Sashe 13
Jariri Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A gagguce ya fara musu bayani dan ba ƙaramin shaƙa ya sha a hannun Goggo ba.
"Barrister ba wani babban ciwo bane yake damunta ta ɗan shiga firgice ne na ɗan wani lokaci, amma da zarar ta tashi daga bacci zata koma normal. Akwai magungunan da zata dinga sha zan rubuta musu sai a siyo mata, kar a dinga yawan barinta ita kaɗai saboda kar ta dinga yawan tunani.
Yana gama faɗa ya fice daga falon ko waiwaye baya yi, Goggo miƙewa tayi ta ƙarasa gaban Inno da take bacci tana ƙarasawa ta share hawayenta a hankali ta ce. "Allah ya baki salawaitun lafiya Rakiya" Daddy da Abba babu wanda ya tanka mata gabaɗaya suka fice daga falon.
Inna sai da ta shafe sama da awa huɗu tana bacci sannan ta farka, tana farkawa a cen gefe ta hango Goggo tana ta zabga gyangyaɗi a hankali ta ce. "Hansai" da sauri Goggo ta buɗe ido aikuwa tana ganin Inno ta tashi zaune ta fara yekuwa a cikin falon, nan da nan mutanen gidan suka ɗauko zuga suka shigo falon.
Tana hango Nusaiba da Halifa ta miƙa hannuwa biyu ta ce. "Ku matsa wallahi karku ƙaraso mini idan ba haka ba sai na ɗebe muku albarka duk kun ɓalɓace." Kallan kallo aka fara yi kowa yana kallan ɗan uwansa babu wanda ya fahimci ga da wanda take. A hassale Inno ta ce. "Halifa wallahi ko a lahira na ganku a kusa da ni saina ɗebe muku albarka." Halifa baya ya ja a hassale ya ruƙo hannun Nusaiba zasu fita. Nusaiba ta marairaice fuska ta ce. "Hubby karka biyeta kasan rikici irin na su Inno" Inno na jin haka ta ce. Uwarki ce me rikici sakarya maras ɗa'a kai Salisu wallahi idan baku dakatar da su Halifa ba zan bar muku gidanku na shiga duniya dan na Allah basa ƙarewa." Goggo tayi karaf ta ce. "Wallahi ƙafa ta ƙafarki dan ba zan zauna ganin salawaitun rashin ɗa'a da cin mutumcin da za'a yi wa ƴar uwa ta ba."
Halifa da sauri ya fisgi hannun Nusaiba suka fice daga ɗakin yana huci ya wuce falon su Hajiyansa.
Bayan kwana biyu jikin Inno ya dawo dai-dai kuma Halifa da Nusaiba sun dawo gida gabaɗaya da zama saboda Inno da Goggo sun ce Allah ya kashe su bazasu ƙara zuwa gidansa su zauna ba, Kuma tun daga ranar babu wani abun firgici da suka ƙara gani. Ana gobe suna gidan cike yake da baƙi daga ɓangare daban-daban, Kayan miya a sayo da kayan abinci kala-kala na ƴan suna. Kayan drinks da kayan gift ɗin da za'a bawa ƴan suna.
Da daddare bayan sallar isha"i Hajiyan Halifa ta shiga cikin store, tana shiga kamar almara ta hango ɗan dunƙulallen mutum ya juya bayansa. A gaban kabewa ta hangoshi ya zage iya ƙarfinsa sai gwaguyar kabewa yake, jikinta na tsuma ta ja gefe banda karkarwa babu abin da take ji, Jariri na jin motsinta ya juyo hannunsa ɗaya ɗauke da rabin ƙatuwar kabewa, da sauri ya fara takowa yana tafe yana tura ciki gaba yana wata rangwaɗa. Yana zuwa gabanta ya fisgota da ƙarfi har ta kai ƙasa, kabewar hannunsa ya miƙa mata cikin wata irin murya yace. "Ungo zauna ku sha tare" Jariri ɗuk abin da ya gani ya ɗauka ya ci idan ya rage sai ya wurgowa Hajiyan Halifa yace ta cinye. Fakar idonsa tayi ta miƙe saɗaf-saɗaf ta fice daga store ɗin, har ta kusa shiga babban Falo ta Jariri ya ta ho da gudu ya cafko zaninta, Hajiyan Halifa iya ƙarfinta ta zage ta fara kwarara ihu. Jariri bai fasa ba har sai da ya ga ya fisge zanin jikin ta.
_UMMOU ASLAM BINT ADAM_😉
[06/11, 16:06] Ameera Adam🌚: *FIRST CLASS WRITERS ASSO*☀️
*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*
https://www.facebook.com/groups/856755331683130/?ref=share
👹 JARIRI 👹
Labari da Rubutawa: AMEERA ADAM
SADAUKARWA GA ƳAN GROUP ƊINA NA AMEERA ADAM FANS GROUP
GARGAƊI
BAN YARDA A SAUYA MUN LITTAFIN NAN TA KOWACCE SIGA BA BATARE DA IZININA BA.
23&24
Hajiyan Halifa na ganin ya fisgi zaninta daga ita sai ɗan fatarin ciki ta miƙe ta shiga cikin falon, da sauri tafi da gudu ya cafko siket ɗinta yana niyyar fisge shi shima gabaɗaya. Da ƙyar ta saau tayi ta maza ta hamɓare shi da ƙafa ta samu ta shige cikin Ɗaki, Daddy na zaune ya ga shigowarta da sauri ta banka ƙofar ta rufe. Daddy da mamaki yake kallonta yace. "Mommyn yara lafiya me yake damunki?"
Mommy dake sauke haki ta ce. "Wallahi aljani ne ba mutum ba jaririn Halifa aljani ne da idona naga yana cin Kabewa" zaro ido waje Daddy ya yi yace. "Jariri kuma? Wai me yake faruwa ne ke kince Jariri su Inno sun ce Jariri wai kaina fa ya kulle" Mommy ta ce. "Wallahi nima na gani da ido na, dubi fa har zani ya cire min Allah me kaɗai yasan abin da ya yi niyyar aikata mini, wallahi kamar wacce zai haikewa haka naga yana ƙoƙarin farmaka ta."
murmushin takaici Daddy ya yi yace. "Dan Allah ki daina faɗar haka karma wani yaji, kema ruɗa kanki zakiyi ne kamar yadda su Inno suke gigita kansu, wannan zancen banza ne dan Allah wuce ki ɗau zani ki ɗaura Allah yasa ƴaƴanki basu ganki a haka ba." Mommy ta ce. "Amma fa..." Ya katse ta. "Amma me?" ki wuce ina da abin yi banasan jin wani abu." Cikin ƙunan rai Mommy ta wuce tana ƙwafa dama tasan idan zata kwana tana faɗa bazai yarda ba.
Cikin tsakiyar dare Daddy ne zaune a falo ya jona laptop yana wani aiki, gidan shiru babu motsin komai sai ƙarar keyboard ɗin laptop ɗin da yake dannawa. Yana nan zaune yaji an jefo wani abu da ƙarfi, yana waigawa yana ƙafafauwan ragon guntulallu da jini yaɓe-yaɓe a jikinsu, da sauri ya zaro ido cikin mamaki yana ture Laptot ɗin gefe.Yana ƙoƙarin tashi ya takun tafiya ƙwas ƙwas ƙwas yana kallon bakin ƙofar yana Jariri hannunsa saɓe da kan rago ya rungumo shi gigin-gigin kamar zasu faɗi tare, Jikin Daddy ne fara ɗaukan tsuma yana yunƙurin tashi ya ga Jaririn ya datse ƙofar falon sannan ya sunkuyo da kan ragon yana lasar jinin da ke ɗiga daga jikin kan ragon.
Daddy ja ya fara yi da baya yana karkarwa da sauri Jariri ya wurga masa kan ragon yace. "Ungo tayani ci tunda da kai muka haɗu." Daddy kallan kai ragon ya yi yaga anyi masa ɓuloli ta ko'ina, tsugunnawa Daddy ya yi yace. "Dan Allah ka yi haƙuri ka mun rai bazan iya cin ɗanyan nama ba." Jariri kallan tsaf ya yiwa Daddy yace. "To cire rigarka" ba musu Daddy ya tuɓe rigarsa daga shi sai gajeren wando kuma har lokacin jikinsa sai ɓari yake." Jariri yace. "Wallahi ko ka ɗauki kan rangon kaci ka na saɓa kamanninka" Daddy ya tsaya yana kallon Kan jaron sunan da aka siyo na jaririn da za'a yanka, a zuciyarsa ya ce. "Ina ɗayan ragon badai shima ya cinye shi ba, ashe dai maganar su Inno a hanya take?" Jariri kamar yasan abin da yake zuciyar Daddy yace.
"Na cinye ɗayan ragon da kuka siyo ba dan ni kuka siyo ba? To wannan kai zaka cinye shi." Daddy yayi tsumu yana zare idanu, Jariri na ganin haka ya nufi gurun da Daddy ya jona laptop ɗinsa ya fisgo chager, riƙewa ya buga tsalle ya ranƙwalawa Daddy kan cazar a kansa da ya sha ƙwaryar molo. Daddy durƙushewa ya yi a gurin yana lailaya kai cikin azaba, bai yi aune ba yaji Jariri ya kuma rankwala masa a kai.
Cikin tsananin azaba Daddy ya dafe kai yana cewa. "Wayyo Allah jama'a ku cece ni zai kashe ni" Jariri tsalle ya buga ya dira a kan tumbulelen tumbin Daddy ya fara sukuwa a kai, Daddy tun yana iya roƙo har ya fara kasa magana. Jaririj ɗaga shi ya yi, ya koma kan kujera ya zauan. Wani tsoronsa ne ya ɗarsu a zuciyar Daddy saboda wahala ko motsi ya kasa yi. Daga gurin da yake Jaririn yace.
"Tashi tsaye" Daddy jiki na ɓari ya yunƙura da ƙyar ya tashi kansa har yayi ƙullutu biyu gurin da Jariri ya ranƙwala masa kan caza. Daddy na tsaye Jariri yace. "Maza kayi mini rawar Ɗan maliyo maliyo" Daddy hawayen wahala yake yi yace. "Ranka ya daɗe wallahi ban iya ba" yana rufe baki Jariri ya diro ƙasa ya dafe kai da hannu ɗaya, ɗayan hannun kuma ya dafe ƙugu da shi, turo ciki gaba ya fara yi idan ya yi taku ɗaya sai ya tura baya har wata rangwaɗa yake yi yana cewa. "Ɗan maliyo maliyo, maliyo. Ɗan maliyo nawa, Maliyo." idan yace maliyo sai ya dafe ƙeya ya girgiza ciki.
Yana gamawa yace. "Maza kayi irin rawar da nayi yanzun nan" Daddy hannunsa biyu yasa ya riƙe ƙugu yana yana cewa. "Ɗan maliyo maliyo, maliyo."
(🤣🤣😂 Mai karatu ka harsaso min muryan Daddy yana waƙar ɗan maliyo maliyo)
Jariri na jin haka ta ja guntun tsaki ya fisgi cazar laptop ɗin ya ƙara ranƙwala Daddy a ka yace. "Haka nace masa hannuwa biyi zaka riƙe ƙugu da su? Ba hannu ɗaya a ƙugu ɗaya a ƙeyar ka zaka riƙe ba." Daddy kuka yake shaɓe-shaɓe ya miƙe ya ci gaba da dafe ƙeya yana tura tumbi gaba yana waƙa.
Sai da ya jima yana abu ɗaya har ya galabaita banda gumi babu abin da yake yi, Jariri ya dakatar da shi sannan yace. "Yanzu kuma rawar salawaitun salo zamuyi" A wahalce Daddy yace.
"Dan Allah ka yi mini rai" Jariri yace. "Ai mun dinga rawa kenan dana yanzu har wayewar gari kuma wallahi duk wanda ka gayawa yadda na gwaguye kan ragon cen haka zan yi maka" Daddy ya hau muzurai yana raba ido wannan karan hawaye sharara yake yi.
"Barrister ba wani babban ciwo bane yake damunta ta ɗan shiga firgice ne na ɗan wani lokaci, amma da zarar ta tashi daga bacci zata koma normal. Akwai magungunan da zata dinga sha zan rubuta musu sai a siyo mata, kar a dinga yawan barinta ita kaɗai saboda kar ta dinga yawan tunani.
Yana gama faɗa ya fice daga falon ko waiwaye baya yi, Goggo miƙewa tayi ta ƙarasa gaban Inno da take bacci tana ƙarasawa ta share hawayenta a hankali ta ce. "Allah ya baki salawaitun lafiya Rakiya" Daddy da Abba babu wanda ya tanka mata gabaɗaya suka fice daga falon.
Inna sai da ta shafe sama da awa huɗu tana bacci sannan ta farka, tana farkawa a cen gefe ta hango Goggo tana ta zabga gyangyaɗi a hankali ta ce. "Hansai" da sauri Goggo ta buɗe ido aikuwa tana ganin Inno ta tashi zaune ta fara yekuwa a cikin falon, nan da nan mutanen gidan suka ɗauko zuga suka shigo falon.
Tana hango Nusaiba da Halifa ta miƙa hannuwa biyu ta ce. "Ku matsa wallahi karku ƙaraso mini idan ba haka ba sai na ɗebe muku albarka duk kun ɓalɓace." Kallan kallo aka fara yi kowa yana kallan ɗan uwansa babu wanda ya fahimci ga da wanda take. A hassale Inno ta ce. "Halifa wallahi ko a lahira na ganku a kusa da ni saina ɗebe muku albarka." Halifa baya ya ja a hassale ya ruƙo hannun Nusaiba zasu fita. Nusaiba ta marairaice fuska ta ce. "Hubby karka biyeta kasan rikici irin na su Inno" Inno na jin haka ta ce. Uwarki ce me rikici sakarya maras ɗa'a kai Salisu wallahi idan baku dakatar da su Halifa ba zan bar muku gidanku na shiga duniya dan na Allah basa ƙarewa." Goggo tayi karaf ta ce. "Wallahi ƙafa ta ƙafarki dan ba zan zauna ganin salawaitun rashin ɗa'a da cin mutumcin da za'a yi wa ƴar uwa ta ba."
Halifa da sauri ya fisgi hannun Nusaiba suka fice daga ɗakin yana huci ya wuce falon su Hajiyansa.
Bayan kwana biyu jikin Inno ya dawo dai-dai kuma Halifa da Nusaiba sun dawo gida gabaɗaya da zama saboda Inno da Goggo sun ce Allah ya kashe su bazasu ƙara zuwa gidansa su zauna ba, Kuma tun daga ranar babu wani abun firgici da suka ƙara gani. Ana gobe suna gidan cike yake da baƙi daga ɓangare daban-daban, Kayan miya a sayo da kayan abinci kala-kala na ƴan suna. Kayan drinks da kayan gift ɗin da za'a bawa ƴan suna.
Da daddare bayan sallar isha"i Hajiyan Halifa ta shiga cikin store, tana shiga kamar almara ta hango ɗan dunƙulallen mutum ya juya bayansa. A gaban kabewa ta hangoshi ya zage iya ƙarfinsa sai gwaguyar kabewa yake, jikinta na tsuma ta ja gefe banda karkarwa babu abin da take ji, Jariri na jin motsinta ya juyo hannunsa ɗaya ɗauke da rabin ƙatuwar kabewa, da sauri ya fara takowa yana tafe yana tura ciki gaba yana wata rangwaɗa. Yana zuwa gabanta ya fisgota da ƙarfi har ta kai ƙasa, kabewar hannunsa ya miƙa mata cikin wata irin murya yace. "Ungo zauna ku sha tare" Jariri ɗuk abin da ya gani ya ɗauka ya ci idan ya rage sai ya wurgowa Hajiyan Halifa yace ta cinye. Fakar idonsa tayi ta miƙe saɗaf-saɗaf ta fice daga store ɗin, har ta kusa shiga babban Falo ta Jariri ya ta ho da gudu ya cafko zaninta, Hajiyan Halifa iya ƙarfinta ta zage ta fara kwarara ihu. Jariri bai fasa ba har sai da ya ga ya fisge zanin jikin ta.
_UMMOU ASLAM BINT ADAM_😉
[06/11, 16:06] Ameera Adam🌚: *FIRST CLASS WRITERS ASSO*☀️
*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*
https://www.facebook.com/groups/856755331683130/?ref=share
👹 JARIRI 👹
Labari da Rubutawa: AMEERA ADAM
SADAUKARWA GA ƳAN GROUP ƊINA NA AMEERA ADAM FANS GROUP
GARGAƊI
BAN YARDA A SAUYA MUN LITTAFIN NAN TA KOWACCE SIGA BA BATARE DA IZININA BA.
23&24
Hajiyan Halifa na ganin ya fisgi zaninta daga ita sai ɗan fatarin ciki ta miƙe ta shiga cikin falon, da sauri tafi da gudu ya cafko siket ɗinta yana niyyar fisge shi shima gabaɗaya. Da ƙyar ta saau tayi ta maza ta hamɓare shi da ƙafa ta samu ta shige cikin Ɗaki, Daddy na zaune ya ga shigowarta da sauri ta banka ƙofar ta rufe. Daddy da mamaki yake kallonta yace. "Mommyn yara lafiya me yake damunki?"
Mommy dake sauke haki ta ce. "Wallahi aljani ne ba mutum ba jaririn Halifa aljani ne da idona naga yana cin Kabewa" zaro ido waje Daddy ya yi yace. "Jariri kuma? Wai me yake faruwa ne ke kince Jariri su Inno sun ce Jariri wai kaina fa ya kulle" Mommy ta ce. "Wallahi nima na gani da ido na, dubi fa har zani ya cire min Allah me kaɗai yasan abin da ya yi niyyar aikata mini, wallahi kamar wacce zai haikewa haka naga yana ƙoƙarin farmaka ta."
murmushin takaici Daddy ya yi yace. "Dan Allah ki daina faɗar haka karma wani yaji, kema ruɗa kanki zakiyi ne kamar yadda su Inno suke gigita kansu, wannan zancen banza ne dan Allah wuce ki ɗau zani ki ɗaura Allah yasa ƴaƴanki basu ganki a haka ba." Mommy ta ce. "Amma fa..." Ya katse ta. "Amma me?" ki wuce ina da abin yi banasan jin wani abu." Cikin ƙunan rai Mommy ta wuce tana ƙwafa dama tasan idan zata kwana tana faɗa bazai yarda ba.
Cikin tsakiyar dare Daddy ne zaune a falo ya jona laptop yana wani aiki, gidan shiru babu motsin komai sai ƙarar keyboard ɗin laptop ɗin da yake dannawa. Yana nan zaune yaji an jefo wani abu da ƙarfi, yana waigawa yana ƙafafauwan ragon guntulallu da jini yaɓe-yaɓe a jikinsu, da sauri ya zaro ido cikin mamaki yana ture Laptot ɗin gefe.Yana ƙoƙarin tashi ya takun tafiya ƙwas ƙwas ƙwas yana kallon bakin ƙofar yana Jariri hannunsa saɓe da kan rago ya rungumo shi gigin-gigin kamar zasu faɗi tare, Jikin Daddy ne fara ɗaukan tsuma yana yunƙurin tashi ya ga Jaririn ya datse ƙofar falon sannan ya sunkuyo da kan ragon yana lasar jinin da ke ɗiga daga jikin kan ragon.
Daddy ja ya fara yi da baya yana karkarwa da sauri Jariri ya wurga masa kan ragon yace. "Ungo tayani ci tunda da kai muka haɗu." Daddy kallan kai ragon ya yi yaga anyi masa ɓuloli ta ko'ina, tsugunnawa Daddy ya yi yace. "Dan Allah ka yi haƙuri ka mun rai bazan iya cin ɗanyan nama ba." Jariri kallan tsaf ya yiwa Daddy yace. "To cire rigarka" ba musu Daddy ya tuɓe rigarsa daga shi sai gajeren wando kuma har lokacin jikinsa sai ɓari yake." Jariri yace. "Wallahi ko ka ɗauki kan rangon kaci ka na saɓa kamanninka" Daddy ya tsaya yana kallon Kan jaron sunan da aka siyo na jaririn da za'a yanka, a zuciyarsa ya ce. "Ina ɗayan ragon badai shima ya cinye shi ba, ashe dai maganar su Inno a hanya take?" Jariri kamar yasan abin da yake zuciyar Daddy yace.
"Na cinye ɗayan ragon da kuka siyo ba dan ni kuka siyo ba? To wannan kai zaka cinye shi." Daddy yayi tsumu yana zare idanu, Jariri na ganin haka ya nufi gurun da Daddy ya jona laptop ɗinsa ya fisgo chager, riƙewa ya buga tsalle ya ranƙwalawa Daddy kan cazar a kansa da ya sha ƙwaryar molo. Daddy durƙushewa ya yi a gurin yana lailaya kai cikin azaba, bai yi aune ba yaji Jariri ya kuma rankwala masa a kai.
Cikin tsananin azaba Daddy ya dafe kai yana cewa. "Wayyo Allah jama'a ku cece ni zai kashe ni" Jariri tsalle ya buga ya dira a kan tumbulelen tumbin Daddy ya fara sukuwa a kai, Daddy tun yana iya roƙo har ya fara kasa magana. Jaririj ɗaga shi ya yi, ya koma kan kujera ya zauan. Wani tsoronsa ne ya ɗarsu a zuciyar Daddy saboda wahala ko motsi ya kasa yi. Daga gurin da yake Jaririn yace.
"Tashi tsaye" Daddy jiki na ɓari ya yunƙura da ƙyar ya tashi kansa har yayi ƙullutu biyu gurin da Jariri ya ranƙwala masa kan caza. Daddy na tsaye Jariri yace. "Maza kayi mini rawar Ɗan maliyo maliyo" Daddy hawayen wahala yake yi yace. "Ranka ya daɗe wallahi ban iya ba" yana rufe baki Jariri ya diro ƙasa ya dafe kai da hannu ɗaya, ɗayan hannun kuma ya dafe ƙugu da shi, turo ciki gaba ya fara yi idan ya yi taku ɗaya sai ya tura baya har wata rangwaɗa yake yi yana cewa. "Ɗan maliyo maliyo, maliyo. Ɗan maliyo nawa, Maliyo." idan yace maliyo sai ya dafe ƙeya ya girgiza ciki.
Yana gamawa yace. "Maza kayi irin rawar da nayi yanzun nan" Daddy hannunsa biyu yasa ya riƙe ƙugu yana yana cewa. "Ɗan maliyo maliyo, maliyo."
(🤣🤣😂 Mai karatu ka harsaso min muryan Daddy yana waƙar ɗan maliyo maliyo)
Jariri na jin haka ta ja guntun tsaki ya fisgi cazar laptop ɗin ya ƙara ranƙwala Daddy a ka yace. "Haka nace masa hannuwa biyi zaka riƙe ƙugu da su? Ba hannu ɗaya a ƙugu ɗaya a ƙeyar ka zaka riƙe ba." Daddy kuka yake shaɓe-shaɓe ya miƙe ya ci gaba da dafe ƙeya yana tura tumbi gaba yana waƙa.
Sai da ya jima yana abu ɗaya har ya galabaita banda gumi babu abin da yake yi, Jariri ya dakatar da shi sannan yace. "Yanzu kuma rawar salawaitun salo zamuyi" A wahalce Daddy yace.
"Dan Allah ka yi mini rai" Jariri yace. "Ai mun dinga rawa kenan dana yanzu har wayewar gari kuma wallahi duk wanda ka gayawa yadda na gwaguye kan ragon cen haka zan yi maka" Daddy ya hau muzurai yana raba ido wannan karan hawaye sharara yake yi.