Sashe 5
Faɗime Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Inna Fatuh dake tafe har sauran kad'an ta kife a k'asa, ta fito k'ofar gidan tare da su Inna Lami da Malam dake biye dasu, da duk mutanan gidan.
"Wai miye ne da naji anata kiran sunan Jikata ne?"
D'an juma mai tsire ne yayi saurin cewa.
"Ai na rantse da Allah yau sai an biyani kud'in tsire na, Jikarki Fad'ime taje ita da K'awayenta suka watsa min k'asa a cikin tsire na, dan haka tsire na, na kusan dubu talatin ne, kuma wallahi ko za'a sake yak'in duniya na biyu sai an biya ni kud'i na, ko mu had'u a Ofishin Y'an Sadda".
"Ai ba kai kad'an bama Malama D'an juma, ni Yaro na ta kama ta kantsama ma Mari har jinsa ya d'auke, dan haka wallahi ko za'ayi mi yau sai tazo ta maido masa da jinsa yadda yake wallahi, ina nan ina jiran Jikar taki".
Cewar wata mata dake rik'e da Yaron har yanzu baya jin abunda ake cewa sai kuka yake.
Inna Fatuh ta wani k'ank'ance ido tana kallonsu d'aya bayan d'aya ta ce.
"da'aAllah Malamai ku tsaya min na ce, nasan dai Jikata bata jan fad'a sai an tab'a ta, su yaran naku baku tabbaye su miye sukai mata bane?, Kai kuma D'an juma akwai abunda kayi mata kaima wallahi. Kuma bamai tab'a min Jika wallahi ehee".
Inna Fatuh ta k'are maganar tana turo kallabi gaban goshinta, dan ko hijab bata sa ba, wani gyale na yafo saman kafad'arta.
Zasu sake magana wata mata ta shayo kwana ita da d'iyarta rik'e a hannunta had'e da Y'an Sadda guda biyu biye da ita fuska murtuke.
"Mun shiga uku, ku kuma fa, daga Ina?".
Cewar Inna Lami tana rik'e k'ugunta.
"Zuwa mukai a kama Fad'ime ta kama Y'ata Binta ta haye ruwan cikinta ta kama bugunta kamar ta sami Jaka, yo ko ni dana haifeta ban tab'a mata irin wannan uban dukan ba, dan haka banga ubanda ya isa ya bigeta haka na kyale shi ba wallahi".
"Wayyo Allah na shige su ni Inna Fatuh, ace duk garin nan duk an tsani Jikata, kamar ita ce kad'ai yarinya a cikin garin nan. Shine ke baiwar Allah harda zuwa ki kwasu Y'an Sadda domin kawai su kama Jikata?, ai ko wallahi banga wadda ya isa ya kama Jikata ba ehee kiji da kyau".
"Haba haba haba Inna Fatuh, Fisbilillahi sai tare ma Fad'ime fad'a kike al'halin kinsan ita ce wacce keda laifi. Ki bari kawai ma ta dawo daga yawon ta zubar d'inta su kamata su wuce da ita can Ofishin Y'an Saddan, su lallasa mana ita ma ko ta d'anyi halkali ma"
Cewar Auta yana duban Inna Fatuh.
Wata dak'uwa Inna Fatuh ta makama Auta tana cewa.
"Ungo nan Auta, kaci gidanku na ce kaji, idan kaga an tafi da Fad'ime to sai dai a had'a da ni da Ubanka duka a tafi damu wallahi".
"A'afa wannan d'aya, sai dai keda Fad'imen za'a tafi da ku amma dai banda Malam wallahi"
Malam ne ya kalli Auta ya ce .
"Karka sake magana a nan wajan, wuce ka shige gida na ce".
Malam ya fad'a yana nuna Auta dake kallon Inna Fatuh fuska ba Rahma.
"Yo ka barsa mana tunda ai uwarsa ce take d'aure masa gindi yayi ma mutane rashin kunya ai".
Inna Lami ta katse Inna Fatuh tana d'aga mata hannu ta ce.
"Kinga Inna Fatuh tunda aka fara wannan kicimulin baki ji baki na ba, dan haka kar a sake saka ni a ciki a'ato".
"Ai kawai ki fito fili ki ce zaki zage ni Lami, dama ai kema ba k'aunar Fad'ime kikeyi ba wallahi, bakik'i ma Fad'ime zuwa yanzu ta mutu ba ai, to Fad'ime dai nan gani nan bari ajiyar Allah ce wallahi".
Lami zata sake magana ranta a b'ace Malam ya d'aga masu hannu zuciyarsa babu dad'i ya kalli dandazon jama'ar dake wajan ya ce.
"Kowa ya fad'i kud'in da tayi masa asara da wadda zasu je asibiti sukai Y'ay'ansu. Dan Allah kuyi hakuri kuma, Yaro ne ka haifesa baka haifi halinsa ba".
Jama'ar wajan tausayin Malam ne ya kamasu dan haka da kyar wasu suka hakura nan take yasa aka kamo Akuya har biyu aka saida, aka biya kowa kud'in da ya kamata, sai mutum d'aya ce bata karb'a ba, wacce Yaronta jinsa ya d'auke ita ce tsaya a wajan yanzu tana cewa.
"Babufa kud'in da zan amsa naku, iyakaci a fito min da Fad'ime ta bud'e ma Yaro na kunnansa, idan ba haka ba kuma nima wallahi wajan Y'an Saddan zan kai k'ara, domin ni kud'inku babu uwar da zasu min".
Inna Fatuh zatai magana ta hango Fad'ime dake tafe ita da zugar K'awayenta.
Ganin Ibrahim zai nufi wajanta Babban Yayansu ta d'aga masa tsawa tana cewa.
"Na rantse da Allah karka sake ta tab'a min Jika, karka sake na ce".
Duk maganar da take yi hakan baisa Ibrahim tsayawa ba, sai da ya kamo hannun Fad'ime dake zare ido waje y'an cikinta na k'ara, domin tasan an kawo k'ararta tun kan ta iso gida, tana jin tsoron Ibrahim shine kad'ai duk cikin familynsu take d'an shakka shima kad'an.
Sai da ya d'auketa da Mari har sau biyu, yana zare mata ido yana cewa.
"Dan Ubanki abunda aka ce kije kiyo kenan?, kin san iyayen mutanan da suka zo kawo k'ararki? Ke wai wacce irin y'ar banzar yarinya ce ne?, shegiya kamar shaid'aniya, ke kullum kece y'ar kawo k'ararki wajan mutane, dalla wuce min a nan karna karya miki k'afafu yanzu nan wallahi".
"Karyata mana, ai kawai ka idasa min ita na ce kaji Ibrahim?"
Cewar Inna Fatuh data warce Fad'ime daga hannunsa yanzu tana b'alla masa uwar harara.
Banza yayi da ita ya kalli sauran K'awayen yana zare masu ido ya ce.
"da'aAllah can kuma kubar wajan nan".
Aje nik'an sukai da sauri suka juya da gudu suka bar wajan.
Sake fisgo Fad'ime yayi a hannun Inna Fatuh ya matso da ita inda Matar nan take da Yaronta yana cewa.
"Kiyi Maza-maza ki bud'e ma Yaron nan kunne idan ba haka ba kuma na rantse miki na lahira sai fiki jin dad'i".
Matsowa Inna Fatuh tayi wajan tana cewa.
"Wai kai Ibrahim wane irin abu ne wannan kake haka, kana ma yarinya tsawa sai ka ce ba ubanku d'aya ba, ai ku duka ba k'aunarta kuke ba, shikenan kullum ace cikin hantarar kuke, to wallahi ranka zaiyi mummunan b'aci ne".
Nan d'in ma ba tanka mata yayi ba.
Sai k'ok'arin bugu da yake son kaima Fad'ime domin yaga yadda ta wani tsaya bata niyar yin abunda ya ce.
Yasa Inna Fatuh kallon Malam dake tsaye cike da jin haushinsa shima ta ce.
"Idan har ni ce na haifeka to kaba Yaronka umarnin cewa karya sake ya sake tab'a min Jika, idan ban isa dashi ba, ai kai na isa da Kai".
Ba dan Malam yaso ba ya dakatar da Ibrahim daga dukan da yake son kaima Fad'ime.
Malam ya matso a hankali cikin kwantar da murya ya ce.
"Fad'ime y'ar albarka ki bud'e ma yaron nan kunnansa kinji".
D'an sakin fuskarta tayi domin da tun farko da lallami aka bi da ita da tuni tayi abunda suke so. Dan a duniya Fad'ime ta tsani a d'aga mata murya.
A hankali ta juya wajan Inna Fatuh tana cewa.
"Suje gida Kunnan nasa zai bud'e".
Tana fad'ar haka ta shige cikin gidan.
"Kutumar uban can, ni Lami naga takaina, ace yarinya tayi laifi amma ko a jikinta, ko da yake d'aurin gindi ta samu ai, dole tayi abunda take so ai, ta taka wadda take so ".
Inna Lami ta fad'a cike da bak'in cikin Fad'ime, yau so tayi a tafi Police teshin d'in da ita ace ubanta sosai.
"Ohhh dai ba kuma yadda za'ayi da ita kuma ba".
Cewar Inna Fatuh.
Lami ta shige gida tana jin bak'in cikin dawowarsu wannan gidan, da ace suna can gidansu ai da sai yadda tayi da wannan aljanar yarinyar.
Kamin su wuce ga mamakin Matar nan uwar yaron nan sai ji tayi Yaronta na cewa yanzu yana jin komai cike da murna yake fad'ar haka.
Inna Fatuh ta kallesu tana cewa.
"To daga yau sai kiyi ma D'anki gargad'in cewa karya sake Jan Jikata, dan k'ila a gaba zai iya rasa idanuwansa ma".
Itama ta k'are maganar tana d'aukar nik'anta dasu Laure suka aje, ta shige cikin gidan.
Malam ne ya tsaya ya sake ba Matar hakuri sosai...........
*FAƊIME...💋🌸💕*
_(Dangin Jinnu)_
©By Nainarh KD & Zahrah Royal Star
*Dedicated to Salma Ahmad Isah (Candy)*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*A love & Laugh story that will capture your heart and soul.*
05
*BAYAN SATI ƊAYA*
"Wai miye ne da naji anata kiran sunan Jikata ne?"
D'an juma mai tsire ne yayi saurin cewa.
"Ai na rantse da Allah yau sai an biyani kud'in tsire na, Jikarki Fad'ime taje ita da K'awayenta suka watsa min k'asa a cikin tsire na, dan haka tsire na, na kusan dubu talatin ne, kuma wallahi ko za'a sake yak'in duniya na biyu sai an biya ni kud'i na, ko mu had'u a Ofishin Y'an Sadda".
"Ai ba kai kad'an bama Malama D'an juma, ni Yaro na ta kama ta kantsama ma Mari har jinsa ya d'auke, dan haka wallahi ko za'ayi mi yau sai tazo ta maido masa da jinsa yadda yake wallahi, ina nan ina jiran Jikar taki".
Cewar wata mata dake rik'e da Yaron har yanzu baya jin abunda ake cewa sai kuka yake.
Inna Fatuh ta wani k'ank'ance ido tana kallonsu d'aya bayan d'aya ta ce.
"da'aAllah Malamai ku tsaya min na ce, nasan dai Jikata bata jan fad'a sai an tab'a ta, su yaran naku baku tabbaye su miye sukai mata bane?, Kai kuma D'an juma akwai abunda kayi mata kaima wallahi. Kuma bamai tab'a min Jika wallahi ehee".
Inna Fatuh ta k'are maganar tana turo kallabi gaban goshinta, dan ko hijab bata sa ba, wani gyale na yafo saman kafad'arta.
Zasu sake magana wata mata ta shayo kwana ita da d'iyarta rik'e a hannunta had'e da Y'an Sadda guda biyu biye da ita fuska murtuke.
"Mun shiga uku, ku kuma fa, daga Ina?".
Cewar Inna Lami tana rik'e k'ugunta.
"Zuwa mukai a kama Fad'ime ta kama Y'ata Binta ta haye ruwan cikinta ta kama bugunta kamar ta sami Jaka, yo ko ni dana haifeta ban tab'a mata irin wannan uban dukan ba, dan haka banga ubanda ya isa ya bigeta haka na kyale shi ba wallahi".
"Wayyo Allah na shige su ni Inna Fatuh, ace duk garin nan duk an tsani Jikata, kamar ita ce kad'ai yarinya a cikin garin nan. Shine ke baiwar Allah harda zuwa ki kwasu Y'an Sadda domin kawai su kama Jikata?, ai ko wallahi banga wadda ya isa ya kama Jikata ba ehee kiji da kyau".
"Haba haba haba Inna Fatuh, Fisbilillahi sai tare ma Fad'ime fad'a kike al'halin kinsan ita ce wacce keda laifi. Ki bari kawai ma ta dawo daga yawon ta zubar d'inta su kamata su wuce da ita can Ofishin Y'an Saddan, su lallasa mana ita ma ko ta d'anyi halkali ma"
Cewar Auta yana duban Inna Fatuh.
Wata dak'uwa Inna Fatuh ta makama Auta tana cewa.
"Ungo nan Auta, kaci gidanku na ce kaji, idan kaga an tafi da Fad'ime to sai dai a had'a da ni da Ubanka duka a tafi damu wallahi".
"A'afa wannan d'aya, sai dai keda Fad'imen za'a tafi da ku amma dai banda Malam wallahi"
Malam ne ya kalli Auta ya ce .
"Karka sake magana a nan wajan, wuce ka shige gida na ce".
Malam ya fad'a yana nuna Auta dake kallon Inna Fatuh fuska ba Rahma.
"Yo ka barsa mana tunda ai uwarsa ce take d'aure masa gindi yayi ma mutane rashin kunya ai".
Inna Lami ta katse Inna Fatuh tana d'aga mata hannu ta ce.
"Kinga Inna Fatuh tunda aka fara wannan kicimulin baki ji baki na ba, dan haka kar a sake saka ni a ciki a'ato".
"Ai kawai ki fito fili ki ce zaki zage ni Lami, dama ai kema ba k'aunar Fad'ime kikeyi ba wallahi, bakik'i ma Fad'ime zuwa yanzu ta mutu ba ai, to Fad'ime dai nan gani nan bari ajiyar Allah ce wallahi".
Lami zata sake magana ranta a b'ace Malam ya d'aga masu hannu zuciyarsa babu dad'i ya kalli dandazon jama'ar dake wajan ya ce.
"Kowa ya fad'i kud'in da tayi masa asara da wadda zasu je asibiti sukai Y'ay'ansu. Dan Allah kuyi hakuri kuma, Yaro ne ka haifesa baka haifi halinsa ba".
Jama'ar wajan tausayin Malam ne ya kamasu dan haka da kyar wasu suka hakura nan take yasa aka kamo Akuya har biyu aka saida, aka biya kowa kud'in da ya kamata, sai mutum d'aya ce bata karb'a ba, wacce Yaronta jinsa ya d'auke ita ce tsaya a wajan yanzu tana cewa.
"Babufa kud'in da zan amsa naku, iyakaci a fito min da Fad'ime ta bud'e ma Yaro na kunnansa, idan ba haka ba kuma nima wallahi wajan Y'an Saddan zan kai k'ara, domin ni kud'inku babu uwar da zasu min".
Inna Fatuh zatai magana ta hango Fad'ime dake tafe ita da zugar K'awayenta.
Ganin Ibrahim zai nufi wajanta Babban Yayansu ta d'aga masa tsawa tana cewa.
"Na rantse da Allah karka sake ta tab'a min Jika, karka sake na ce".
Duk maganar da take yi hakan baisa Ibrahim tsayawa ba, sai da ya kamo hannun Fad'ime dake zare ido waje y'an cikinta na k'ara, domin tasan an kawo k'ararta tun kan ta iso gida, tana jin tsoron Ibrahim shine kad'ai duk cikin familynsu take d'an shakka shima kad'an.
Sai da ya d'auketa da Mari har sau biyu, yana zare mata ido yana cewa.
"Dan Ubanki abunda aka ce kije kiyo kenan?, kin san iyayen mutanan da suka zo kawo k'ararki? Ke wai wacce irin y'ar banzar yarinya ce ne?, shegiya kamar shaid'aniya, ke kullum kece y'ar kawo k'ararki wajan mutane, dalla wuce min a nan karna karya miki k'afafu yanzu nan wallahi".
"Karyata mana, ai kawai ka idasa min ita na ce kaji Ibrahim?"
Cewar Inna Fatuh data warce Fad'ime daga hannunsa yanzu tana b'alla masa uwar harara.
Banza yayi da ita ya kalli sauran K'awayen yana zare masu ido ya ce.
"da'aAllah can kuma kubar wajan nan".
Aje nik'an sukai da sauri suka juya da gudu suka bar wajan.
Sake fisgo Fad'ime yayi a hannun Inna Fatuh ya matso da ita inda Matar nan take da Yaronta yana cewa.
"Kiyi Maza-maza ki bud'e ma Yaron nan kunne idan ba haka ba kuma na rantse miki na lahira sai fiki jin dad'i".
Matsowa Inna Fatuh tayi wajan tana cewa.
"Wai kai Ibrahim wane irin abu ne wannan kake haka, kana ma yarinya tsawa sai ka ce ba ubanku d'aya ba, ai ku duka ba k'aunarta kuke ba, shikenan kullum ace cikin hantarar kuke, to wallahi ranka zaiyi mummunan b'aci ne".
Nan d'in ma ba tanka mata yayi ba.
Sai k'ok'arin bugu da yake son kaima Fad'ime domin yaga yadda ta wani tsaya bata niyar yin abunda ya ce.
Yasa Inna Fatuh kallon Malam dake tsaye cike da jin haushinsa shima ta ce.
"Idan har ni ce na haifeka to kaba Yaronka umarnin cewa karya sake ya sake tab'a min Jika, idan ban isa dashi ba, ai kai na isa da Kai".
Ba dan Malam yaso ba ya dakatar da Ibrahim daga dukan da yake son kaima Fad'ime.
Malam ya matso a hankali cikin kwantar da murya ya ce.
"Fad'ime y'ar albarka ki bud'e ma yaron nan kunnansa kinji".
D'an sakin fuskarta tayi domin da tun farko da lallami aka bi da ita da tuni tayi abunda suke so. Dan a duniya Fad'ime ta tsani a d'aga mata murya.
A hankali ta juya wajan Inna Fatuh tana cewa.
"Suje gida Kunnan nasa zai bud'e".
Tana fad'ar haka ta shige cikin gidan.
"Kutumar uban can, ni Lami naga takaina, ace yarinya tayi laifi amma ko a jikinta, ko da yake d'aurin gindi ta samu ai, dole tayi abunda take so ai, ta taka wadda take so ".
Inna Lami ta fad'a cike da bak'in cikin Fad'ime, yau so tayi a tafi Police teshin d'in da ita ace ubanta sosai.
"Ohhh dai ba kuma yadda za'ayi da ita kuma ba".
Cewar Inna Fatuh.
Lami ta shige gida tana jin bak'in cikin dawowarsu wannan gidan, da ace suna can gidansu ai da sai yadda tayi da wannan aljanar yarinyar.
Kamin su wuce ga mamakin Matar nan uwar yaron nan sai ji tayi Yaronta na cewa yanzu yana jin komai cike da murna yake fad'ar haka.
Inna Fatuh ta kallesu tana cewa.
"To daga yau sai kiyi ma D'anki gargad'in cewa karya sake Jan Jikata, dan k'ila a gaba zai iya rasa idanuwansa ma".
Itama ta k'are maganar tana d'aukar nik'anta dasu Laure suka aje, ta shige cikin gidan.
Malam ne ya tsaya ya sake ba Matar hakuri sosai...........
*FAƊIME...💋🌸💕*
_(Dangin Jinnu)_
©By Nainarh KD & Zahrah Royal Star
*Dedicated to Salma Ahmad Isah (Candy)*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*A love & Laugh story that will capture your heart and soul.*
05
*BAYAN SATI ƊAYA*