisa ta cinyemu!”
Ya farka da wannan batu a tsorace, amma ganin Damisar ba ta cinyesu ba ya sa ya fara son kwantar da hankalinsa, kusan a tare suka dubi Ivana dake can nesa da su, hakan ya sa Arman ya miƙe ya nufi inda take, ita ma ya tasheta.
“Wai a ina muke ne?”
Adam ya tambaya yana miƙewa tsaye, yayin da Arman ya cillar da tsohon glasses ɗinsa da ya fashe, Ivana kuma ta ba shi wani domin ya saka, sai da ya saka glasses ɗin sannan shi ma ya tsaya ƙarewa wurin kallo, daji ne fetal, ba gida gaba ba gida baya.
“Kai! Ina ƙofar da muka shigo?”
Cewar Ivana tana waige-waige, amma sam babu alamar ta a wurin, shi ko Arman shiru ya yi yana wani lissafi a cikin kansa, idan zai iya tunawa bayan wannan Cheetah ɗin ta biyosu sun buɗe wata ƙofa sun shiga, bayan da suka shiga ƙofar kuma ba su iya ganin komai ciki sai haske, sai wani abu me kama da iska da suka ji ya kwashesu, to daga nan ne ba su sake sanin me ke wakana a duniya ba sai yanzu...
“Arman a ina muke ne?”
Adam ya tambaya yana riƙo Arman, shi kansa Arman ba shi da wannan amsar, domin bai san a ina suke ba, bai san ya aka yi suka zo nan ba. A hankali ya ɗan matsa bayan bishiryar da suke kusa da ita, nan ya hangi wata bukka guda ɗaya tal.
“Ga wani ɗaki can, mu je mu duba”
Ya faɗa yana ɗaukan jakarsa, tare da goyata a bayansa. Suma nasu kayan suka ɗauka, sannan suka bi shi, shi dai Adam ya san cewa ɗakin bukka ce, su kuma sauran ba su san wani abu me kama da hakan ba. Shi ya sa tun kafin su ƙarasa kusa da bukkar suka fara taradaddin a duniyar da suke.
Ko da suka iske bukkar sai aka tsaya kallon-kallo, dan ba su san me za su iske a ciki ba. Arman ne ya fara ƙundun balar nufar ƙofar, yana taku a hankali, hannunsa ya sa ya ɗaga wani abu me kama da labule da ya saya ƙofar, hakan ya ba shi damar ganin cikin ɗakin.
Babu komai a ciki face tarin littattafai irin na da, da kuma wasu takardu da aka yi su da fatar dabbobi, sai wani gadon ciyawa dake a gefe, sannan wani gajeren teburi, wanda a kusa da shi wani farin dattijo ne zaune.
“Barka da zuwa JAGORA”
Su ne kawai kalaman da dattijon ya furta yana ɗora ido a kan Arman. Shi kuma Arman tsaye ya yi yana kallon tufafi da kayan ɗakin mutumin, ko kusa ko alama bai yi kama da wanda yake rayuwa a zamaninsu ba, mutumin ya fi kama da irin mutanen da suka rayu a baya.
Shiru suka yi su ukun, yayin da suke zaune gaban dattijo, banda kallonsa ba abin da suke, suna jiran ya amsa musu tambayoyin da suka soma masa, shi kuma sai murmushi yake musu, kamar wanda ya san da zuwansu.
“Ina ne nan?”
Arman ya sake nanatawa datijjon tambayar da Ivana ta fara masa tun ɗazu. Kuma sai yanzu ya samu damar ba shi amsa.
“Hayy al- Umda!”
Arman Ivana da Adam suka dubi juna cike da kokwanton da ya zarce na da, su har yanzu sun kasa gane abin da yake faruwa, amma Arman ya fara fuskantar wani abu guda...
“Ban taɓa jin sunan dajin nan ba, kuma mu a Bavarian forest muke ba Hayy al- Umda ba”
Cewar Ivana. Dattijo ya yi murmushi, sannan cikin larabcinsa me matuƙar daɗi da bawa ko wani harafi hakkinsa yace.
“A halin yanzu kun bar zamaninku matasa, a yanzu kuna zamaninmu ne, a ƙalla shekaru 1000 baya!”