Sashe 3
Ibtihal Hausa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya na zama tare da cewa”zaki fara mitar tsohuwar nan toh ba na garin tafiya na yi shiyasa “
Ta ce “haka dai baku da aiki sai gantali a jirgi daga kai har uban naka”
Ya na taɓe baki ya ce”Ita kuma waccen fa yaushe ta dawo”
Ta na harararsa ta ce “ka shiga ka tambayeta munafuki saikace bai san da zuwan nata ba ko ba saboda ita ka shigo ba”
Ba tare da ya bata amsa ba ya miƙe tare da nufar ɗakin na ta “
Hajiya ta taɓa hannu ta ce “Eyye da gaske kuma shigar zakayi zo ka wuce don ubanka karka sake ka shigar mata ɗaki bana son taɓara ƙaton baligi dakai ka faɗa ɗakin yarinya”
Ko waiwayowa baiyi ba bare ta sa ran amsa.
Ibtihal na shiga ta ja dogon tsaki bacci ma takeji gwara ta kwanta ta huta da wuri hakan ya sanyata cire kayan jikinta tare da ɗaura Towel ta na niyyar juyawa ta nufi Bathroom ta ji an Banko ƙofar,
a matuƙar firgice ta waiga ganin mai shigowar ne ya sanya gabanta tsananta faɗuwa ran ta na tsananin ɓaci ta juya da sauri zata wuce toilet don gaba ɗaya ta duburce ta ji an kamo hannunta cikin sauri ta waigo sukayi ido huɗu dashi ta rumtse ido da ƙarfi ta na jin tamkar ta ɗauke sa da mari ta ce ……….✍🏽
https://chat.whatsapp.com/JYPWPtF78zlIr2kJcbp6ms?mode=gi_t
_*Miss Hajo ce*_🤙🏿
🪅*IBTIHAL*🪅
~MALLAKAR~
*HAJARA L SADEQ*
(miss Hajo)
MARUBUCIYAR👇🏼
Auren wata tara
Ni da yaya arman
Matar uncle
Najmat abiy
Komai mukaddari ne
Khadijatul Sabren
Ribar so
Mata ta ce
*And now*
*IBTIHAL*
*DEDICATED TO MY HUSBAND*
🅿️…………………………..*03*
Ta ce “Ba ka da hankali ne yaya Yusuf za ka shigo mun ɗaki ba neman izini ka sakemun hannu kar nayi maka abunda duk bazamuji daɗi ba”
Ba tare da ya sakar mata hannu ba ya ce
“meye zakimun duka na zakiyi ko zagi na watau da sabuwar rashin kunya kika dawo ko meye a ciki don na shigo ɗakin ki ba izini kin manta matsayina a wajenki yaya kuma miji nan gaba kaɗan gaba ɗaya ma abunda kike ɓoyewar bakya son na gani zai zama mallaki na “
Haushi ,Takaici gami da kunya ne suka lulluɓeta wani ɓacin rai takejin na taso mata ba tare da zato ba ta ji ya saki hannunta ya na taɓe baki ya ce idan kin gama wankan ki sameni a falo idan ba haka ba Allah na sake shigowa bazakiji da daɗi ba”
Ya na gama faɗar haka ya fice tare da zare makullin ɗakin ta bi sa da kallo saida ta ga ficewarsa kafin ta sauke nauyayyar ajiyar zuciya ta na jan dogon tsaki tare da nufar Toilet ba ta wani ɓata lokaci sosai ba wajen wankan ta fito shiri tayi cikin kayan bacci silver masu masifar kyau riga da wando yalwaltaccen gashin kanta da ke ta sheƙi da ɗaukar ido ta tace da mataci wanda ni kaina tsawon gashin da sulɓin saida ya masifar burgeni turaruka masu sanyin ƙamshi ta fesa tare da gabatar da sallah don har wankan tsarki ta yi kasancewar perioud ɗinta ya ɗauke.
Ta na shirin kwanciya ta tuna Wancen mutumin ya cire key ya tafi da shi kuma ba kunya ta ishe sa ba zai iya dawowa tunda komai yayi mata ba dukansa ko zaginsa zatayi ba a ranta takejin tsanantar jin haushinsa,
Hijab blue black mai girma ta ɗora saman kayan baccin tare da fita ta na harhaɗe
Fuska,
Tunda ta fito idanunsa a kanta baisan sanda ya furta kalmar “Wow “ba “ ita komai ta saka sai ya mata kyau ne?”
ya tambaya kansa ya shagala da kallonta wanda har baisan ta zauna ɗaya daga cikin kujerun nesa da shi ba saida zazzaƙar muryarta ta doshi dodon kunnansa ya dawo cikin hayyacinsa ya na sauke ajiyar zuciya tare da amsa gaisuwar da tayi masa ya ɗora da cewa”ya aka gama karatun dukda baki faɗa mana dawowar ba bare mu shirya miki partyn graduation”
Hankalinta akan t v ba tare da ta kallesa ba ta ce”Alhmdulillah”ba tare da ta basa waccen amsar ba
Tashi ya yi daga kujerar da ya ke ya na komawa wacce take zaune 2sitter da sauri ta matsa ganin yanda Yake shirin shige mata harga Allah shiyasa bata so ba ganin ba hajiya a ɗakin don ta riga ta shige ciki ana isha’i dama ta ke kwantawa abinta,
Ƙara matsawa tayi murya ba wasa ta ce”meye haka yaya Yusuf”
Ya ce “Soyayya ce”
“Amma dai kasan babu kyau abunda kakeyi”
Ya na wani lumshe ido ya ce “meye marar kyawun “
Rasa da me zata amsa kawai tayi sai tsaki da ta ja a cikin ranta”
“Ya maganar Auren mu “
Ta tsinta muryarsa,
Ba tare da ta kallesa ba har lokacin idonta na kan tv dukda tana jin kusancin na su ya yi yawa ta ce”Daman munyi alƙawarin aure ne da kai?
“Hmmmm har yanzu ba ki janye kalamanki ba kenan amma kinsan a gobe na ga damar a ɗaura mana aure sai an ɗaura bana son ne na tilastaki shiyasa ko a baya na ƙyale har kika tafi ƙarin karatu”
Banza tayi ta ƙyalesa ta na jinjina Gadara da nuna iko na Yaya yusuf na daga dalilin da yasa kwata-kwata daman chan ba sa jituwa”
“Hmmm na kula kin dawo da sabon wulaƙanci karatun nan da kika dawo ko don kina ganin Kina Da PHD ina da Masters ko yanzu na ga daman zama DR ma zan zama don kar ki ga kamar kin fini ajin karatu ki rainani gaba nake dake a komai tunda Allah ma da kansa ya bamu wannan girman a kanku ko primary gareni ki sani gaba nake da ke don Haka ki aje girman kai mu fuskanci juna da bakya nan idan na daure yanzu bazan iya daurewa ba komai zai iya faruwa don haka ki bani hankalinki mu fuskanci juna”
Ba tare da ta basa amsar waccen tambayar ba ta miƙe tare da cewa” makullin ƙofar ta fa”
“Hmmm haka ma kawai zakice”
Ta ce “eh”
Ya na zare ɗaya daga cikin makullan ƙofar ya ce “Ga shi”
Ta na mamakin me zaiyi da makulli ta kallesa ta ce “ka mayar mun makulli na me zakayi dashi kuma “?
Ba tare da ya ba ta amsa ba ya miƙe tare da damƙa mata makullin a hannu ya na damƙar hannun kamar gaisuwa ya ce “Have a nice dream my beautiful wife”
tare da sumbatar hannun ya fice ta bishi da kallo sakaka tamkar sakarai kafin ta kalli hannunta da ya sumbata ta na jin takaici wasu hawayen takaici ta ji ya zubo mata ta wuce bedroom ta na hawaye zuciyarta chunkushe duk ba daɗi har ga Allah ba ta ƙaunar takurar nan da yaya faruq ke mata ita gaskiya ma sai ta bar gidan ma indai haka zaici gaba da mata”
“to ki bar gidan ki je ina kin manta mahaifinki ya muku iyaka da shi ko a waya ballantana gidansa da yayi muku korar kare”
“Innalillahi wa inna ilaihiraju’un wata Kewar Mahaifinta take ji har ƙasar zuciyarta dukda abunda yayi musu amma batajin tsanarsa ko kaɗan a cikin ranta”
Nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke ta na duba lokaci ta ga 10:30 tasan chan yanzu kusan 12 ma ta wuce kuma yanzu ta na tare da mijinta bai dace ta kirata a daidai wannan lokacin ba “Jiniour nasan yanzu baiyi bacci ba”
Ta faɗa ta na lalubo number sa saida ta kusan katsewa kafin ya ɗauka cikin muryar wanda ya fara bacci ya ce “Waye”
Ta ce “Sabuwar budurwarka da muka haɗu rannan”
Ta na jin sautin dariyarsa ya ce”Haba Aunty Ibtihal ko a mafarki akace na kasa gane muryarki ai zakice ba Jiniour ɗinki ba ne”
Ta ce “hummm ɗaɗin baki”
Ya ce “gaskiyace aunty na yi ta kiranki nayi miki sannu da zuwa ba ta shiga shine ko ki faɗa mun zaki dawo ƙasar da ko ƙaryar rashin lfy ne sainayi an barni na zo tarbarki”
Ta ce “nasan Exams kake shiyasa Bana son ka samu matsala a karatunka na so ma Zuwa Sch ɗin naku to da naga 10days ya rage ka dawo shiyasa na hakura don kasan nayi missing naka sosai bro”
Cike da zallar ƙauna ya ce”nima nayi matuƙar missing ɗinki aunty har bana son ayi hutu saboda idan nazo nasan bazan iske ki ba aunty ba ke ba momy ba Daddy dukda Shi daddy ba ya ƙaunarmu yanzu amma ai ita momy ta na ƙaunarmu amma itama ta rabu da mu ta zaɓi mijinta a kanmu a shekara sau ɗaya take zuwa ƙasar gwara ke ma kina zuwa inda take amma ni saidai a waya “
Gaɓa ɗaya jikin Ibtihal yayi sanyi ganowar jiniour hawaye ne ya ke itama hawayen takeji amma ta daure don ta kwantar masa da hankali ta ce”Karna ƙarajin kalar maganar nan daga bakinka jiniour jarabawa ce kowa da kalar tasa haka Allah ya zaɓa mana kuma dole mu bi na kiraka domin na ji muryarka naji sanyi a raina Muyi hira shine zaka tayarmun da hankali”
Da sauri ya ce”Kiyi hakuri bazan Sake ba”
Kafin su sake su hau hira sai wajen 11pm suka rabu cike da ƙaunar ƴan uwantaka mafi shaƙuwa.
Washegari kasancewar bazataje office ba tunda ba wani abu take ba sai 10:Am ta fito cikin doguwar riga marar nauyi ta zaman gida da tayi masifar mata kyau,
Breakfast ta je ta yi kafin ta wuce ɗakin hajiya samu tayi ta na walaha saida ta gama kafin ta gaisheta ta amsa da kulawa tare da cewa”meyasa tunda kika dawo bakije sashen Abban ku ba”?
Ta ce “haka dai baku da aiki sai gantali a jirgi daga kai har uban naka”
Ya na taɓe baki ya ce”Ita kuma waccen fa yaushe ta dawo”
Ta na harararsa ta ce “ka shiga ka tambayeta munafuki saikace bai san da zuwan nata ba ko ba saboda ita ka shigo ba”
Ba tare da ya bata amsa ba ya miƙe tare da nufar ɗakin na ta “
Hajiya ta taɓa hannu ta ce “Eyye da gaske kuma shigar zakayi zo ka wuce don ubanka karka sake ka shigar mata ɗaki bana son taɓara ƙaton baligi dakai ka faɗa ɗakin yarinya”
Ko waiwayowa baiyi ba bare ta sa ran amsa.
Ibtihal na shiga ta ja dogon tsaki bacci ma takeji gwara ta kwanta ta huta da wuri hakan ya sanyata cire kayan jikinta tare da ɗaura Towel ta na niyyar juyawa ta nufi Bathroom ta ji an Banko ƙofar,
a matuƙar firgice ta waiga ganin mai shigowar ne ya sanya gabanta tsananta faɗuwa ran ta na tsananin ɓaci ta juya da sauri zata wuce toilet don gaba ɗaya ta duburce ta ji an kamo hannunta cikin sauri ta waigo sukayi ido huɗu dashi ta rumtse ido da ƙarfi ta na jin tamkar ta ɗauke sa da mari ta ce ……….✍🏽
https://chat.whatsapp.com/JYPWPtF78zlIr2kJcbp6ms?mode=gi_t
_*Miss Hajo ce*_🤙🏿
🪅*IBTIHAL*🪅
~MALLAKAR~
*HAJARA L SADEQ*
(miss Hajo)
MARUBUCIYAR👇🏼
Auren wata tara
Ni da yaya arman
Matar uncle
Najmat abiy
Komai mukaddari ne
Khadijatul Sabren
Ribar so
Mata ta ce
*And now*
*IBTIHAL*
*DEDICATED TO MY HUSBAND*
🅿️…………………………..*03*
Ta ce “Ba ka da hankali ne yaya Yusuf za ka shigo mun ɗaki ba neman izini ka sakemun hannu kar nayi maka abunda duk bazamuji daɗi ba”
Ba tare da ya sakar mata hannu ba ya ce
“meye zakimun duka na zakiyi ko zagi na watau da sabuwar rashin kunya kika dawo ko meye a ciki don na shigo ɗakin ki ba izini kin manta matsayina a wajenki yaya kuma miji nan gaba kaɗan gaba ɗaya ma abunda kike ɓoyewar bakya son na gani zai zama mallaki na “
Haushi ,Takaici gami da kunya ne suka lulluɓeta wani ɓacin rai takejin na taso mata ba tare da zato ba ta ji ya saki hannunta ya na taɓe baki ya ce idan kin gama wankan ki sameni a falo idan ba haka ba Allah na sake shigowa bazakiji da daɗi ba”
Ya na gama faɗar haka ya fice tare da zare makullin ɗakin ta bi sa da kallo saida ta ga ficewarsa kafin ta sauke nauyayyar ajiyar zuciya ta na jan dogon tsaki tare da nufar Toilet ba ta wani ɓata lokaci sosai ba wajen wankan ta fito shiri tayi cikin kayan bacci silver masu masifar kyau riga da wando yalwaltaccen gashin kanta da ke ta sheƙi da ɗaukar ido ta tace da mataci wanda ni kaina tsawon gashin da sulɓin saida ya masifar burgeni turaruka masu sanyin ƙamshi ta fesa tare da gabatar da sallah don har wankan tsarki ta yi kasancewar perioud ɗinta ya ɗauke.
Ta na shirin kwanciya ta tuna Wancen mutumin ya cire key ya tafi da shi kuma ba kunya ta ishe sa ba zai iya dawowa tunda komai yayi mata ba dukansa ko zaginsa zatayi ba a ranta takejin tsanantar jin haushinsa,
Hijab blue black mai girma ta ɗora saman kayan baccin tare da fita ta na harhaɗe
Fuska,
Tunda ta fito idanunsa a kanta baisan sanda ya furta kalmar “Wow “ba “ ita komai ta saka sai ya mata kyau ne?”
ya tambaya kansa ya shagala da kallonta wanda har baisan ta zauna ɗaya daga cikin kujerun nesa da shi ba saida zazzaƙar muryarta ta doshi dodon kunnansa ya dawo cikin hayyacinsa ya na sauke ajiyar zuciya tare da amsa gaisuwar da tayi masa ya ɗora da cewa”ya aka gama karatun dukda baki faɗa mana dawowar ba bare mu shirya miki partyn graduation”
Hankalinta akan t v ba tare da ta kallesa ba ta ce”Alhmdulillah”ba tare da ta basa waccen amsar ba
Tashi ya yi daga kujerar da ya ke ya na komawa wacce take zaune 2sitter da sauri ta matsa ganin yanda Yake shirin shige mata harga Allah shiyasa bata so ba ganin ba hajiya a ɗakin don ta riga ta shige ciki ana isha’i dama ta ke kwantawa abinta,
Ƙara matsawa tayi murya ba wasa ta ce”meye haka yaya Yusuf”
Ya ce “Soyayya ce”
“Amma dai kasan babu kyau abunda kakeyi”
Ya na wani lumshe ido ya ce “meye marar kyawun “
Rasa da me zata amsa kawai tayi sai tsaki da ta ja a cikin ranta”
“Ya maganar Auren mu “
Ta tsinta muryarsa,
Ba tare da ta kallesa ba har lokacin idonta na kan tv dukda tana jin kusancin na su ya yi yawa ta ce”Daman munyi alƙawarin aure ne da kai?
“Hmmmm har yanzu ba ki janye kalamanki ba kenan amma kinsan a gobe na ga damar a ɗaura mana aure sai an ɗaura bana son ne na tilastaki shiyasa ko a baya na ƙyale har kika tafi ƙarin karatu”
Banza tayi ta ƙyalesa ta na jinjina Gadara da nuna iko na Yaya yusuf na daga dalilin da yasa kwata-kwata daman chan ba sa jituwa”
“Hmmm na kula kin dawo da sabon wulaƙanci karatun nan da kika dawo ko don kina ganin Kina Da PHD ina da Masters ko yanzu na ga daman zama DR ma zan zama don kar ki ga kamar kin fini ajin karatu ki rainani gaba nake dake a komai tunda Allah ma da kansa ya bamu wannan girman a kanku ko primary gareni ki sani gaba nake da ke don Haka ki aje girman kai mu fuskanci juna da bakya nan idan na daure yanzu bazan iya daurewa ba komai zai iya faruwa don haka ki bani hankalinki mu fuskanci juna”
Ba tare da ta basa amsar waccen tambayar ba ta miƙe tare da cewa” makullin ƙofar ta fa”
“Hmmm haka ma kawai zakice”
Ta ce “eh”
Ya na zare ɗaya daga cikin makullan ƙofar ya ce “Ga shi”
Ta na mamakin me zaiyi da makulli ta kallesa ta ce “ka mayar mun makulli na me zakayi dashi kuma “?
Ba tare da ya ba ta amsa ba ya miƙe tare da damƙa mata makullin a hannu ya na damƙar hannun kamar gaisuwa ya ce “Have a nice dream my beautiful wife”
tare da sumbatar hannun ya fice ta bishi da kallo sakaka tamkar sakarai kafin ta kalli hannunta da ya sumbata ta na jin takaici wasu hawayen takaici ta ji ya zubo mata ta wuce bedroom ta na hawaye zuciyarta chunkushe duk ba daɗi har ga Allah ba ta ƙaunar takurar nan da yaya faruq ke mata ita gaskiya ma sai ta bar gidan ma indai haka zaici gaba da mata”
“to ki bar gidan ki je ina kin manta mahaifinki ya muku iyaka da shi ko a waya ballantana gidansa da yayi muku korar kare”
“Innalillahi wa inna ilaihiraju’un wata Kewar Mahaifinta take ji har ƙasar zuciyarta dukda abunda yayi musu amma batajin tsanarsa ko kaɗan a cikin ranta”
Nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke ta na duba lokaci ta ga 10:30 tasan chan yanzu kusan 12 ma ta wuce kuma yanzu ta na tare da mijinta bai dace ta kirata a daidai wannan lokacin ba “Jiniour nasan yanzu baiyi bacci ba”
Ta faɗa ta na lalubo number sa saida ta kusan katsewa kafin ya ɗauka cikin muryar wanda ya fara bacci ya ce “Waye”
Ta ce “Sabuwar budurwarka da muka haɗu rannan”
Ta na jin sautin dariyarsa ya ce”Haba Aunty Ibtihal ko a mafarki akace na kasa gane muryarki ai zakice ba Jiniour ɗinki ba ne”
Ta ce “hummm ɗaɗin baki”
Ya ce “gaskiyace aunty na yi ta kiranki nayi miki sannu da zuwa ba ta shiga shine ko ki faɗa mun zaki dawo ƙasar da ko ƙaryar rashin lfy ne sainayi an barni na zo tarbarki”
Ta ce “nasan Exams kake shiyasa Bana son ka samu matsala a karatunka na so ma Zuwa Sch ɗin naku to da naga 10days ya rage ka dawo shiyasa na hakura don kasan nayi missing naka sosai bro”
Cike da zallar ƙauna ya ce”nima nayi matuƙar missing ɗinki aunty har bana son ayi hutu saboda idan nazo nasan bazan iske ki ba aunty ba ke ba momy ba Daddy dukda Shi daddy ba ya ƙaunarmu yanzu amma ai ita momy ta na ƙaunarmu amma itama ta rabu da mu ta zaɓi mijinta a kanmu a shekara sau ɗaya take zuwa ƙasar gwara ke ma kina zuwa inda take amma ni saidai a waya “
Gaɓa ɗaya jikin Ibtihal yayi sanyi ganowar jiniour hawaye ne ya ke itama hawayen takeji amma ta daure don ta kwantar masa da hankali ta ce”Karna ƙarajin kalar maganar nan daga bakinka jiniour jarabawa ce kowa da kalar tasa haka Allah ya zaɓa mana kuma dole mu bi na kiraka domin na ji muryarka naji sanyi a raina Muyi hira shine zaka tayarmun da hankali”
Da sauri ya ce”Kiyi hakuri bazan Sake ba”
Kafin su sake su hau hira sai wajen 11pm suka rabu cike da ƙaunar ƴan uwantaka mafi shaƙuwa.
Washegari kasancewar bazataje office ba tunda ba wani abu take ba sai 10:Am ta fito cikin doguwar riga marar nauyi ta zaman gida da tayi masifar mata kyau,
Breakfast ta je ta yi kafin ta wuce ɗakin hajiya samu tayi ta na walaha saida ta gama kafin ta gaisheta ta amsa da kulawa tare da cewa”meyasa tunda kika dawo bakije sashen Abban ku ba”?