← Book details Exiled Prince Part 4 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 23

Sashe 1

Exiled Prince Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read

❤⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❤

🔥👑 ( LOVE MEETS POWER ) 👑🔥

( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )

STORY & WRITTEN BY : MEERAH ⚘🕊

【THE ROYALTY LOVE ❤🌹】

【 BOOK ________4 📚🔥❤ 】

😂😂😂 TO BARI MU GA WANNAN SABUWAR DRAMAR YA ZA TA KARE 🤣🤣

SAKO GA MA SU YI SHARING LITTAFI BA TARE DA SANI NA BA !

* ALLAH NA GANIN KU IN NI BAN GANI 😴😴😴 *

_______________________♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡______________________

{ P A G E ............ 1 & 2🌹🕊}

▪SRORY 🔥

A hankali Malik ya mike ya na fadin " ki kontar da hankalinki , ina nan zuwa gobe " ya na gama fadar haka ya sauko wayar ya katse kiran
haka ya ci gaba da latsa wayar shi , ya dan jima kafin ya kai wayar a kunne babu ko sallama ya ce " ina jiran ka Saudiya gobe , tare da Familyna " ya na gama fadar haka ya sauko wayar ya katse kiran ya mike tsaye
kai tsaye stair ya nufa ya Haye ya koma bedroom din su
ko da ya shiga dressing room ya wuce , ya shirya kayan su cikin trolley guda babba , ya fiddo ta ya ajiye bakin kofar

sannan ya nufi bed din su ya haye ya na sauke ajiyar zuciya , ya lumshe idanunshi
ya na a haka ya jiyo Muryar ta ta na fadin " yaya Zayd , gida za mu koma ? "
ba tare da ya bude idanunshi ba ya ce " No , ke a nan za ki zauna , ni ma ba zan jima zan dawo "

" what ? me ya sa ? ni gaskiya tare za mu tafi , ina so na ga su Ammie " ta fada kamar za ta yi kuka

a hankali ya ware idanunshi ya juya su na fuskantar juna ya ce " ki yi hakuri Cutie ki zauna a nan , wlh idan ki ka bi ba zan samu nitsuwar yin aikin da ya mayar da ni , idan ki na nan hankali na zai fi konciya , ba zan so wani abu ya same ki tare da babyn mu ba "

" ni gaskiya yaya Zayd tare za mu tafi , ka na bukata ta a kusa da kai , ni wlh ko ka tafi ka bar ni sai na bi bayan ka , in ya so na bace saman hanyar "

" please my Cutie , kar ki raba min hankali gida biyu , kin ga ko kwana biyu ba zan yi ba zan dawo "

a hankali ta juyo ta ba shi baya , kawai sai ta sakin mishi kuka ba tare da ta ce komai ba

" ya salam !" ya furta cen kassan makoshi
a hankali ya kai hannu ya janyo ta jikin shi ya hade bayan ta da kirjin shi ya ce " shikenan , rigimamiya kawai, mu tafi , amma wlh ba za ki fito bedroom din ki ba "

wata yar karamar dariya ta yi dama ba kukan ta ke ba kawai dai ta san duk lokacin da ta ke mishi kuka ya na yi mata abun da ta ke so

cikin sanyin murya ta ce mishi " Baby , na yi kewar Su Ammie sosai , da mama , da Nesi , da Aunty RIANNA , Aunty Tesnim ........ "

cikin nitsuwa ya katse ta da cewa " uhm uhm , ki ce duk Saudiyar ma kin yi kewar ta "

wata yar karamar dariya ta yi kafin ta ce " Eh , na yi kewar Saudiya sosai "

a hankali ya matso ya manna mata kiss saman forehead kafin ya ce " su ma sun yi kewar ki my Cutie , now rufe ido ki yi barci "

noke mishi kafada ta yi ta na fadin " ni ba barcin da zan yi , ina farin ciki Sosai za mu koma gida gobe "

a hankali ya dan matso kusa da ita , murya kassa kassa kamar mai rada ya ce mata " okay , mu yi wani game din , har yanzu ban koshi ba "

hararrar shi ta yi ta wutsiyar ido , tun kafin ta ce wani abu ya riga ta cewa " Matsalar wannan katon cikin naki na tare min hanyata "

turo mishi dan bakin nan nata ta yi ta na fadin " ni ka daina ce min me katon ciki "

" okay , okay , yanzu dai ba ni na sha , har yanzu yunwa na ke ji "

hannu ta kai ta janyo duvet ta rufe jikin ta , har da kai , kafin ta ce mishi " no , ni barci na ke ji "

marairaice mata murya ya yi ya na fadin " please my Cutie , wai kin ji wani dadi da ki kara ? Allah ji na ke kamar na kama da wuta , please ki yi wani abu a kai mana "

wata yar karamar dariya ta yi , amma ba ta ce mishi komai ba
shi ma bai ce mata komai ba ya janyo duvet din ya shige ciki shi ma
sai da su ka gama buga wassan su , sannan su ka yi barci , har yanzu dai bai sauya ba da wannan muguwar sha'awar tashi , dan sai da ta dinga rokon shi ya kyale ta , ta na yi mishi magiya , sannan ya hakura ya bar ta , shi ma dan ya na tsoron ya ji wa Baby Nayel ne ciwo ya hakura , ba dan haka ba sai dai ta kwana ta rokon shi ba zai bar ta ba

▪BAYAN SALLAR ASUBA ⛅

tsaye Malik ya ke bakin kofar shiga parlourn , ya na sanye da wandon jeans black color , da T-shirt red color , ya daura wata jacket black color da ga sama , ya na tsaye sai faman duba watch din hannun shi ya ke

ya na tsaye a haka Inaya ta fara sauko stair , ta na sanye da wata Abaya pink color , sai dan karamin hijab din ta white color dai'dai kirji , ga katon cikinta ya yi tsaye
a hankali ta ke sauko stair din ,
tun da ta fara saukowa ya tsare ta da ido babu ko kiftawa
har sai da ta karaso gaban shi ta tsaya , ta na shagwabe fuska , ta na faman turo bakin nan nata kamar ya ce zai yi mata kiss

matse gera ya yi ya na nuna mata hanyar fita parlourn ya ce " wuce mu tafi , da wani katon cikinki kamar ball "

murguna mishi baki ta yi ta na yi mishi hararrar kassa ido kafin ta daga kafa ta fice
sai da ya kashe duk lamps din parlourn , sannan ya bi bayan ta su ka fita
kai tsaye get din fita gidan su ka nufa , ta na gaba ya na bayan ta
su na fitowa gidan ta ga motar shi bakin kofar an yi parking din ta , ga gateman nan tsaye geffen ta

su na fitowa Malik ya bude mata kofar motar ta shiga a hankali , sannan ya juya ya yi wa gateman magana kafin ya juya ya nufi wajen driver ya shiga ya tada motar kai tsaye ya nufi airport

su na isa , su ka shiga private jet din shi , lokaci guda Jet din ya daga ya nufi kassar Saudiya

▪AFTER SOME HOURS

▪MASARAUTAR SAUDIYA ❤

Misalin karfe 9 na safe , jirgin su ya sauka a kassar Saudiya
tun da ya shigo kassar ya ga komai ya sauya mishi kamar ba Saudiyar da ya sani ba
bai gama shan mamaki ba sai da ya isa bakin kofar Daular Saudiya
a nan ya ga wasu status guda biyu na lions sun bude bakunansu , ga wasu Sword biyu gaban kawuna su , a takaice tambarin Daular Ottoman ne a kafe bakin kofar Daular Saudiya da ga gani kuma na zallar gold

a haka Malik ya danne abun cikin zuciyar shi ya shiga Daular
nan ya tabbatar da cewa Eh Aymane ba Al'heri ya ke shukawa ba , dan duk Daular ta ruguje
garden din ta ya bushe kamar ba a taba yin ciyayi a wajen ba , duk ginin sun kwararabe da ga gani ba a kula da su

a hankali Inaya ta tabo hannun shi ta na cewa " yaya Zayd , an ya nan gidan mu ne ? ba ka yi batan kai ba ? "

murya a sanyaye ya ce mata " No my Cutie , ban yi batan kai ba , in sha Allah komai zai koma kamar da farko "

ba ta ce mishi komai ba ta tsaya ta bin wajen da kallo ga jikin ta ya yi mugun sanyi
duk inda motar su ta wuce sai an tsaya a na bin ta da kallo
Malik kuwa kai tsaye part din MALIKAT HOUDA ya nufa ya yi parking din motar bakin kofar shiga part din

ya na yin parking ya kashe motar ya kalli ta cikin glass din motar
ya ga kowa ya tsaya waje guda su na kallon motar allamun su na jiran su ga wanda zai fito da ga ciki
a hankali ya sauke ajiyar zuciya , kafin ya kai hannu ya bude kofar motar ya sauko da kafar shi guda ,
sai da ya dan jinkirta kafin ya fiddo gudar kafar ya fito da ga cikin motar

duk wanda ke wajen sai da ya saki kuka lokaci guda ganin Malik ya dawo cikin masarautar
shi kan shi sai da idanunshi su ka ciko da ruwa

a hankali ya fara bin wajen da kallo , cen ya hango Azim ya tunkaro shi da mugun gudu ya na daga mishi hannu , ga idanun shi nan cike da ruwa

haka Malik ya tsaya ya na kallon shi , har sai da ya kusa kawowa wajen motar ya yi tuntunbe ya fadi
da gudu Malik ya nufe shi , ya na zuwa ya Zube saman guyiwowinshi ya tallabo Azim ya na fadin " Azim , ba ka ji ciwo ba ? "
Chapter 1 · 0% Book details