← Book details Faɗime Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 2 OF 13

Sashe 2

Faɗime Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A taƙaice dai a Ranar sunan Lami ta samu ta faki ido ta bar gidan zuwa wurin Malam kasan komai domin neman mafita na wannan al'amari domin so take daga Jaririyar har uwan nata duka su baƙunci halira.

Sai dai sosai jikinta ya yi sanyi lagwas lokacin da ta ƙari sa wurin Malam kasan komai tun kafin ta sanar da shi abin da ya faru ya rufe ta da masifa kamar zai cinye ta ɗanye sakamakon kuskuren da ta tafka ya kuma tabbatar ma ta ba shi ba koda wurin wani Malamin tsubbu ko boka zataje to fa ba mai iya kashe ma ta wannan Jaririya Muddun ba Allah ne ya so hakan ta kasance ba.
Sai dai duk da haka bata karaya ba ta buƙaci a yi aikin da zai sa Malam ya dena bawa uwan da Jaririyar kulawar da yake basu a saka yaji duk Duniyar nan babu waɗan da ya tsana kuma bai san gani fa ce Ummah da ƴarta. Anan ne kuma Kasan komai ya tabbatar ma ta da aiki zai yiwuwa muddun zatayi biya mai kyau kuma ta cike da wasu matakai, ba musu ya yarje masa a taƙaice dai kafin ta bar wurinsa sai da suka yi abin da suka saba muddun ta kai masa ziyara to fa sai sun kusanci juna....

_______
________
_______

TO FA! ANA DARA GA DARE YA YI. GA DAI DA YADDA LABARIN NAMU MAI TAKEN FAƊIME (DANGIN JINNU) YA FARA. YA KUKE GANIN ZATA KASANCE? TO MU DAI HAƊU A FEJI NA GABA, KAR A MANTA DA YIN LIKE, SHARE FISABILILLAH

ZAHRAH ROYAL STAR CE TARE DA NAINARH KD SUKA TSARA KUMA SUKA RUBUTA ✍️🤍

*FAƊIME...💋🌸💕*
_(Dangin Jinnu)_

©By Nainarh KD & Zahrah Royal Star

*Dedicated to Salma Ahmad Isah (Candy)*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*A love & Laugh story that will capture your heart and soul.*

02

*ƘAUYEN KINKIBA, KADUNA STATE.*

*GIDAN MALAM YAHAYA*

*Five Years later*

"Haba Auta miye Fad'ime tayi maka ne da zaka kai mata wannan dukan haka, ai K'anwarka ce".

Cewar Umma ta k'are maganar tana jawo Fad'ime dake zaune a k'asa tana wasan k'asa irin na yara duk da dukan da Auta ya kai mata batai kuka ba bare tari sai ma wasan data ci gaba tana kallonsu da idanuwanta masu haske cikinsu kamar na mage.

"Baki ga miye tamin bane?, nifa na tsaneta bana sonta haka kawai duk ta zo tafi y'an gidanmu kyau k'ila ma ba y'ar gidanmu ba ce can akaje a ka samo mana ita a ka k'ak'ubama Abbanmu ita"

"Kaii Auta ubanwa ya gaya maka wannan maganar"

Umma ta idasa maganar tana neman kai masa mari a fuska. Wuffff Lami ta fito daga d'aki har zanin dake d'aure a k'ugunta na neman kwancewa tsabar masifa har bakinta na kunfa wajan cewa.

"Lahhh karki kuskura ki ce zaki tab'a min Yaro, bamu kwashi y'an kallo dake ba yanzun nan ehee"

"Amma Iya Lami kina jin abunda yake fad'a min, kuma kin san hakan bai dace ba ina a matsayin matar ubans......

Lami ta katseta da hanzari tana cewa

"Kee kinga bana son jin soki burutsinki. Kuma ai Yaro gaskiya ya fad'a duk cikin dangin Malam babu mai kyan wannan d'iyar taki mai kama da Iskokai ai Yaro ya fad'i gaskiya yo wa ya sani ma ko cikinta akaje aka yo daga waje aka zo aka k'ak'uba Malam shi"

Umma tayi shuru tana jin zuciyarta na zafi sosai bata san sadda hawaye suka cika mata ido ba. Batai aune ba taga Fad'ime ta gangaro har inda take tana tab'a mata k'afa, jiki a sanyaye tasa hannu ta d'auki d'iyarta, ga mamakinta sai taga Yarinyar tasa hannunta tana d'an share mata hawayen dake mata zuba.

Wani dogon tsaki Lami ta saki tana juya ga Auta ta dafasa tana cewa.

"Kai da'aAllah rabu da ita je abunka ka ci gaba da wasanka, naga ubanda ya isa ya hanaka watayawa a cikin gidan ubanka".

Umma bata sake cewa komai ba kusan a tare zasu juya domin barin wajan Auta dake wasa kawai suja ji ya fasa wata gigitacciyar k'ara ya fad'i a k'asa yana shure-shure.

Habawa ai a haukace Lami tayo kansa Umma ma ta aje Fad'ime a k'asa tana yo wajan.

Lami ta kamasa tana faman jijjigasa tana tabbayar miye ya sameshi miye yake masa ciwo duk ta rud'e ta fita hayaccinta. Ganin Umma na neman b'atasa yasa Lami a haukace muryarta har tana shak'ewa ta dubi inda Umma take ta d'aga mata hannu tana cewa.

"Karki sake ki tab'a min d'ana karki sake ki k'araso inda muke. Kuma wallahi komi ya sami Yaro na to wallahi wannan y'ar iskar yarinyar taki ce sila domin naga ana tab'a ta aljanunta ke d'aukar mataki to ni dai nafi k'arfinsu nan gani nan bari, yo waye ma yasan k'ila aljana kika haifa ba mutum ba ce".

Wata dariya Lami taji an b'ab'b'ake da ita a zabure ta kai dubanta wajan Fad'ime inda take jiyo dariyar, wani zaro ido tayi waje tana kallon yadda yarinyar ke kallonta tana mata dariya harda tab'a hannu.

Sakin Auta tayi tana murza idonta da k'arfi ta bud'e again dai dariyar take mata had'e da gwalo ma take gani.

"Innallihi wa'inna alaihir raju'on na shiga uku na, Wallahi Malam an haifar maka masifa a cikin gida, wallahi wannan d'iyar taki masifa ce a cikin jama'a"

Umma ta waiga inda Lami ke kallon ita dai D'iyarta ta gani zaune hasalima wasanta take irin na Yara.

Tsaye tayi kawai tana kallon ikon Allah.

Zuwa can Malam ya fad'u gidan kamar wadda akai ma kiranye.

Shima a rud'e kamar wadda akace ma Auta ya mutu ya nufi inda yake.

Ai Lami na ganin Malam ya shigo ta fashe da kukan munafurci tana cewa.

"Ni dai wallahi Malam na gaji, na gaji wallahi gara na bar maka gidanka dana zauna bak'in cikin matarka ya kashe ni, ita da aljanar yarinyar can tata, Fisbilillahi yanzu nan suna wasa da Auta yarinyar nan kawai mukaji Auta ya fad'i yana shure-shure, kuma na rantse da Allah ita ce tayi masa wani uban, dan haka wallahi idan Yaro na bai dawo yadda yake ba, na rantse da tsarkin mulkin Allah yau koto ce zata rabani dake wallahi".

Lami ta k'are maganar tana kallon Umma data daskare waje d'aya.

Gani tayi Malam ya mik'e ya nufi inda Fad'ime take kawai sai dai taji saukar k'arar Mari, ba shiri ta zabura ta nufi inda Malam yake ganin yadda ya Mari y'ar yarinyar da bata san miye duniyar take ciki bama.

Ido a waje Umma ta warce yarinyarta tana shafa fuskarta yarinyar ko tari batai ba bare tayi kukan Marin da Malam d'in yayi mata, hasali ma dariyarta take masa tana wangale masa bakinta wadda ba hak'ora cikinsa.

Shi kansa Malam d'in mamakin yarinyar ya fara kashe zuwa yanzu, kwata-kwata ji yake ba wadda ya tsana irin uwar d'iyar nan da ita kanta yarinyar.

Umma cike da tsananin mamakin Malam d'in a kullum da yake k'ara kashe mata jiki ta ce

"Malam yanzu dana barka saika ci gaba da dukan wannan y'ar yarinyar?, da bata san miye ma take yi ba, yanzu komai aka fad'a maka sai kawai ka hau sama ka zauna ka yarda, miye wannan yarinyar zatai ma Auta Fisbilillahi kawai saboda anga ina hakuri kuma bana magana, kai kuma baka son gaskiya yanzu sa.......

Tasssss

Rauntse idonta tayi da k'arfi had'e da dafe k'uncinta, bata san hawa ba bata san sauka ba kawai taji an d'auke ta da Mari, Abun bai sake bata mamaki sai da taga ashe Malam ne da wannan aiki yana tsaye kanta sai huce yake kamar wani Zaki kamar ace masa takk ya rufeta da duka gaba d'aya.

Lami tana daga gafe sai sakin dariya take had'e da jin dad'in yadda yanzu ta gama malke Malam gaba d'aya sai abunda ta ce shine yake yi, idan aka tab'a ta da ita da yaranta kuwa yi yake kamar ya yanka mutum tsabar yadda yake mugun tsoronta a yanzu.

Wasu zafafan hawaye ne suka shiga zarya akan fuskar Umma ba abunda take sai kallon Malam. Tunda take dashi bai tab'a daga hannunsa da sunan ya dake ta, sai a yanzu duk da tsawon shekarun nan taga abubuwa na wulakanci daga garesa da Matarsa Lami wacce abun ya samo asali ne tun washe garin da aka haifi Fatima, Lami ta fita ita ce bata dawo ba sai wajan dare kuma tunda ta dawo Umma taji gabanta na fad'uwa sosai saboda ganin yadda Lami ke sakar mata wani irin murmushi mai kamar gugar zana.

Tun wannan lokacin shikenan zaman lafiya da jin dad'i ya k'are ma Umma da ita da abunda ta haifa yau bak'i gobe fari. Gashi gaba d'aya Yaran Iya Lami sun raina Umma rashin kunya babu wacce bata gani bare Auta yafi kowa iya rashin kunya sai ya gaya mata maganar da ko a mafarki bazaka ce shine yayita ba, garama sauran su sun zama manya ba wani zama gidan suke ba sosai.

"Malam......

"Kimin shuru, ki sauk'e d'iyar nan taki ta warware abunda tayima Auta idan ba haka ba ranki daga ke har ita sai yayi mummunan b'aci wallahi"

Nuna kanta take Umma tana kiran.

"Malam yanzu miye wannan yarinyar zata yi ma Auta, duk fa wannan abun canfi ne fa ni yarinyata mutum ce kamar kowa bata da wani abu wallahi".

Ganin Auta ya mik'e sai raba ido yake yasa Lami rungumesa tana kallon Umma ta mik'e dashi rik'e a jikinta tana cewa.

"Barta Malam sa'arta d'aya D'ana ya mik'e, bance kuma ka sake ta ba har sai lokacin dana ga damar ta bar min cikin gidana daga ni sai Yara na, ai tunda kika ce zakiyi kishi da Lami shige ka fasa wallahi".

Ko a jikin Malam kamar wadda ake ba umarni haka ya fara gyad'a ma Lami kai sai ka ce wani Yaronta wadda ta haifa da cikinta.

Ta sake kallonsa tana cewa.

"Muje ciki Malam"

Sumi-sumi ya bi bayanta suka shige d'akin Lamin Umma na tsaye tana kallon ikon Allah.
Chapter 2 · 0% Book details