Sashe 18
Ibtihal Hausa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cike da jin haushi Sajida ta ce “meyasa ke wai kike da zurfin ciki Sis wlh bakya son Yusuf me ya sa zaki amince a aura miki shi alhalin zaki chutu ki fito ki faɗa bakya sonsa a wuce wajen tunda ba Auren dole za ayi miki mi daman chan bana son Aurenki da shi wannan zafin zuciyar tasa da masifa ga faɗin baƙaƙen maganganu”
Ibtihal na miƙewa zaune cike da Ɓacin rai ta ce “babu ruwanku rayuwata ce ba taku ba Zan Aure sa Koda hakan shi zai zama silar mutuwa ta kuma wlh Duk wanda ya faɗawa Iyayenmu maganar nan bazan taɓa Yafe masa ba”
Safa ta ce “me yayi zafi Allah huci zuciyarki “
Ta ce “Amen “
Ta na komawa ta kwanta”
sajida ta ja tsaki ta fice cike da jin haushi wannan tsinannen zurfin cikin na Ibtihal da babu abunda ya ke ƙwarar rayuwarta ko a baya kamar shi,
Washegarin ranar da Sassafe aka sallame su da Asibiti bayan magunguna da shawarwari da Dr ya bayar,
Sakamakon allurorin baccin da aka mata yasa yinin ranar kusan yini ta yi a kwace,
Dukkaninsu Zaune Suke a Palour suna Hira Tundaga Kan Abba,Aunty Aisha,Momyn Ibtihal,Aunty salma, sai hira suke gwanin sha’awa da burgewa kallo ɗaya zaka musu kasan akwai shaƙuwa mai ƙarfi da soyayya a tsakaninsu,
Aunty salma ta so kwana a nan amma Hajja ta Tisata ta bi mijinta da ya zo ɗaukarta daman ya je duba Ibtihal Asibiti sau biyu daman Safa ta Ƙi binsu saboda Sajida a nan suka gama tattaunawa akan Batun Auren Ibtihal Da Yusuf Tare da na Sajida Da Marwan da dama a sanye ya ke wata Ukku da sati biyu ya rage wanda yayi daidai da lokacin ta gama Masters ɗinta Sun tsaida magana akan za a haɗe bikin tare da na Ibtihal,Bayan ya je sun gana da mahaifinta za su tsaida Ranar a chan”
Momy lokaci guda fuskarta ta sauya ta ce “ba na buƙatar sako Mahaifinta a batun nan Yaya Don Allah “
Ya ce “a a Nafisa baza’ayi haka ba shi ya ke da haƙƙi akan ƴarsa dole zamu basa Haƙƙinsa”
Aunty Aisha ta ce “haba Yaya Bashir wani kuma haƙƙi yaran da ya wulakanta ya musu Allah ya isa suka Ƙara taka gidansa ko kiransa a waya ko nemansa ma ya ce ba ya buƙatarsu a cikin rayuwarsa har abada su nemu sabon uba shi ya yafe su shine har kake maganar tunkaransa da batun yaran saikace bamu da zuciya a ƙirjinmu ai gaskiyar Nafisa Kai ma Uba ne Ka yanke duk wani hukunci akan Ibtihal amma ba ma buƙatar Adam a batun nan”
Abba ya ce “ku mata ne mu kuma maza ne akwai banbancin tunani tsakaninmu tunda nace hakan kawai ku ƙyaleni”
Hajja ta ce “Hakane sannan Ni har yanzu ban yarda ba Ɗana Adam ba a hayyacinsa ya ke ba kuma har yau har gobe bazan daina masa Addu’a ba Allah kuɓutar dashi”
Abba ya ce “Amen Hajiya”
Ta ce “idan ka je goben ka ce ina gaishe sa “ya ce “Insha Allah Hajiya”
Aunty Aisha da mom ba su ƙaracewa komai ba amma tsananin haushin hakan suke ji,
Washegari misalin takwas na safe Ibtihal ta farka bayan ta yi wanka ta shirya cikin kaya mararsa nauyi Safa da ke shirin tafiya school ta kalleta ta ce”don Allah kafin ki wuce kisa Saratu(mai aikinsu)
Ta haɗomin Tea Ba madara da milo zallarsa kawai banda bread”
Safa na Gama roalling gyale ta ce “toh amma ai da abu me nauyi kika ci zafikijin ƙwarin jikinki amma fa tun a asibiti daga Fruits sai Tea kike ta sha kinga yanda kika rame”
Ta ce “bana son cin abincin ne”
Ta ce “haka dai zaki daure”
Ta yi shiru batace komai ba”
Safa ta buga ƙafar Sajida da ke bacci ta na daga kwance cikin gigin bacci ta ce”meye”safa ta ce “ba fa kiyi salla ba Dukda gaba Ɗaya muka makara amma kiduba 7:30 fa”
Ta na juyawa tare da komawa bacci ta ce “banayi”
Jin haka ya safa Ƙyaleta ta na ficewa maimakon maid ta haɗo wa Ibtihal da kanta ta haɗa mata kafin ta wuce school a motar Ibtihal ɗin domin ta ta ta na gida,
A parking space suka haɗu da Lena kamar yanda suka saba haɗuwa kullum domin duk inda zasu a schook ɗin su biyu za ka gansu tare ba sa Mu’amular abota da kowa sai su biyu sai few mutane da suke gaisawa haka 9:30 suka fito lectures kai tsaye motocinnsu suka nufa suna nufar wani haɗaɗɗen restaurant bayan Sunyi Order abunda zasuci saboda dukkaninsu Basu karya ba suna Tsaka da karyawa Lena ta yi murmushi ta ce “Besty Alƙawari na”Safa na waro ido ta ce”Na meye”ta ce “kinga besty banson jan rai ki bani Labari kawai muna gama breakfast ɗinnan”
Ta ce “Ai yau ban bada labarin nan ba inaga zaman Abuja sai ya gagareni “
Ta ce “ba ma Abuja ba duka Nigeria”
minti Ƙalilan suka gama Kafin Lena ta ce “Oya Ke nake saurara”
Safa na goge bakinta da Tissue ta ce “Asalin kakanninmu wanda suka Haifi Iyayenmu Haifaffun……….✍🏽
*ZAMU KAMMALA FREE PAGES NA WANNAN LITTAFIN A PAGE 15 KUNA DA DAMAR FARA BIYAN KUƊINSA TUN YANZU 500 TA WANNAN ASUSUN BANKIN 7026166536 OPAY HAJARA ABUBAKAR LAWAL TARE DA SHAIDAR BIYA TA 07026166536*
_*Miss Hajo ce*_🤙🏿
🪅*IBTIHAL*🪅
~MALLAKAR~
*HAJARA L SADEQ*
(miss Hajo)
MARUBUCIYAR👇🏼
Auren wata tara
Ni da yaya arman
Matar uncle
Najmat abiy
Komai mukaddari ne
Khadijatul Sabren
Ribar so
Mata ta ce
*And now*
*IBTIHAL*
*DEDICATED TO MY HUSBAND*
*Ƙawa ta zama Ƴar uwa💃🏼🎶Roky magaji tawa ƴar amanata wlh jinta nake Ƙasar raina🥹Fatan Alkhairi gareki da dukkan ahalinki Alkhairin Allah yaci gaba da Dabaibaye rayuwarki Allah ya baki miji nagari wanda zai kula mana da ke ya so ki ya ƙaunaceki Allah ya nuna mana ranar Auranki Ranar Zaria ko ba Taya Wollah*
🅿️…………………………..*13*
Asalin kakanninmu wanda suka haifi iyayenmu haifaffun garin Bama Local goverment ne da ke jahar Borno State wanda asalin su Shuwa’arab ɗin Sudan ne,
Kakarmu mai suna Zainab Tare da Kakanmu Alhaji Dikko ƴan uwan juna ne auren zumunci aka musu,
Kakarmu su biyu a gurin iyayensu daga ita sai Ƙanwarta Aisha ,
sun ta so cikin soyayya Da Ƙaunar Juna Wanda kusan tattare akayi aurensu domin shekarar Zainab guda da Aure Akayi auren Aisha lokacin Zainab na da tsohon cikinta na fari wanda Aure ya raba su ita Aisha ya kaita Katsina saɓanin Zainab da aka aje ta a nan Bama saboda lokacin kakanmu Soja ne yana tafiya ya yi watanni ya dawo kafin daga baya ya koma duk inda zaije tare da Ita ya ke tafiya,
Ta haifi Ɗanta na farko Ya ci suna bashir bayan shekara ukku Da haihuwar bashir itama aisha aka kawota gida haihuwa wanda Zainab ta matuƙar kula da ita Har Allah ya sauketa ta haifi ɗanta namiji wanda ta matuƙar jigatuwa bayan haihuwarsa da awa guda Allah ya amsa Ranta bayan ta damƙa amanar jaririnta a hannun Zainab Shine wasiyarta na ƙarshe zainab ta matuƙar jin mutuwar Aisha,
Wanda lokacin ta so shayar da shi amma hakan bai yiwu ba sakamakon tsohon ciki da take ɗauke dashi dole sai haƙura tayi wata ƴar uwarsu ta shayar dashi amma anan gidanta saboda daman zawarace ,
sosai zainab ke Ƙaunar Adam Tamkar ɗan da ta haifa a cikinta yanda take bamu labari bata taɓajin banbanci tsakaninsa da ƴaƴan da ta haifa ba Lokacin Allah ya sauketa lafiya ta haifi Aisha watau Momyn Sajida daga nan kuma sai bayan shekara huɗu ta sake haihuwar wata ƴa macen ta ci suna Nafisa Kafin ta haifi Salma Momy na kenan Bayan ita ta haifi ɗanta namiji Allah yayi masa rasuwa,bayan shekaru biyu da haihuwarsu,
Ƴaƴanta sun taso cikin soyayya da ƙaunar juna gami da tarbiya haɗe da ilimin boko da na zamani domin Alhaji dikko mutum ne mai Tsananin Aƙida da Ƙaunar boko hakan ya sa duk ƴaƴansa suka taso cikin boko ba kowa yasan Da Adam ba uwa ɗaya uba ɗaya suke ba a cikin ƴaƴansa sai daga baya da mahaifinsa ya ke zuwa ganinsa kafin ya na da shekaru goma Allah yayiwa mahaifinsa rasuwa a hanyarsa ta komaqa chan katsina da ya zo ganin Ɗansa daman shi kaɗai ya haifa a nan katsina akayi suturarsa,
A lokacin mutum ne mai arziƙin Gaske Ɗan kasuwa ne daman a harkar kasuwancinsa ya kaisa har Bama ya ga aisha ya aura gona ɗari Ya bari banda filaye da shanaye da gidaje tare da zunzurutun kuɗi masu yawa a lokacin ,
Wanda dukkan wannan dukiya ɗansa Adam kaɗai ya gada domin bashi da uwa bashi da uba wannan haushin ya sa Tun lokacin danginsa suka Tsani Adam Da uwar riƙonsa domin sun so su handame dukiyar Adam da mahaifinsa ya bar masa ,
Alhaji dikko ya tsaya tsayin daka wajen ganin Ya ƙwatowa adam haƙƙinsa sanin ba Allah a ransu ya sanya duka dukiyar Adam da ke garin ya sayar ya haɗa kuɗaɗen waje Guda ya saya Masa Manyan gonaki da filaye dukansu a maiduguri wanda hakan ya ƙara musu ƙiyayyarsu a ransu hakan ya sa tunda aka tafi da Adam ba su ƙara waiwayarsa ba Matsayinsu na Dangin Mahaifinsa,
To fa lokacin ne Adam da su Momynmu suka fahimci Alaƙarsu da adam,
Ibtihal na miƙewa zaune cike da Ɓacin rai ta ce “babu ruwanku rayuwata ce ba taku ba Zan Aure sa Koda hakan shi zai zama silar mutuwa ta kuma wlh Duk wanda ya faɗawa Iyayenmu maganar nan bazan taɓa Yafe masa ba”
Safa ta ce “me yayi zafi Allah huci zuciyarki “
Ta ce “Amen “
Ta na komawa ta kwanta”
sajida ta ja tsaki ta fice cike da jin haushi wannan tsinannen zurfin cikin na Ibtihal da babu abunda ya ke ƙwarar rayuwarta ko a baya kamar shi,
Washegarin ranar da Sassafe aka sallame su da Asibiti bayan magunguna da shawarwari da Dr ya bayar,
Sakamakon allurorin baccin da aka mata yasa yinin ranar kusan yini ta yi a kwace,
Dukkaninsu Zaune Suke a Palour suna Hira Tundaga Kan Abba,Aunty Aisha,Momyn Ibtihal,Aunty salma, sai hira suke gwanin sha’awa da burgewa kallo ɗaya zaka musu kasan akwai shaƙuwa mai ƙarfi da soyayya a tsakaninsu,
Aunty salma ta so kwana a nan amma Hajja ta Tisata ta bi mijinta da ya zo ɗaukarta daman ya je duba Ibtihal Asibiti sau biyu daman Safa ta Ƙi binsu saboda Sajida a nan suka gama tattaunawa akan Batun Auren Ibtihal Da Yusuf Tare da na Sajida Da Marwan da dama a sanye ya ke wata Ukku da sati biyu ya rage wanda yayi daidai da lokacin ta gama Masters ɗinta Sun tsaida magana akan za a haɗe bikin tare da na Ibtihal,Bayan ya je sun gana da mahaifinta za su tsaida Ranar a chan”
Momy lokaci guda fuskarta ta sauya ta ce “ba na buƙatar sako Mahaifinta a batun nan Yaya Don Allah “
Ya ce “a a Nafisa baza’ayi haka ba shi ya ke da haƙƙi akan ƴarsa dole zamu basa Haƙƙinsa”
Aunty Aisha ta ce “haba Yaya Bashir wani kuma haƙƙi yaran da ya wulakanta ya musu Allah ya isa suka Ƙara taka gidansa ko kiransa a waya ko nemansa ma ya ce ba ya buƙatarsu a cikin rayuwarsa har abada su nemu sabon uba shi ya yafe su shine har kake maganar tunkaransa da batun yaran saikace bamu da zuciya a ƙirjinmu ai gaskiyar Nafisa Kai ma Uba ne Ka yanke duk wani hukunci akan Ibtihal amma ba ma buƙatar Adam a batun nan”
Abba ya ce “ku mata ne mu kuma maza ne akwai banbancin tunani tsakaninmu tunda nace hakan kawai ku ƙyaleni”
Hajja ta ce “Hakane sannan Ni har yanzu ban yarda ba Ɗana Adam ba a hayyacinsa ya ke ba kuma har yau har gobe bazan daina masa Addu’a ba Allah kuɓutar dashi”
Abba ya ce “Amen Hajiya”
Ta ce “idan ka je goben ka ce ina gaishe sa “ya ce “Insha Allah Hajiya”
Aunty Aisha da mom ba su ƙaracewa komai ba amma tsananin haushin hakan suke ji,
Washegari misalin takwas na safe Ibtihal ta farka bayan ta yi wanka ta shirya cikin kaya mararsa nauyi Safa da ke shirin tafiya school ta kalleta ta ce”don Allah kafin ki wuce kisa Saratu(mai aikinsu)
Ta haɗomin Tea Ba madara da milo zallarsa kawai banda bread”
Safa na Gama roalling gyale ta ce “toh amma ai da abu me nauyi kika ci zafikijin ƙwarin jikinki amma fa tun a asibiti daga Fruits sai Tea kike ta sha kinga yanda kika rame”
Ta ce “bana son cin abincin ne”
Ta ce “haka dai zaki daure”
Ta yi shiru batace komai ba”
Safa ta buga ƙafar Sajida da ke bacci ta na daga kwance cikin gigin bacci ta ce”meye”safa ta ce “ba fa kiyi salla ba Dukda gaba Ɗaya muka makara amma kiduba 7:30 fa”
Ta na juyawa tare da komawa bacci ta ce “banayi”
Jin haka ya safa Ƙyaleta ta na ficewa maimakon maid ta haɗo wa Ibtihal da kanta ta haɗa mata kafin ta wuce school a motar Ibtihal ɗin domin ta ta ta na gida,
A parking space suka haɗu da Lena kamar yanda suka saba haɗuwa kullum domin duk inda zasu a schook ɗin su biyu za ka gansu tare ba sa Mu’amular abota da kowa sai su biyu sai few mutane da suke gaisawa haka 9:30 suka fito lectures kai tsaye motocinnsu suka nufa suna nufar wani haɗaɗɗen restaurant bayan Sunyi Order abunda zasuci saboda dukkaninsu Basu karya ba suna Tsaka da karyawa Lena ta yi murmushi ta ce “Besty Alƙawari na”Safa na waro ido ta ce”Na meye”ta ce “kinga besty banson jan rai ki bani Labari kawai muna gama breakfast ɗinnan”
Ta ce “Ai yau ban bada labarin nan ba inaga zaman Abuja sai ya gagareni “
Ta ce “ba ma Abuja ba duka Nigeria”
minti Ƙalilan suka gama Kafin Lena ta ce “Oya Ke nake saurara”
Safa na goge bakinta da Tissue ta ce “Asalin kakanninmu wanda suka Haifi Iyayenmu Haifaffun……….✍🏽
*ZAMU KAMMALA FREE PAGES NA WANNAN LITTAFIN A PAGE 15 KUNA DA DAMAR FARA BIYAN KUƊINSA TUN YANZU 500 TA WANNAN ASUSUN BANKIN 7026166536 OPAY HAJARA ABUBAKAR LAWAL TARE DA SHAIDAR BIYA TA 07026166536*
_*Miss Hajo ce*_🤙🏿
🪅*IBTIHAL*🪅
~MALLAKAR~
*HAJARA L SADEQ*
(miss Hajo)
MARUBUCIYAR👇🏼
Auren wata tara
Ni da yaya arman
Matar uncle
Najmat abiy
Komai mukaddari ne
Khadijatul Sabren
Ribar so
Mata ta ce
*And now*
*IBTIHAL*
*DEDICATED TO MY HUSBAND*
*Ƙawa ta zama Ƴar uwa💃🏼🎶Roky magaji tawa ƴar amanata wlh jinta nake Ƙasar raina🥹Fatan Alkhairi gareki da dukkan ahalinki Alkhairin Allah yaci gaba da Dabaibaye rayuwarki Allah ya baki miji nagari wanda zai kula mana da ke ya so ki ya ƙaunaceki Allah ya nuna mana ranar Auranki Ranar Zaria ko ba Taya Wollah*
🅿️…………………………..*13*
Asalin kakanninmu wanda suka haifi iyayenmu haifaffun garin Bama Local goverment ne da ke jahar Borno State wanda asalin su Shuwa’arab ɗin Sudan ne,
Kakarmu mai suna Zainab Tare da Kakanmu Alhaji Dikko ƴan uwan juna ne auren zumunci aka musu,
Kakarmu su biyu a gurin iyayensu daga ita sai Ƙanwarta Aisha ,
sun ta so cikin soyayya Da Ƙaunar Juna Wanda kusan tattare akayi aurensu domin shekarar Zainab guda da Aure Akayi auren Aisha lokacin Zainab na da tsohon cikinta na fari wanda Aure ya raba su ita Aisha ya kaita Katsina saɓanin Zainab da aka aje ta a nan Bama saboda lokacin kakanmu Soja ne yana tafiya ya yi watanni ya dawo kafin daga baya ya koma duk inda zaije tare da Ita ya ke tafiya,
Ta haifi Ɗanta na farko Ya ci suna bashir bayan shekara ukku Da haihuwar bashir itama aisha aka kawota gida haihuwa wanda Zainab ta matuƙar kula da ita Har Allah ya sauketa ta haifi ɗanta namiji wanda ta matuƙar jigatuwa bayan haihuwarsa da awa guda Allah ya amsa Ranta bayan ta damƙa amanar jaririnta a hannun Zainab Shine wasiyarta na ƙarshe zainab ta matuƙar jin mutuwar Aisha,
Wanda lokacin ta so shayar da shi amma hakan bai yiwu ba sakamakon tsohon ciki da take ɗauke dashi dole sai haƙura tayi wata ƴar uwarsu ta shayar dashi amma anan gidanta saboda daman zawarace ,
sosai zainab ke Ƙaunar Adam Tamkar ɗan da ta haifa a cikinta yanda take bamu labari bata taɓajin banbanci tsakaninsa da ƴaƴan da ta haifa ba Lokacin Allah ya sauketa lafiya ta haifi Aisha watau Momyn Sajida daga nan kuma sai bayan shekara huɗu ta sake haihuwar wata ƴa macen ta ci suna Nafisa Kafin ta haifi Salma Momy na kenan Bayan ita ta haifi ɗanta namiji Allah yayi masa rasuwa,bayan shekaru biyu da haihuwarsu,
Ƴaƴanta sun taso cikin soyayya da ƙaunar juna gami da tarbiya haɗe da ilimin boko da na zamani domin Alhaji dikko mutum ne mai Tsananin Aƙida da Ƙaunar boko hakan ya sa duk ƴaƴansa suka taso cikin boko ba kowa yasan Da Adam ba uwa ɗaya uba ɗaya suke ba a cikin ƴaƴansa sai daga baya da mahaifinsa ya ke zuwa ganinsa kafin ya na da shekaru goma Allah yayiwa mahaifinsa rasuwa a hanyarsa ta komaqa chan katsina da ya zo ganin Ɗansa daman shi kaɗai ya haifa a nan katsina akayi suturarsa,
A lokacin mutum ne mai arziƙin Gaske Ɗan kasuwa ne daman a harkar kasuwancinsa ya kaisa har Bama ya ga aisha ya aura gona ɗari Ya bari banda filaye da shanaye da gidaje tare da zunzurutun kuɗi masu yawa a lokacin ,
Wanda dukkan wannan dukiya ɗansa Adam kaɗai ya gada domin bashi da uwa bashi da uba wannan haushin ya sa Tun lokacin danginsa suka Tsani Adam Da uwar riƙonsa domin sun so su handame dukiyar Adam da mahaifinsa ya bar masa ,
Alhaji dikko ya tsaya tsayin daka wajen ganin Ya ƙwatowa adam haƙƙinsa sanin ba Allah a ransu ya sanya duka dukiyar Adam da ke garin ya sayar ya haɗa kuɗaɗen waje Guda ya saya Masa Manyan gonaki da filaye dukansu a maiduguri wanda hakan ya ƙara musu ƙiyayyarsu a ransu hakan ya sa tunda aka tafi da Adam ba su ƙara waiwayarsa ba Matsayinsu na Dangin Mahaifinsa,
To fa lokacin ne Adam da su Momynmu suka fahimci Alaƙarsu da adam,