← Book details Faɗime Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 13

Sashe 3

Faɗime Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A hankali taji ana share mata hawaye, k'aro ma d'iyar tata ido tayi tana mamakin yarinyar indai zata ga tana kuka to tabbas ita ce zaka sameta tana share mata hawayen dake zubo mata, wayonta bai kai tasan hakan ba, kallonta take tana so ta gano miye yasa Mutane ke mata kallon wacce ba mutum ba, bare su Iya Lami dake hurara abun a wajan mutane suna muzanta mata yarinya. Wani irin taji a jikinta tana jin tausayin yarinyar tata a yau d'in, haka nan taji a jikinta ba lallai suyi rayuwa mai tsawo da yarinyarta, wani irin tsananin tausayin d'iyarta ne ya rufeta, ya rayuwarta zata kasance idan bata nan?, miye zai faru da ita idan bata gidan Mahaifinta?, tana gidan ma ya aka k'are inaga kuma ace bata nan babu idonta a cikin gidan...........

*FAƊIME...💋🌸💕*
_(Dangin Jinnu)_

©By Nainarh KD & Zahrah Royal Star

*Dedicated to Salma Ahmad Isah (Candy)*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*A love & Laugh story that will capture your heart and soul.*

03

*One week later.*

“Innallihi wa'inna alaihir raju'on, jama'a ku kawo ɗauki gini ya danne Umman Faɗime da ita kanta Faɗimen ku kawo agaji jama'a!”

Iya Lami ce ke wannan kururuwar ta ɗaura hannu a ka cikin tashin hankali yayin da take tsaye gaban gidan Malam Yahaya dake ta faman rushewa yadda ka san an kasa motar rushe gini ana rusawa haka ginin gidan ta ko'ina yake ci gaba da rushewa yayin da Iya Lami take ci gaba da kururuwar neman taimako, ai kuwa lokaci ƙanƙani jama'a suka cika ƙofar gidan kowa yana tambayar abin da yake faruwa, ita kam Iya Lami ta ruɗe ba abin da take iya faɗa fa ce a kawo ɗauki gini ya rufe FAƊIME da mahaifiyarta, ai kuwa hankali tashe jama'a suka fara neman yadda za'a ɓullo ma lamarin kar a rasa rai biyu ana cikin haka sai ga Malam Yahaya ya dawo hankali tashe domin labari ya kai masa ai kuwa da ƙari sowarsa bai kula Iya Lami dake ƙoƙarin yi masa bayanin yadda al'amarin ya kasance ba, gadan-gadan ya nufa cikin gidan da ya gama rushewa faɗi yake.

“Mata ta! 'yata! Jama'a ku taimaka ‘yata da Matata suna ciki gini ya rushe da su.”

Ganin da gaske dai ƙoƙarin shiga ciki yake ne ya sa maƙocinsa Malam Idi ya yi saurin riƙo shi yana bashi haƙuri.

Ita kam Iya Lami tsabar baƙin ciki da ganin halin ruɗani da Malam Yahaya ya shiga ya sa ta dakata cak daga kukan munafurcin da take yi duk da ta wani bangaren zuciyarta fal domin tasan koba komai FAƊIME da Mahaifiyarta sun mutu sanadin wannan rushewar ginin da ita ce sila.

Curko curko kowa ya yi cike da alhini na wannan abu da ya faru sai da ƙyar ma wata ta sama zarafin faɗin.

“amma garin ya ya wannan lamari ya kasance?”

Ta kai maganar tana kallon Iya Lami da ta yi nisa Duniyar tunani a kan yadda zata ɓullo wa lamarin malam dan ta lura aikin baya ya fara sakin jikinsa dole yana buƙatar sabon aiki.

“ah eh uhm! E dama fa, dama...”

“dama me?”

Malam Idi Mijin Matar da ta yi tambayar ya katse Iya Lami da faɗin hakan sai kuma kallo gaba ɗaya ya koma kanta, Iya Lami ganin asirinta yana shirin tonuwa ta yi saurin faɗin.

“dama daga maƙota nima na fito kwatsam naga gidan yana rushewa kuma FAD'IME da umman ta duk suna ciki....”

Ƙoƙarin zubewa ƙasa da Malam Yahaya ke yi ya sa ta kasa ƙari sa maganar ta yi saurin kamo shi tana kiran sunanshi.

Sosai jikin mutanen wurin ya yi sanyi ganin irin halin da malam yahaya ya shiga domin sambatu ya shiga yi faɗi yake.

“Allah Sarki Rayuwa shikenan kuma na rasaki Umman Fatima matar kirki duk irin cin kashin da nakeyi miki da wulaƙanci keda ‘yarki baki taɓa buɗe baki kin yi ƙorafi ba kullum cikin haƙuri kike dani gashi yau na rasa ku gaba ɗaya wayyo rayuwa kaico...”

“haba mana Malam me ya sa kake faɗin hakan ne ai wani sai ya ɗauka Mugun wuya kake bawa Umman FAƊIME ka gyara kalamanka dai”

Cewar Iya Lami tana zazzaro ido kamar wacce ta yi ma sarki ƙarya.

Malam Yahaya bai kulata ba sai ma miƙe wa daga zaunen da yake da ya yi tare da nufar hanyar gidan nasa da ya gama rushewa zuwa yanzu.

Yayin da wata cikin matar unguwa dake wurin ta katse Iya Lami da faɗin.

“ke dai Lami kiyi shiru kawai in ba so kike ayi 'yar tone-tone ba domin kam wuya dai Umman FAƊIME tana sha a hannunki dan ma Allah yayi ta mai haƙuri ne da kuma kauda kai shi ya sa kawai...”

Shiru kakeji Iya Lami bata tanka ta ba domin ji take tana ƙara magana asirinta ne zai tonu, a ka ce mara gaskiya ko'a ruwa gumi yake.....

Buguzun buguzun haka take tafiya irin nasu na tsofi har ta ƙari so Anguwan da 'yan kullin kayanta a hannu sai dai tun daga shigowarta layin take hango mutane tsai-tsaye bata gama mamaki ba ta hango har da ɗanta Yahaya tsaye a wurin ta buɗe baki da mamaki sai kawai ta hango saitin gidansa da ya zama fili sai bulon ginin da ya rushe ai ba shiri a tamanin ta ƙara sauri tana faɗin a bata hanya ta ga abin da yake faruwa da kyau ko dai makuwa ta yi ba gidan ɗan ta Yahaya ba ne.

“Iya kece anan kuma?”

Malam Yahaya ta tambaya murya sanyin ƙalau yana ƙoƙarin ƙari sawa wurin da Mahaifiyar nasa take.

“ni ce ɗan nan ka ganni da safen nan gajiya nayi ina so naga Takwarata mai sunan manya kwana biyu ana yi min rowarta shi ne nazo da kaina na ganta ka ganni harda tsaraba nayo ma ta ita da mahaifiyarta mai kyawun hali dana fuska ba irinsu oh oh ba, sai dai gashi na ƙari so gidan naga lissafin ya canza kamar na rikice a toh Fisabilillah ban da na rikice me zai sa na dinga ganin fili a wuri maimakon naga ginin gidan ka...”

Wani kuka ne ya taho ma Malam Yahaya jin kalaman da mahaifiyarsa ke yi sai ya daure amma ya rasa ta inda zai yi ma ta bayani domin bai san ta inda zai fara ba, ita kuma taƙi shiru sai tambayar abin da yake faruwa take.

Da ƙyar dai ya samu ya buɗe baki ya ce.

“Fatima da mahaifiyarta...”

Kasa ƙari sa maganar ya yi sakamakon hango FAƊIME da ya yi ta shigo layin a guje fuskarta ta yi futu futu da ƙasa da alama daga wasar ƙasa take sam bata lura da mutanen dake tsai-tsaye curko curko a wurin ba kai tsaye ta wuce wurin gidansu. Sai dai cak ta ja ta tsaya tana ƙare ma yadda gidan ya koma da kallo tashi ɗaya sai kawai ta fasa ihu tare da juyawa gadan-gadan ta nufa wurin da Iya Lami take tana gwarancinta tun kafin ta ƙari sa Malam Yahaya ya yi saurin riƙo ta ya haɗa da jikinsa yana sauke ajiyar zuciya da hamdala ga Allah na ganin ashe FAƊIME bata cikin gidan.

Sai lokacin ya sama zarafin yi ma Iya Fatuh bayanin abin da yake faruwa, ai kuwa ta yi matuƙar girgiza da jin wannan al'amari ta kuma fusata jin kalaman da matan unguwan ke yi na irin zaman haƙuri da Ummah takeyi a gidan kuma bata ƙara tabbatarwa ba sai ganin ƙiri-ƙiri FAƊIME taƙi zuwa wurin Malam Yahaya duk kuwa da yadda ya so, ai kuwa kunyar Duniyar nan da kuma dana sani ya cika shi.

Daga ƙarshe dai an samu an sama wasu sun fito da gawar mahaifiyar FAƊIME daga cikin gidan yayin da Iya Fatuh ta wuce da FAƊIME can gidan gado da take zaune da sauran iyalanta dama Malam Yahaya ne kawai yake gidansa daban dan bashi da ra'ayin zama a gidan gado sai dai sanadin wannan iftila'in da ya faɗa masa na rushewar gida da ba'a san mene ne sila ba ya sa ba shiri ya koma gidan gado shida Lami da sauran yaransa, a ranar a ka yi ma mahaifiyar FAƊIME sallah da komai a ka wuce da ita gidanta na gaskiya, yayin da kacokan raino da riƙon FAƊIME ya koma hannun Iya Fatuh dama taso tun ya ye a bata ita to Malam Yahaya ne yaƙi yarda yanzu kuma bashi da bakin musu haka Rayuwar ta ci gaba da gangarawa yayin da Malam Yahaya suke zaune a gidan gado da sauran dangi gefe guda kuma riƙon FAƊIME ya koma hannun Iya Fatuh gaba ɗaya dan ta rantse koda Aure malam yahaya ya ƙara to fa ba zata bashi FAƊIME ba bare kuma ace bai ƙara aure ba kuma ya yi zaton zata bawa Matarsa Lami Matar da batasan mutunci ba dan sam Lami da Iya Fatuh basa ga maciji tsakaninsu kuma hakan ya samo asali ne tun lokacin da Malam Yahaya zai Aure Lami ita Iya Fatuh bata so amma haka Malam Yahaya ya kafe dole a ka yi auren.

WANNAN KE NAN.

*Eleven years later*

*FAƊIME...💋🌸💕*
_(Dangin Jinnu)_

©By Nainarh KD & Zahrah Royal Star

*Dedicated to Salma Ahmad Isah (Candy)*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*A love & Laugh story that will capture your heart and soul.*

04

*FAD'IME POV*

"Inna Fatuh kiyi sauri ki ban kud'in nik'an mana, K'awaye na na jira a waje fa"

Fad'ime ta k'are maganar tana kallon k'ofar d'akin Inna Fatuh.

Da sauri Inna Fatuh ta fito tana k'irga kud'i, ta kalli Fad'ime dake dubanta ta ce.

"Y'ar albarka Fad'ime ta, dan Allah karki tsaya wasa da jan matune fad'a kinji, kar a kawo min k'ararki yau kinji, karki tsaya ko ina ki amso nik'an kawai ki dawo gida kinga yamma tayi"

Turo baki kawai Fad'ime tayi tasa hannunta ta amshi kud'in tayi waje da gudu.

Tana gaf ficewa daga zauran gidan kawai taji ta bangaje mutum, bata tsaya bada hakuri ba zata k'ara gaba, taji an jawota ta baya an d'auke ta da wani irin Mari tasssss.

"Kan uba"....

Fad'ime ta fad'a tana ware idonta akan Auta dake tsaye yana kallonta cike da jin haushinta sosai, duk da yasan tab'a Fad'ime a wajansa ba abu bane mai dad'i da zai biyo baya.
Chapter 3 · 0% Book details