Sashe 10
Faɗime Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Faɗime ta kai maganar tana lumshe ido cike da zumuɗi bata jira Sa'ade da mamaki ya sa ta kasa magana ba ta ci gaba da faɗin.
“saboda haka yanzu kije tun kafin Laure ta fito ki faɗa ma ta labari ya sauya ba batun guduwa.”
Faɗime tana gama maganar ta juya abin ta zuwa gida domin zumuɗin zuwa birni take.
_____
DA RANA
Inna Lami ce durƙushe gaban Inna Fatuh tana faman yi ma ta magiya a kan ta bari a tafi da Faɗime Birni aikatau a gobe.
Yayin da Faɗime take zaune gefe tana faman kai loma kamar batasan abin da ke wakana ba.
“ke Lami nafa san ba mutunci ne dake ba ki faɗa min abin da kike shiryawa da kike wannan magiyar a kan na bar Faɗime taje Birni aikatau salon ki cutar min da ita ko to kuwa ba zata saɓu ba ehe wato saboda kin ga auren bai yiwu ba shi ne kika ɓullo ta nan.”
Inna Fatuh ta ƙare maganar tana bin Inna Lami da kallon banza.
Wani takaici ya cike Lami amma ta daure domin ita kaɗai ta san abin da take shiryawa a kan zuwan Faɗime Birnin, hakan ya sa ta ce.
“wallahi Inna Fatuh ba abin da nake shiryawa kawai dai nayi nadama ne da irin abubuwan da nake yi ma Faɗime a da.... ouch”
Ta kai maganar tare da sakin ƙara na azaba sakamakon wani tsunƙuli da a ka yi ma ta a baya.
Faɗime ta saki dariyar mugunta a fili da hakan ya sa duk suka dubeta sai ta ma ze da faɗin.
“Inna Fatuh kawai ki yarda kika sani ma ko na samo zuƙeƙen miji a can Birnin”
Washe bari Inna Fatuh ta yi jin kalaman Faɗime sai kawai ta duba Lami dake sakar ma ta harara a fakaice.
“to ai sai ki tashi ki bani wuri tun da ta amince kuma kada ki kuskura na gano kina shirya wani abin ne dan ba zan kyaleki ba.”
“ai Inna Fatuh ba ma abin da nake shiryawa.”
Cewar Lami sannan ta bar wurin cike da farin ciki ta lalubo ƙaramar nokiya ɗin wayarta ta kira Dillaliya ta sanar da ita halin da a ke ciki.
_____
“wai Faɗime shikenan yanzu tafiya Birnin zakiyi?”
Laure ta tambaya lokacin da su ukun suka haɗu a wurin da suka saba haɗu wa.
Sai da Faɗime ta gwagwiyi goribar hannunta sannan ta ce.
“da gudu ma, ke Laure ko dai baƙin ciki kike min ban sani ba?”
Da sauri Laure ta ce.
“Ni a wa Allah baki haƙuri kawai ina jajatawa ne zamuyi kewarki”
Sai Faɗime ta yi dariya tana faɗin.
“mu je nayi ɓarna na ƙarshe kafin na tafi birni domin ban san ranar dawowata ba.”
Ɗunguma suka yi suka nufa hanyar fadamar mai gari da suka ɗibo rake jiya.
____________
Hajiya Saleema uwar gidan Alhaji Sa'id Ahmad Lamiɗo tana da yara huɗu sun haɗa da Alhaji Ahmad da shi ne Babba sai kuma mai bi masa Eng. Khamis sannan sai Alhaji Tasi'u da kuma Prof. Ridwan sai kuma Auta wato Hajiya Saratu...
Sannan sai Hajiya Haleema yaranta biyu, Alhaji Dauda sai kuma Hajiya Laraba.
Duka suna zaune ne a SAL Estate tare da iyalansu baki ɗaya.
Hajiya Saratu wato mahaifiyar Fidaus ta kasance mace ce da bata yarda wani yafita da komai ba zata iya aikata komai muddun wani muradi nata da ta saka a gaba na son duniya zai cika sam bata yarda da faɗuwa ba al'amarin ta shi ya sa sam basa shiri da Mommy Matar Alhaji Dauda kasancewar Mommy ita ma halinta kusan ɗaya ne dana Hajiya Saratu na son abin duniya sai dai ta wani ɓangaren sun sha bamban. Kowacce tana Burin ganin tafi ɗaya a komai shi ya sa har yaransu sun taso a haka sam basa wani ga maciji tsakaninsu kuma hakan ya samo asali ne daga iyayen nasu mata, domin su iyayen maza kullum burinsu bai wuce ganin kan yaran nasu ya haɗu ba.
Alhaji Ahmad SAL yana da mata biyu Hajiya Zakiya da ake kira da Mamy sai kuma Hajiya Lubabatu da a ke kira da Nur.
Mamy yaranta huɗu curr, Salim, Maryam, sai kuma Muhammad da Saddika, yayin da Hajiya Lubabatu take da yara Biyar duk da kasancewarta mace ta biyu a gidan Alhaji Ahmad SAL sai dai ita ce macen da ya fara so tun ƙuruciya yayin da Hajiya Zakiya ta kasance auren haɗi a ka yi musu sai daga baya ne ya Aura Hajiya Lubabatu wato Nur, kuma ita ce mahaifiyar Safiuddin, Safiya ita ce ƴarta ta fari sai kuma Safiuddin mai bi ma ta sannan sai Jalil da Jalila twins sai kuma Auta Shaheeda.
Shekarun baya Mahaifan Safiuddin suka yi hatsarin mota lokacin suna tare da Jalilah a motar gaba ɗayansu babu wanda ya yi rai. Zo kuga tashin hankali wurin waɗan nan Ahali sosai suka girgiza da wannan mutuwar musamman ma Safiuddin da ƴan uwansa.
Prof Ridwan Matarsa ɗaya yaransu biyu rak, mace da namiji kuma suna zaune a ƙasar Faransa har wa yau kasancewarsa Ambassador.
Haka ma Eng. Khamis da Alhaji Tasi'u duk matansu ɗaiɗai kuma kowannensu Allah ya azurtashi da yara.
Sai kuma Alhaji Dauda Mijin Mommy matansa biyu Mommy ce ta biyu yayin da Hajiya Saima da ake kira da Ammiey ta kasance ta farko, Mommy yaranta biyu Asma da Fahat sai kuma Junaidiya da Sudais da kuma Firdaus yaran Ammiey.
Tsayawa ƙiyasa adadin familyn SAL ba abu ne mai sauƙi ba mu dai afka gadan-gadan cikin labarin a hankali za'a san kowa kuma halin kowa ya bayyana mu dai ci gaba da gashi kawai....🔥
*FAƊIME...💋🌸💕*
_(Dangin Jinnu)_
©By Nainarh KD & Zahrah Royal Star
*Dedicated to Salma Ahmad Isah (Candy)*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*A love & Laugh story that will capture your heart and soul.*
09
*FAD'IME POV*
Inna Lami dake kallon Fad'ime shirye take domin yau aminiyarta Inna Zubaida ita ke dillancin kai Yara aikatau tunda sanyin asubahi tayi mata a gidan su Fad'ime. Jikin Inna Lami har yana rawa wajan zuwa k'ofar d'akin Inna Fatuh domin taso k'eyar Fad'ime su wuce.
"Wai nikam Lami wannan sammako haka tunda uwar safiyar nan, miye kike buk'ata ne?".
Fad'in Inna Fatuh tana kallon Lami data fad'o masu d'aki tunda uwar safiya.
Sosa k'ayarta Inna Lami tayi tana inina wajan fad'in.
"Uhum uhum....da...dama...dama ga wacce zata tafi da Fad'ime can ta zo domin tafiyar wuri take".
Wani kallon rashin gaskiya Inna Fatuh ke bin Lami dashi d'an tashi tayi tana kallon Fad'ime dake bacci hankalinta kwance ta b'ararraje akan gadon Inna Fatuh sai baccinta take.
"Wace irin tafiya ce haka tunda sanyin asubahi?, to gaskiya bada ni ba wallahi domin sanin kanki ne kin san ba'a tayar da Fad'ime idan tana wannan baccin nata, idan ko tsautsayi yasa ka tayar da ita wallahi kaine masha wuya".
Wani duba Inna Lami tayi ma Inna Fatuh a zuciyarta zai dannk'ara ma Inna Fatun zagi take, a fali kuma ta saki murmushin yak'e tana cewa.
"Haba Inna Fatuh ai ke babu abunda take miki idan kika tayar da ita d'in, kawai ki tada ta ko sun wuce kar waje ya k'ure, karma ta ce ta fasa kaita wajan aikatau d'in".
Inna Fatuh zatai magana Fad'ime ta saki hamma mai sauti had'e da wata mik'a ta bud'e idonta, domin tun d'azo take jin y'ar hayaniya a cikin d'akin, maganganun su ne suka tayar da ita.
D'an tashi tayi tana duban Inna Fatuh da Inna Lami dake tsaye a tsakiyar d'akin d'an sak'o k'afarta tayi k'asa tana duban Inna Lami ta kalli Inna Fatuh tana turo baki gaba ta ce.
"Inna Fatuh sai hayaniya kuke min har kun tayar dani, Fisbilillahi basai ku fita waje kuyi firar tak'u ba".
D'an murmushi Inna Lami ta saki tana maganar zuci.
"Kaji y'ar iskar yarinya, ai insha Allahu idan na samu kika tafi keda gidan nan har abada wallahi, domin ba wani aikatau d'in da zaki je inda za'a wargaza rayuwarki can zakije, ai dama nayi rantsuwa bazan tab'a bari ki zama wani abu ba Fad'ime, ba aljanu ba, ko kuka ce a kanki inda za'aje dake yau sai kin Gwammace kid'a da karatu, ke saima kinyi danasanin zuwanki duniya Dan........
Maganar da Inna Fatuh ke mata ce ta katse maganar zucin da take fad'a tana yi ma ta kallon Fad'ime tana jefanta da murmushi, mai cike da gugar zana.
"Wai ke Lami tunanin miye kike haka?, sai magana nake na jiki Shuru, sai kallon Fad'ime kike kina murmushi, shin wai ko dai akwai muguntar da kike k'ullawa ne?, nifa tun farko ban yarda dake ba dama".
Fad'in Inna Fatuh tana k'arema Inna Lami wani kallon tuhuma sosai.
Cike da d'an firgice ta maze tana cewa da sauri
"Haba Inna Fatuh ki daina min irin haka mana, miye zan k'ullama Fad'ime ne, da duk da banyi mata mugunta ba sai yanzu kuma".
Tab'e baki Inna Fatuh tayi tana cewa
"Yo waye ya sani abu a duhu, kuma ai waye bai sanki ba da can baya, idan banda ido na, da bana raye Allah kad'ai yasan abunda zaki yima wannan marainiyar Allahn ai wallahi ke kima yi istigfari Lami waye bai san baki k'aunar Fad'ime ba"
A fakaice Inna Lami ke hararar Inna Fatuh dake maganar.
Fad'ime ta saki wani murmushin gefen baki tana duban Inna Lami ta ce.
"Nifa Inna Fatuh nama fasa tafiyar nan wallahi, domin wani mafarki nayi akanta, dan haka bazanje ba".
Baki a bud'e hankali a tashe kuma Inna Lami ke saurin fad'in, sai dai tun kamin ta fad'i abunda ke cin ranta, Inna Fatuh ta tari hanzarinta.
Da fad'in "shikenan falin lahil amdu, ai ni dama can ban wani ji tafiyar nan a raina ba, saboda nasan bak'in hali irin na Lami, tana iya kai ki inda za'a datse lumfashinki".
Baki na rawa Inna Lami ke fad'in.
“saboda haka yanzu kije tun kafin Laure ta fito ki faɗa ma ta labari ya sauya ba batun guduwa.”
Faɗime tana gama maganar ta juya abin ta zuwa gida domin zumuɗin zuwa birni take.
_____
DA RANA
Inna Lami ce durƙushe gaban Inna Fatuh tana faman yi ma ta magiya a kan ta bari a tafi da Faɗime Birni aikatau a gobe.
Yayin da Faɗime take zaune gefe tana faman kai loma kamar batasan abin da ke wakana ba.
“ke Lami nafa san ba mutunci ne dake ba ki faɗa min abin da kike shiryawa da kike wannan magiyar a kan na bar Faɗime taje Birni aikatau salon ki cutar min da ita ko to kuwa ba zata saɓu ba ehe wato saboda kin ga auren bai yiwu ba shi ne kika ɓullo ta nan.”
Inna Fatuh ta ƙare maganar tana bin Inna Lami da kallon banza.
Wani takaici ya cike Lami amma ta daure domin ita kaɗai ta san abin da take shiryawa a kan zuwan Faɗime Birnin, hakan ya sa ta ce.
“wallahi Inna Fatuh ba abin da nake shiryawa kawai dai nayi nadama ne da irin abubuwan da nake yi ma Faɗime a da.... ouch”
Ta kai maganar tare da sakin ƙara na azaba sakamakon wani tsunƙuli da a ka yi ma ta a baya.
Faɗime ta saki dariyar mugunta a fili da hakan ya sa duk suka dubeta sai ta ma ze da faɗin.
“Inna Fatuh kawai ki yarda kika sani ma ko na samo zuƙeƙen miji a can Birnin”
Washe bari Inna Fatuh ta yi jin kalaman Faɗime sai kawai ta duba Lami dake sakar ma ta harara a fakaice.
“to ai sai ki tashi ki bani wuri tun da ta amince kuma kada ki kuskura na gano kina shirya wani abin ne dan ba zan kyaleki ba.”
“ai Inna Fatuh ba ma abin da nake shiryawa.”
Cewar Lami sannan ta bar wurin cike da farin ciki ta lalubo ƙaramar nokiya ɗin wayarta ta kira Dillaliya ta sanar da ita halin da a ke ciki.
_____
“wai Faɗime shikenan yanzu tafiya Birnin zakiyi?”
Laure ta tambaya lokacin da su ukun suka haɗu a wurin da suka saba haɗu wa.
Sai da Faɗime ta gwagwiyi goribar hannunta sannan ta ce.
“da gudu ma, ke Laure ko dai baƙin ciki kike min ban sani ba?”
Da sauri Laure ta ce.
“Ni a wa Allah baki haƙuri kawai ina jajatawa ne zamuyi kewarki”
Sai Faɗime ta yi dariya tana faɗin.
“mu je nayi ɓarna na ƙarshe kafin na tafi birni domin ban san ranar dawowata ba.”
Ɗunguma suka yi suka nufa hanyar fadamar mai gari da suka ɗibo rake jiya.
____________
Hajiya Saleema uwar gidan Alhaji Sa'id Ahmad Lamiɗo tana da yara huɗu sun haɗa da Alhaji Ahmad da shi ne Babba sai kuma mai bi masa Eng. Khamis sannan sai Alhaji Tasi'u da kuma Prof. Ridwan sai kuma Auta wato Hajiya Saratu...
Sannan sai Hajiya Haleema yaranta biyu, Alhaji Dauda sai kuma Hajiya Laraba.
Duka suna zaune ne a SAL Estate tare da iyalansu baki ɗaya.
Hajiya Saratu wato mahaifiyar Fidaus ta kasance mace ce da bata yarda wani yafita da komai ba zata iya aikata komai muddun wani muradi nata da ta saka a gaba na son duniya zai cika sam bata yarda da faɗuwa ba al'amarin ta shi ya sa sam basa shiri da Mommy Matar Alhaji Dauda kasancewar Mommy ita ma halinta kusan ɗaya ne dana Hajiya Saratu na son abin duniya sai dai ta wani ɓangaren sun sha bamban. Kowacce tana Burin ganin tafi ɗaya a komai shi ya sa har yaransu sun taso a haka sam basa wani ga maciji tsakaninsu kuma hakan ya samo asali ne daga iyayen nasu mata, domin su iyayen maza kullum burinsu bai wuce ganin kan yaran nasu ya haɗu ba.
Alhaji Ahmad SAL yana da mata biyu Hajiya Zakiya da ake kira da Mamy sai kuma Hajiya Lubabatu da a ke kira da Nur.
Mamy yaranta huɗu curr, Salim, Maryam, sai kuma Muhammad da Saddika, yayin da Hajiya Lubabatu take da yara Biyar duk da kasancewarta mace ta biyu a gidan Alhaji Ahmad SAL sai dai ita ce macen da ya fara so tun ƙuruciya yayin da Hajiya Zakiya ta kasance auren haɗi a ka yi musu sai daga baya ne ya Aura Hajiya Lubabatu wato Nur, kuma ita ce mahaifiyar Safiuddin, Safiya ita ce ƴarta ta fari sai kuma Safiuddin mai bi ma ta sannan sai Jalil da Jalila twins sai kuma Auta Shaheeda.
Shekarun baya Mahaifan Safiuddin suka yi hatsarin mota lokacin suna tare da Jalilah a motar gaba ɗayansu babu wanda ya yi rai. Zo kuga tashin hankali wurin waɗan nan Ahali sosai suka girgiza da wannan mutuwar musamman ma Safiuddin da ƴan uwansa.
Prof Ridwan Matarsa ɗaya yaransu biyu rak, mace da namiji kuma suna zaune a ƙasar Faransa har wa yau kasancewarsa Ambassador.
Haka ma Eng. Khamis da Alhaji Tasi'u duk matansu ɗaiɗai kuma kowannensu Allah ya azurtashi da yara.
Sai kuma Alhaji Dauda Mijin Mommy matansa biyu Mommy ce ta biyu yayin da Hajiya Saima da ake kira da Ammiey ta kasance ta farko, Mommy yaranta biyu Asma da Fahat sai kuma Junaidiya da Sudais da kuma Firdaus yaran Ammiey.
Tsayawa ƙiyasa adadin familyn SAL ba abu ne mai sauƙi ba mu dai afka gadan-gadan cikin labarin a hankali za'a san kowa kuma halin kowa ya bayyana mu dai ci gaba da gashi kawai....🔥
*FAƊIME...💋🌸💕*
_(Dangin Jinnu)_
©By Nainarh KD & Zahrah Royal Star
*Dedicated to Salma Ahmad Isah (Candy)*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*A love & Laugh story that will capture your heart and soul.*
09
*FAD'IME POV*
Inna Lami dake kallon Fad'ime shirye take domin yau aminiyarta Inna Zubaida ita ke dillancin kai Yara aikatau tunda sanyin asubahi tayi mata a gidan su Fad'ime. Jikin Inna Lami har yana rawa wajan zuwa k'ofar d'akin Inna Fatuh domin taso k'eyar Fad'ime su wuce.
"Wai nikam Lami wannan sammako haka tunda uwar safiyar nan, miye kike buk'ata ne?".
Fad'in Inna Fatuh tana kallon Lami data fad'o masu d'aki tunda uwar safiya.
Sosa k'ayarta Inna Lami tayi tana inina wajan fad'in.
"Uhum uhum....da...dama...dama ga wacce zata tafi da Fad'ime can ta zo domin tafiyar wuri take".
Wani kallon rashin gaskiya Inna Fatuh ke bin Lami dashi d'an tashi tayi tana kallon Fad'ime dake bacci hankalinta kwance ta b'ararraje akan gadon Inna Fatuh sai baccinta take.
"Wace irin tafiya ce haka tunda sanyin asubahi?, to gaskiya bada ni ba wallahi domin sanin kanki ne kin san ba'a tayar da Fad'ime idan tana wannan baccin nata, idan ko tsautsayi yasa ka tayar da ita wallahi kaine masha wuya".
Wani duba Inna Lami tayi ma Inna Fatuh a zuciyarta zai dannk'ara ma Inna Fatun zagi take, a fali kuma ta saki murmushin yak'e tana cewa.
"Haba Inna Fatuh ai ke babu abunda take miki idan kika tayar da ita d'in, kawai ki tada ta ko sun wuce kar waje ya k'ure, karma ta ce ta fasa kaita wajan aikatau d'in".
Inna Fatuh zatai magana Fad'ime ta saki hamma mai sauti had'e da wata mik'a ta bud'e idonta, domin tun d'azo take jin y'ar hayaniya a cikin d'akin, maganganun su ne suka tayar da ita.
D'an tashi tayi tana duban Inna Fatuh da Inna Lami dake tsaye a tsakiyar d'akin d'an sak'o k'afarta tayi k'asa tana duban Inna Lami ta kalli Inna Fatuh tana turo baki gaba ta ce.
"Inna Fatuh sai hayaniya kuke min har kun tayar dani, Fisbilillahi basai ku fita waje kuyi firar tak'u ba".
D'an murmushi Inna Lami ta saki tana maganar zuci.
"Kaji y'ar iskar yarinya, ai insha Allahu idan na samu kika tafi keda gidan nan har abada wallahi, domin ba wani aikatau d'in da zaki je inda za'a wargaza rayuwarki can zakije, ai dama nayi rantsuwa bazan tab'a bari ki zama wani abu ba Fad'ime, ba aljanu ba, ko kuka ce a kanki inda za'aje dake yau sai kin Gwammace kid'a da karatu, ke saima kinyi danasanin zuwanki duniya Dan........
Maganar da Inna Fatuh ke mata ce ta katse maganar zucin da take fad'a tana yi ma ta kallon Fad'ime tana jefanta da murmushi, mai cike da gugar zana.
"Wai ke Lami tunanin miye kike haka?, sai magana nake na jiki Shuru, sai kallon Fad'ime kike kina murmushi, shin wai ko dai akwai muguntar da kike k'ullawa ne?, nifa tun farko ban yarda dake ba dama".
Fad'in Inna Fatuh tana k'arema Inna Lami wani kallon tuhuma sosai.
Cike da d'an firgice ta maze tana cewa da sauri
"Haba Inna Fatuh ki daina min irin haka mana, miye zan k'ullama Fad'ime ne, da duk da banyi mata mugunta ba sai yanzu kuma".
Tab'e baki Inna Fatuh tayi tana cewa
"Yo waye ya sani abu a duhu, kuma ai waye bai sanki ba da can baya, idan banda ido na, da bana raye Allah kad'ai yasan abunda zaki yima wannan marainiyar Allahn ai wallahi ke kima yi istigfari Lami waye bai san baki k'aunar Fad'ime ba"
A fakaice Inna Lami ke hararar Inna Fatuh dake maganar.
Fad'ime ta saki wani murmushin gefen baki tana duban Inna Lami ta ce.
"Nifa Inna Fatuh nama fasa tafiyar nan wallahi, domin wani mafarki nayi akanta, dan haka bazanje ba".
Baki a bud'e hankali a tashe kuma Inna Lami ke saurin fad'in, sai dai tun kamin ta fad'i abunda ke cin ranta, Inna Fatuh ta tari hanzarinta.
Da fad'in "shikenan falin lahil amdu, ai ni dama can ban wani ji tafiyar nan a raina ba, saboda nasan bak'in hali irin na Lami, tana iya kai ki inda za'a datse lumfashinki".
Baki na rawa Inna Lami ke fad'in.