Sashe 22
Juyin KwaÉ—o Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai da sarki ya amshi gaisuwar tasu, sannan kowa ya miƙe kan ƙafafunsa, hakan ya bawa Asra damar matsawa kusa da Malik, domin jin abin da ke tafe da shi. Yau ma kammaninsa sak na matasa, ba za ka ce shi ne mahaifin gimbiyoyin uku ba, kai kace wani yayansu ne.
“Horarwa na tafiya yanda ake so Asra!”
Cewar Malik cike da izza, Asra ta yi murmushi tana duban mahaifinta, sannan ta jinjina kanta a ladabce.
“Sosai ma kuwa Darvesh (Holy man)”
“Ko za mu iya ganawa na wasu daƙiƙu?”
Faɗin Malik Cangaz, Asra ta gyaɗa kai, a tare suka taka zuwa wata kusurwa dake cikin filin, wadda ta fitar da su (balcony) dake can saman fadar, daga wurin ma za ka iya hango gine-ginen gidaje masallatai da kuma kasuwar masarautar kaf.
“Zuwa yanzu kwanaki uku kacal suka rage a ɗaura auren Iqrah da yariman Azad... Duk wasu shirye-shirye mun kammalasu, ɓangaren tsaro ne ba mu yi komai ba, dan haka ina so a tabbatar da tsaro a masarautar nan, domin akwai tarin baƙin da za su zo daga baƙin masarautun da suke maƙotantaka da mu... Ba na son a samu wani kuskure!”
Asra ta jinjina kai tana saƙala gashin kanta a bayan kunnenta.
“Zan tabbatar da hakan Darvesh...”
“Zuwa gobe zan je kaiwa abokina sarkin Mamlakatul Dahi goron gayyata, domin ba na so na aika Manzo! Na fi so na je da kaina domin isar da saƙon... Dan haka ki shirya, ina so ki min rakiya!”
Asra ta risina cikin girmamawa.
“An gama Darvesh...”
“Na sallameki”
Da haka ta juya ta barshi tsaye a wurin yana kallon girman masarautarsa. Kafin kuma amintaccen hadiminsa ya shigo wurin a hanzarce.
“An kamo matasan da ake zargi da cin amanar ƙasarmu ta hanyar fitar da bayanan kasuwancinmu na sirri ya shugabana!”
Cewar hadimin, bayan ya kwashi gaisuwa. Malik ya dube shi cike da isa, sannan ya furta.
“A kai min su kurkukun cikin ƙasa, a gana musu azaba ta mako guda, kafin na kai ga zartar da hukuncin da ya dace a kansu, kafin su mutu ina so su ɗanɗana azabar da za ta bawa duk wani me sha'awar aikata laifi irin nasu tsoro!”
Hadimin ya risina cikin alamar dake nuna ya karɓi saƙon shugaban nasa.
“An gama ya kai wannan adalin sarki!”
Daga haka shi ma ya fita daga wurin ya barshi, tsaye cikin sallalamin jiran ranar da boka Jalis zai sake naimansa. Domin tun bayan ranar da suka haɗu a kan maganar gano matasan nan uku bai sake naimansa ba, kuma hakan na nuna cewa har yanzu boka bai gano inda suke ba. A tsarinsa shi kuma ba ya zuwa wurin bokan ba tare da bokan ya naime shi ba... Amma a wannan karon dole ya karya ƙa'idar, dole ya je ya ji yanda aka yi aka haihu a ragaya.
MAMLAKATUL AFSAH.
Cike da zaƙuwa Malik Safraz ya ɗaga kai ga tawagar ɓoyen da yakan aika domin bincike, ya ƙagu su sanar da shi inda takobin mulkinsa yake.
“Ya shuganmu, haƙiƙa takobinka ya bayyana a ban ƙasa, sai dai samunsa shi ne abu mai matuƙar wuya a gareka!”
Muryar ɗaya daga cikinsu ta furta, ba tare da ya bayyana ba, domin ko shi kansa ba ya iya ganinsu sai idan sun so hakan. Ya ɗaga kansa ya kalli saitin inda maganar ke tashi, sannan ya furta.
“Shin har akwai wani abu da zai gagareni samu a faɗin wannan duniyar?”
“Ƙwarai kuwa ya shugabanmu, kuma wannan takobi na ɗaya daga ciki!”
“Me nene dalilinku na faɗin hakan?”
“Wanda yake tare da takobin shi ne abin ji, domin ko da yankar naman jikinsa za'ayi a kan takobin nan sai dai a yi, amma ba zai taɓa bari a raba shi da wannan takobi ba...”
“Waye shi?”
Malik Safraz ya tambaya ransa na ɓaci.
“UWAIS!”
Muryoyi uku suka ba shi amsa take, a nan ne fa hantar cikinsa ta fara motsi, domin in har Uwais ko Feroza na raye a ban ƙasa mulkinsa na cikin haɗari!... Ke nan me ya kamata ya yi a wannan gaɓar!?... Tambayar ta tuno masa da wata hatsabibiya ɗaya da zai iya sawa wannan aikin hankali kwance. Lokaci guda ya yi murmushi, sai kuma ya haɗa da dariya yana jinjina kai, sannan laɓɓansa suka furta sunanta.
“NATILA!”
GARIN QUDWA, YANKIN GABASHIN SAHARAR SUBAH.
Hayaniyar jama'ar dake kaikawo a cikin 'yar ƙaramar kasuwar garin ce ta cika ko ina. Komai na kayan siye da siyarwa daga ƙasashen duniya akan kawosu kasuwar wannan gari na Qudwa. Domin garin ya kasance cibiyar kasuwanci, duk da garin bai cika girma ba.
Ko wani mutum dake cikin kasuwar za ka same shi sanye da shiga irin ta garinsu ko yankinsu, ko kuma masarautarsu. Yayin da ake hada-hadar cinnikayya a cikin kasuwar. Wata iska me ƙarfi ta taso daga cikin sahararar dake gabas da kasuwar, hakan yasa ƙura ta shiga bule mutanen cikin kasuwar. Kafin wata guguwa ta shigo cikin kasuwar, sannan ba ta sauƙa a ko ina ba sai kan rufin wani shago.
Kaɗan-kaɗan iskar ta fara raguwa, har ta ɗauke gaba ɗaya. Yayin da wannan guguwar ta rikiɗa zuwa wata doguwar budurwa. Sanye cikin baƙaƙen kaya, ta yi kitso guda biyu a kanta, tsayin jelar kitson har cinyoyinta. Fuskanta kuma a rufe yake, a hankali ta yi tsugunnon mage a kan rufin shagon, sannan ta shiga baza idonta a kan mutanen dake kai kawo...
Dan iskar da ta taso ba ta sa kasuwancin da ake gudanarwa ya dakata ba, sautin murmushin da ta yi ya fito tare da motswar ƙyallen da ta rufe fuskarta da shi, domin ta hango abin harinta, ci gaba ta yi da bin sawunsa, har ta ga sanda ya shiga wani loko da take da tabbacin babu kowa ciki.
Take ta ɓace daga saman shagon, kuma ba ta bayyana a ko ina ba sai a cikin lokon, sannan a gaban mutumin da take bibiya. Shi kansa mutumin da ya ganta sai da ya razana, hakan ya sa kayan dake hannunsa suka zube a ƙasa, ya ɗaga hannayensa sama kamar me laifi.
A wannan karon budurwar dariya ta yi, sannan ta buɗe fuskarta, kyakkyawar fuskarta ta bayyana gare shi, haƙika tana da kyau, amma kyawun ɗan maciji. Lokacin da ya ganeta bai san sanda ya saki fitsari a wando ba, jikinsa ya soma kyarma, domin ganin NATILA na dai-dai da ganin mutuwar mutum.
“Sannunmu da sake haɗuwa, Malam Ayyaz!”
Jikin Ayyaz na rawa ya shiga ja da baya yana son bata haƙuri, cikin wani irin sauri da ya ɗararma hankali ta isa gabansa, sannan ta saka hannayenta ta riƙe wuyansa.
“Dole na kasheka, sannan na ciro zuciyarka na kaiwa shugabana, na masa alƙawarin sadaukar masa da zuciyarka a daren yau!...”
Ta ƙarashe maganar wasu zaƙa-zaƙan fiƙoƙi na fitowa daga haƙwaranta na sama. Sannan ta kafasu a wuyansa, nan take Ayyaz ya fara shure-shure, amma Natila ba ta saki wuyansa ba sai da ta zuƙe fiye da rabin jinin jikinsa. Duk da haka ba ta ƙyale shi ba, da ta saki wuyan nasa ta ɗaga hannunta me yalwar dogayen farata, ta caka a ƙirjinsa, sannan ta ciro zuciyarsa, kana ta saki gangar jikinsa ta faɗi ƙasa.
Zuciyar dake riƙe a hannunta ta kalla, bakinta duk ya ɓaci da jinin jikinsa, ta sa bayan hannunta goge bakin nata, sannan ta sake rufe fuskarta, ta tsallake gawarsa ta ɓace a iska.
Salma Ahmad Isah ✍️
___________
_😳 Akwai matsala!_
_Ko su waye suka kama ADVENTURERS ɗinmu?. Shin ya za a yi su kuɓuta?_
_Batun wannan Natilar! Ya kuke ganin haɗuwarta da ADVENTURERS ɗinmu za ta kasance?._
_Book 1 ya kusa ƙarewa, dan haka ya kamata a fara biyan kuɗin book 2 tun yanzu._
5487270431
Salma Isah
Monie point
Shaidar biya kuma ta 08130172704.
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
🪄 ...JUYIN KWAƊO...🪄
©️Salma Ahmad Isah
SalmaAhmadIsah @ArewaBooks
SalmaAhmadIsah @Wattpad
Page-13
ADVENTURERS.
Kukan Adam shi ne ya cika ɗan ƙaramin akurkin da aka cusasu ciki, dan duka su huɗun tare da wata mata da ba su santa ba na cikin wani abu me kamar keji, yayin da mutanen da suka kamosu ke zaune kusa da kejin, sun yi ayari suna gabatar da bautarsu zuwa ga wutar da suka hura, domin sun lura cewa mutanen wuta sukw bautawa.
Kuma bayan hasken wutar babu komai a wurin sai na farin wata da ya samu zarafin ratsowa ta jikin ganyen bishiyoyin da suke a ko ina na dajin, sai kuma na fitilun wayoyinsu da suka kunna. Tun bayan da mutanen suka kama su ba su musu komai ba, kuma ba su ce da su komai ba, sai kallonsu da suke ta yi tun ɗazu, kamar za su cinyesu.
“Mi shan Allah Adam skut! (Dan Allah Adam ka yi shiru!)”
Cewar Ivana cikin rarrashi, Adam ya goge hawayen da yake, yana duban Arman dake wurga masa harara, shi kuma Uwais kallonsu kawai yake yana murmushi, dan kukan da Adam ɗin ke yi dariya yake son ba shi.
“Ki bar ni na yi kuka, wata ƙila wannan shi ne kukana na ƙarshe, daga shi kuma ba zan sake ba!... Saboda waɗannan abubuwan yanka mu za su yi, ko su cinye, ko su bawa dabbobinsu!...”
Ya ƙarashe yana jingina kansa da jikin itatuwan da suka kafa kejin.
“Idan ba ka mana shiru ba sai na maka duka!”
Cewar Arman a ƙufule. Sannan ya ƙara da.
“Kalli Ivana, ko ita ba ta yi kuka ba sai kai, ƙaton banza kawai!”
Adam ya kame jikinsa yana ƙifƙita ido. A karo na barkatai, Arman ya sake haske matar da suka tarar a cikin kejin da fitilar wayarsa, amma har yanzu tana a yanda suka shigo kejin suka sameta. Dunƙule take a wuri guda, ta haɗa kai da gwiwa, kuma duka jikinta a rufe yake.
“Uwais ka tambaya mana wannan matar ko ta san abin da mutane nan suke so!...”
Cewar Arman yana gyara zaman glasses ɗinsa.
“Da ace za ta faɗa da ta faɗa tuntuni, tun yaushe nake mata magana? Amma ko tari ka ji ta yi?...”
“Horarwa na tafiya yanda ake so Asra!”
Cewar Malik cike da izza, Asra ta yi murmushi tana duban mahaifinta, sannan ta jinjina kanta a ladabce.
“Sosai ma kuwa Darvesh (Holy man)”
“Ko za mu iya ganawa na wasu daƙiƙu?”
Faɗin Malik Cangaz, Asra ta gyaɗa kai, a tare suka taka zuwa wata kusurwa dake cikin filin, wadda ta fitar da su (balcony) dake can saman fadar, daga wurin ma za ka iya hango gine-ginen gidaje masallatai da kuma kasuwar masarautar kaf.
“Zuwa yanzu kwanaki uku kacal suka rage a ɗaura auren Iqrah da yariman Azad... Duk wasu shirye-shirye mun kammalasu, ɓangaren tsaro ne ba mu yi komai ba, dan haka ina so a tabbatar da tsaro a masarautar nan, domin akwai tarin baƙin da za su zo daga baƙin masarautun da suke maƙotantaka da mu... Ba na son a samu wani kuskure!”
Asra ta jinjina kai tana saƙala gashin kanta a bayan kunnenta.
“Zan tabbatar da hakan Darvesh...”
“Zuwa gobe zan je kaiwa abokina sarkin Mamlakatul Dahi goron gayyata, domin ba na so na aika Manzo! Na fi so na je da kaina domin isar da saƙon... Dan haka ki shirya, ina so ki min rakiya!”
Asra ta risina cikin girmamawa.
“An gama Darvesh...”
“Na sallameki”
Da haka ta juya ta barshi tsaye a wurin yana kallon girman masarautarsa. Kafin kuma amintaccen hadiminsa ya shigo wurin a hanzarce.
“An kamo matasan da ake zargi da cin amanar ƙasarmu ta hanyar fitar da bayanan kasuwancinmu na sirri ya shugabana!”
Cewar hadimin, bayan ya kwashi gaisuwa. Malik ya dube shi cike da isa, sannan ya furta.
“A kai min su kurkukun cikin ƙasa, a gana musu azaba ta mako guda, kafin na kai ga zartar da hukuncin da ya dace a kansu, kafin su mutu ina so su ɗanɗana azabar da za ta bawa duk wani me sha'awar aikata laifi irin nasu tsoro!”
Hadimin ya risina cikin alamar dake nuna ya karɓi saƙon shugaban nasa.
“An gama ya kai wannan adalin sarki!”
Daga haka shi ma ya fita daga wurin ya barshi, tsaye cikin sallalamin jiran ranar da boka Jalis zai sake naimansa. Domin tun bayan ranar da suka haɗu a kan maganar gano matasan nan uku bai sake naimansa ba, kuma hakan na nuna cewa har yanzu boka bai gano inda suke ba. A tsarinsa shi kuma ba ya zuwa wurin bokan ba tare da bokan ya naime shi ba... Amma a wannan karon dole ya karya ƙa'idar, dole ya je ya ji yanda aka yi aka haihu a ragaya.
MAMLAKATUL AFSAH.
Cike da zaƙuwa Malik Safraz ya ɗaga kai ga tawagar ɓoyen da yakan aika domin bincike, ya ƙagu su sanar da shi inda takobin mulkinsa yake.
“Ya shuganmu, haƙiƙa takobinka ya bayyana a ban ƙasa, sai dai samunsa shi ne abu mai matuƙar wuya a gareka!”
Muryar ɗaya daga cikinsu ta furta, ba tare da ya bayyana ba, domin ko shi kansa ba ya iya ganinsu sai idan sun so hakan. Ya ɗaga kansa ya kalli saitin inda maganar ke tashi, sannan ya furta.
“Shin har akwai wani abu da zai gagareni samu a faɗin wannan duniyar?”
“Ƙwarai kuwa ya shugabanmu, kuma wannan takobi na ɗaya daga ciki!”
“Me nene dalilinku na faɗin hakan?”
“Wanda yake tare da takobin shi ne abin ji, domin ko da yankar naman jikinsa za'ayi a kan takobin nan sai dai a yi, amma ba zai taɓa bari a raba shi da wannan takobi ba...”
“Waye shi?”
Malik Safraz ya tambaya ransa na ɓaci.
“UWAIS!”
Muryoyi uku suka ba shi amsa take, a nan ne fa hantar cikinsa ta fara motsi, domin in har Uwais ko Feroza na raye a ban ƙasa mulkinsa na cikin haɗari!... Ke nan me ya kamata ya yi a wannan gaɓar!?... Tambayar ta tuno masa da wata hatsabibiya ɗaya da zai iya sawa wannan aikin hankali kwance. Lokaci guda ya yi murmushi, sai kuma ya haɗa da dariya yana jinjina kai, sannan laɓɓansa suka furta sunanta.
“NATILA!”
GARIN QUDWA, YANKIN GABASHIN SAHARAR SUBAH.
Hayaniyar jama'ar dake kaikawo a cikin 'yar ƙaramar kasuwar garin ce ta cika ko ina. Komai na kayan siye da siyarwa daga ƙasashen duniya akan kawosu kasuwar wannan gari na Qudwa. Domin garin ya kasance cibiyar kasuwanci, duk da garin bai cika girma ba.
Ko wani mutum dake cikin kasuwar za ka same shi sanye da shiga irin ta garinsu ko yankinsu, ko kuma masarautarsu. Yayin da ake hada-hadar cinnikayya a cikin kasuwar. Wata iska me ƙarfi ta taso daga cikin sahararar dake gabas da kasuwar, hakan yasa ƙura ta shiga bule mutanen cikin kasuwar. Kafin wata guguwa ta shigo cikin kasuwar, sannan ba ta sauƙa a ko ina ba sai kan rufin wani shago.
Kaɗan-kaɗan iskar ta fara raguwa, har ta ɗauke gaba ɗaya. Yayin da wannan guguwar ta rikiɗa zuwa wata doguwar budurwa. Sanye cikin baƙaƙen kaya, ta yi kitso guda biyu a kanta, tsayin jelar kitson har cinyoyinta. Fuskanta kuma a rufe yake, a hankali ta yi tsugunnon mage a kan rufin shagon, sannan ta shiga baza idonta a kan mutanen dake kai kawo...
Dan iskar da ta taso ba ta sa kasuwancin da ake gudanarwa ya dakata ba, sautin murmushin da ta yi ya fito tare da motswar ƙyallen da ta rufe fuskarta da shi, domin ta hango abin harinta, ci gaba ta yi da bin sawunsa, har ta ga sanda ya shiga wani loko da take da tabbacin babu kowa ciki.
Take ta ɓace daga saman shagon, kuma ba ta bayyana a ko ina ba sai a cikin lokon, sannan a gaban mutumin da take bibiya. Shi kansa mutumin da ya ganta sai da ya razana, hakan ya sa kayan dake hannunsa suka zube a ƙasa, ya ɗaga hannayensa sama kamar me laifi.
A wannan karon budurwar dariya ta yi, sannan ta buɗe fuskarta, kyakkyawar fuskarta ta bayyana gare shi, haƙika tana da kyau, amma kyawun ɗan maciji. Lokacin da ya ganeta bai san sanda ya saki fitsari a wando ba, jikinsa ya soma kyarma, domin ganin NATILA na dai-dai da ganin mutuwar mutum.
“Sannunmu da sake haɗuwa, Malam Ayyaz!”
Jikin Ayyaz na rawa ya shiga ja da baya yana son bata haƙuri, cikin wani irin sauri da ya ɗararma hankali ta isa gabansa, sannan ta saka hannayenta ta riƙe wuyansa.
“Dole na kasheka, sannan na ciro zuciyarka na kaiwa shugabana, na masa alƙawarin sadaukar masa da zuciyarka a daren yau!...”
Ta ƙarashe maganar wasu zaƙa-zaƙan fiƙoƙi na fitowa daga haƙwaranta na sama. Sannan ta kafasu a wuyansa, nan take Ayyaz ya fara shure-shure, amma Natila ba ta saki wuyansa ba sai da ta zuƙe fiye da rabin jinin jikinsa. Duk da haka ba ta ƙyale shi ba, da ta saki wuyan nasa ta ɗaga hannunta me yalwar dogayen farata, ta caka a ƙirjinsa, sannan ta ciro zuciyarsa, kana ta saki gangar jikinsa ta faɗi ƙasa.
Zuciyar dake riƙe a hannunta ta kalla, bakinta duk ya ɓaci da jinin jikinsa, ta sa bayan hannunta goge bakin nata, sannan ta sake rufe fuskarta, ta tsallake gawarsa ta ɓace a iska.
Salma Ahmad Isah ✍️
___________
_😳 Akwai matsala!_
_Ko su waye suka kama ADVENTURERS ɗinmu?. Shin ya za a yi su kuɓuta?_
_Batun wannan Natilar! Ya kuke ganin haɗuwarta da ADVENTURERS ɗinmu za ta kasance?._
_Book 1 ya kusa ƙarewa, dan haka ya kamata a fara biyan kuɗin book 2 tun yanzu._
5487270431
Salma Isah
Monie point
Shaidar biya kuma ta 08130172704.
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
🪄 ...JUYIN KWAƊO...🪄
©️Salma Ahmad Isah
SalmaAhmadIsah @ArewaBooks
SalmaAhmadIsah @Wattpad
Page-13
ADVENTURERS.
Kukan Adam shi ne ya cika ɗan ƙaramin akurkin da aka cusasu ciki, dan duka su huɗun tare da wata mata da ba su santa ba na cikin wani abu me kamar keji, yayin da mutanen da suka kamosu ke zaune kusa da kejin, sun yi ayari suna gabatar da bautarsu zuwa ga wutar da suka hura, domin sun lura cewa mutanen wuta sukw bautawa.
Kuma bayan hasken wutar babu komai a wurin sai na farin wata da ya samu zarafin ratsowa ta jikin ganyen bishiyoyin da suke a ko ina na dajin, sai kuma na fitilun wayoyinsu da suka kunna. Tun bayan da mutanen suka kama su ba su musu komai ba, kuma ba su ce da su komai ba, sai kallonsu da suke ta yi tun ɗazu, kamar za su cinyesu.
“Mi shan Allah Adam skut! (Dan Allah Adam ka yi shiru!)”
Cewar Ivana cikin rarrashi, Adam ya goge hawayen da yake, yana duban Arman dake wurga masa harara, shi kuma Uwais kallonsu kawai yake yana murmushi, dan kukan da Adam ɗin ke yi dariya yake son ba shi.
“Ki bar ni na yi kuka, wata ƙila wannan shi ne kukana na ƙarshe, daga shi kuma ba zan sake ba!... Saboda waɗannan abubuwan yanka mu za su yi, ko su cinye, ko su bawa dabbobinsu!...”
Ya ƙarashe yana jingina kansa da jikin itatuwan da suka kafa kejin.
“Idan ba ka mana shiru ba sai na maka duka!”
Cewar Arman a ƙufule. Sannan ya ƙara da.
“Kalli Ivana, ko ita ba ta yi kuka ba sai kai, ƙaton banza kawai!”
Adam ya kame jikinsa yana ƙifƙita ido. A karo na barkatai, Arman ya sake haske matar da suka tarar a cikin kejin da fitilar wayarsa, amma har yanzu tana a yanda suka shigo kejin suka sameta. Dunƙule take a wuri guda, ta haɗa kai da gwiwa, kuma duka jikinta a rufe yake.
“Uwais ka tambaya mana wannan matar ko ta san abin da mutane nan suke so!...”
Cewar Arman yana gyara zaman glasses ɗinsa.
“Da ace za ta faɗa da ta faɗa tuntuni, tun yaushe nake mata magana? Amma ko tari ka ji ta yi?...”