← Book details Jariri Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 20

Sashe 7

Jariri Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

" Ita wannan layar ki saƙaleta aɗakinki zata taimaka miki na bunnuwar wasu sirrika na ki, wannan kuma ki binneta akan ƙofar shiga gidan masarautarku, bance zata Hana faruwar komai ba sai dai wannan layar zata hana tonuwar muhimmin sirinki musamman akan wance yaran, kinfi kowa sanin dai ba jinin Aminullahi ba ne hasalima ba jinin masarautar Kano bane, to ki saƙale ta gun da kikasan bazata faɗo ba, ita wannan ta ƙofar gidan wasu aljanune zasu miki gadin bakin ƙofar don hana ta shigowa, amma banda tabbaci yaƙini nake watakila shigowar Rayzuta gidan ya sa ta faɗowa wata ƙila kuma bazata faɗo ba, kuma na lura da faɗuwar gaba a duk lokacin da zaku haɗu da ita wannan yarinyar, sai ki riƙe wannan duk lokacin da kikaji faɗuwar gaba ki dinga lura da waɗanda suke tare da ke, ni nayi iya yi na ku tashi ku bani guri "

Jakadiya dake gefe tsumu tayi najin kalaman boka cikin zuciyarta ta ke faɗin, " Au dama Salman ba jinin Takawa bane? Lallai duk inda makirci ya je Fulani Maryama ta kai cen, babu ko tantama ɗan wajen Fulani Zulaiha shi zai zama magajin Izza, muje zuwa mahaukaci ya hau kura na tabbata akwai ranar da Ya zata ɗakin Ƙanwa, Fulani Maryama kinyi shuka a idon makwarya, lokaci na nan zuwa da kwaɓarki zatai ruwa, tafiya sannu-sannu kwana nesa. "

Kamar Fulani Maryama tasan abinda yake ran Jakadiya aikuwa ta juyo cikin tsuke fuska ta fara mata magana, " Jakadiya duk abinda kika ji agurin nan ki tabbata da ya zama sirri banasan kowacce magana ta fito daga bakinki, bakinki ƙanin ƙafarki, kinsanni sarai kinsan wacce Fulani Maryama bani da kyau banida daɗi, idan na sake naji wata magana ta ɓilla waje to daga gareki ne, kuma insa a hallakaki ba abu ne mai wuya agurina ba "

Jakadiya sarai ta san Fulani Maryama zatayi abinda yafi haka ma ta rissinar da kai ƙasa ta ce, " Wane ni da wannan ɗanyen aikin ya Shugabata indai wanda ya mutu zai dawo to maganar nan zata tashi, ai duk wanda ya ƙona rumbunsa yasan inda toka take tsada, ina ni ina bayyana sirrin Uwar gijiya ta idan nai haka ai kamar na daɓawa kaina wuƙa ne "

Fulani Maryama ɗauke kanta gefe tayi tana faɗin, " Ki tabbatar da kin kiyaye abinda kika faɗa domin ni ginshiƙin dutse ce kowa yayi karo dani shi ka faɗi, idan kunne yaji gangar jiki ta tsira " Jakadiya haɗiye yawu tayi mai ɗaci saboda jin haushin maganar Fulani, cikin zuciyarta ƙwafa tayi ta ce, " Tunkafin ahaifi uwar mai sabulu balbela ta ke da farinta, Fulani Maryama dani kike zance wallahi duk wannan wulaƙancin da kike mun akwai lokacin da zan farke miki laya. "

" Muna godiya Ubangidana maganin kuka na dukda yau ce rana ta farko da zan fita daga kogon dutsen bada biyan dukkan buƙata ba, amma ni mai bin umarnin ka ce akan duk abubuwan daka gindaya mun, tsafi ya dafa hatsabibancin ka ya cigaba da wanzuwar har ƙarshen zamani " Fulani Maryama ta faɗa tana karɓar layun da ya bata.

Cikin jindaɗin kirarinta ya ce, " Taɓewa ta tabbata ga mai yin shirka kije tukwicin aikinmu na ga cikin bayin Masarautar ku kamar yanda muka saba duk lokacin da kuka ziyarce mu, zan ƙara miki tuni idan kun wayi gari da mutuwar wani bawan babu ku babu cin kayan sadakar inba haka ba zaku bishi, ku fice daga kogon dutse kuna masu ambatan sunan mu " yana gama faɗa ya ɓace daga gurin, Jakadiya da Fulani tashi suka yi suka fita, suna zuwa bakin kogon dutsen Fulani ta kuma runtse idonta tana karanta ɗalasiman tsafin, atake haske ya kuma mamaye su suka ɓace daga gurin.

Lokacin da suka koma cikin Masarautar tuni dare ya tsala babu motsin komai sai kukan tsuntsaye da ƙananan dabobbi, Fulani karɓar Salman tayi dake hannun Jakadiya sannan ta ce mata, " Ƙuda wajen kwaɗayi akan mutum ina fatan baki manta maganar boka ba " rissunawa Jakadiya tayi ta ce, " Ina ankare ya shugaba ta "

_UMMOU ASLAM BINT ADAM_😉
[13/10, 19:37] Ameera Adam🌚: ☀️ *FIRST CLASS WRITERS ASSO*☀️

*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*
https://www.facebook.com/groups/856755331683130/?ref=share

👹 JARIRI 👹
Labari da Rubutawa: AMEERA ADAM

SADAUKARWA GA ƳAN GROUP ƊINA NA AMEERA ADAM FANS GROUP

GARGAƊI
BAN YARDA A SAUYA MUN LITTAFIN NAN TA KOWACCE SIGA BA BATARE DA IZININA BA.

7&8

Goggo waigawa tayi jin babu wanda ya tako hanyar ɗakin domin kawo mata a gaji ta buɗe baki ta kuma magana da ƙarfi ta ce. "Jama'a ku dubeni ku dubi tsufa ku taimaka mun zai hallakani da raina, ku zo ku fitarmun da shi yau na shigesu nikam ina ganin salawaitun rayuwa" Wani uban tsalle Jaririn ya buga har sai da zanin Goggo ya ɗaga sama sannan ya fito ya cigaba da dafe ƙeya yana wani irin rangaji sannan yayi tsalle ya faɗa cikin robar wankan, ga mamakin Goggo sai ji tayi ya fara magana cikin wata iri gwarjejiyar murya kamar ta ƙaton gardi yace. "Ko da wasa naji kin buɗi baki da niyyar magana sai shaƙe miki wuya kin mutu har lahira" Goggo buɗe baki tayi tana zaro idanu ana cikin haka su Inno suka shigo ɗakin da sauri Nusaiba ta ce. "Goggo lafiya naji kina ta kurma ihu" Inno ta hau tattaɓa kafaɗar Goggo ta ce. "Oh ni jikar mutum huɗu Hansai ince dai wannan ɗan ƙundalon Jaririn ba wani rashin ɗa'ar yayi miki ba, dan wannan ihun ɗiban albarkar ba banza ba" Goggo ido ta zurawa Inno tana jin bayaninta sai kuma ta tuno da kashedin da Jariri ya yi mata, nuna hannu ta fara yi irin na kurame tana gunguni da baki kamar yadda kurame suke yi idan zasuyi magana.

Goggo nuna Jariri tayi da hannu sannan ta ɗan bankaɗa zaninta tana nuna mata, Nusaiba ta ce. "Goggo kiyi magana mana kya dinga bankaɗa zani me zamuyi a ciki" Goggo ta kuma kallan Jaririn ta bankaɗa zani sannan ta nuna gado, sai kuma ta nuna dai-dai maƙogaronta. Inno ta rafka salati ta ce. "Yau naga abinda ya tsone idon Kakata Laure mun shigesu Hansai Kurumcewa kikayi?" Goggo kasa magana tayi ta kuma nuna Jaririn ta bankaɗa zaninta ta ce. "Ummmm ummmmm" Inno ta riƙe baki ta ce. "Hansai ban fahimci ɗiban albarka da kike nuna mun ba ta bankaɗa zani, wai ko haihuwa kike sha'awar yi" Goggo da sauri ta gyaɗa kai sai kuma ta nuna Jaririn ta ce. "Ummmm ummmmm" Inno ta ce. "Yoooooo Hansai ko sharafa kike yi ke da haihuwa ai har abada banƙi ba ko a lahira idan anayi, amma wallahi ina jiye miki tsoron ɗiban albarkar da yaron nan yayi mun yayi miki shi a cikin zanin nan da kike ta bankaɗawa." Goggo na jin haka ta fara gyaɗa kai tana cewa. "Ummmmm Ummmm"

KUYI HKR BAN ZAUNA BA DANMA NA MUKU ALƘAWARI NE.

_UMMOU ASLAM BINT ADAM_😉
[15/10, 19:49] Ameera Adam🌚: ☀️ *FIRST CLASS WRITERS ASSO*☀️

*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*
https://www.facebook.com/groups/856755331683130/?ref=share

👹 JARIRI 👹
Labari da Rubutawa: AMEERA ADAM

SADAUKARWA GA ƳAN GROUP ƊINA NA AMEERA ADAM FANS GROUP

GARGAƊI
BAN YARDA A SAUYA MUN LITTAFIN NAN TA KOWACCE SIGA BA BATARE DA IZININA BA.

9&10

Inno ta rafka salati tana tafa hannuwa haɗe da karkata kai ta ce. "Wannan bankaɗar ɗiban albarkar da kike mana na meye haka Hansai?" Nusaiba da takaici ya rufeta ta ajiye kayan Jaririn a kan gado ta fice daga ɗakin dan yin wanka, Inno sunkuyowa tayi ta ce. "Hansai ki dubi Allah kimun magana karfa daga wasa abu ya zama gaske dan wannan ɗiban albarkar ya fara bani tsoro" Goggo ta sauke wata ajiyar zuciya murya na rawa ta ce. "Rakiya babu komai lokaci ɗaya ne kawai naji salawaitun bakina ya ɗauke" Inno ta taɓe baki ta ce. "Wallahi keda Allah ƙarya kuma haramun ce amma duk wanda ya ƙare miki kallo yasan kina cikin halin rashin ɗa'a, wallahi badan ina duba zumuncin Allah ba da tuni na kwashe miki albarka yadda kika faɗar mun da gaba, haka kawai ki ɗora mun ciwo ki cuci ƴaƴana ki barsu da jinya suna kashe kuɗaɗe banda ma Allah ya rufa musu asiri, Kai duniya ni jikar huɗu Hamsai ina zaki bar mugun hali? Kiyi ki wanke musu ɗa kin tsaya bankaɗe-bankaɗen ɗiban albarka." Inno ta ƙarasa faɗa tana wucewa cikin ɗakin, kamar wacce ta ga mugun abu da sauri Inno ta dafe ƙirjina tana zaro ido ta ce. "Hansai waya yiwa jika ta wannan rashin ɗa'ar da labulaye, Oh nikam yau naga abinda ya tsone idon kakata Laure anya wannan ɗanƙundalon yaron aljannu basu mulmuleshi ba" Goggo cikin suɓutar baki ta yarfe hannu gefe ta ce. "Yoo Allah na tuba ba dole kiga sabon salawaitun abubuwa ba, muna tare da Ƙunduss..."

(ME SAN JIN YADDA NA SAMO SUNAN ƘUNDUSS YA NEMI LITTAFINA NA ƊAN BA ƘARA🤣 WOLLAH DARIYA SAI TA KUSA SAKU FITSARI A ZAUNE)

Da sauri Goggo tasa hannu ta rufe bakinta tana zare idanu kamar wacce tayi saɓo sabida tuno kashedin da jariri yayi mata, Inno ta dafe ƙirji ta ce. "Allahu Akabar kabiran Alhamdulillahi kema ya nuna miki ɗiban albarkar ko" Goggo da tayi fiƙi-fiƙi da idanu ta ce. "Waye kuma?" Inna ta keɓe baki ta ce. "Ina ce da wannan ɗan ƙundalon kike?" Goggo da sauri ta ce. "Nina gaya miki wallahi karki zabga mun sabuwar salawaitin ƙarya ido biyu, abinda baki sani ba wannan Jaririn ya fi mun ke sau dubu" Inno ta zaro ido ta ce. "Jaririn da kika sani jiya-jiya shine ya fini a gurki saboda ɗiban albarka" Inno ta fara matsar ƙwallanta ce. "Yanzu saboda uban yaron nan na da abun duniya ko Hansai?" kafin Goggo tayi magana Halifa ya shigo cikin ƙananan kaya ba ƙaramin kyau yayi ba, Inno washe baki tayi tace. "Halifun har an fito" Halifa yace. "Goggo wai har yanzu ba'ayi masa wankan ba? So nake fa na kaisu asibitin nan da wuri inasan na shiga office da wuri"
Chapter 7 · 0% Book details