Sashe 68
Duniya Ta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Koda duka awanninmu na yau zaka qarar sir mun sadaukar maka dasu" Sauran suka shiga gyada kai. Kowannensu da wani irin qawa zuci da qauna ta gaske yake zaune dashi,duk da ba'a rasa qananu matsaloli da kowacce tafiya bata rabo dashi,amma ya gina wani irin qaunarshi a zukatansu da sadaukarwa me tarin gaske,wanda shi kansa baisan ya gina din ba. Saidai kuma abune sananne,duk wajen da ake samun kulawa tausayi da kyautatawa dole qauna ta biyo baya. Fada ce ta ma'aiki,an gina zukata abisa son wanda ke kyautata musu da qin wanda ke munana musu.
"Alright.....na gode" Ya fada da salon daya sake sanyawa kowa nutsuwa da qaunarsa a zuciya.
Boyayyar ajiyar zuciya mika'il din ya saki,gumi yana fara tsatsatsafo masa. Yafi kowa son samun kusanci da jadda......yafi kowa son ganin yafi kusancin dashi,yanaso yafi kowa samun fada da dama,don haka shi yafi cancanta ya nuna zallar biyayyarsa ga boss din ba wasu ba,don haka ya saki wani murmushi
"As you wish sir.....mu duka muna qarqashin cewarka ne". Kadan fuad ya waiwaya ya kalleshi,sai ya gyada masa kai ba tare da yace komai ba.
Gyara zamansa yayi saman kujerar kamar tana mintsininsa ne,yana jin kamar babbar asara tana shirin samunsa ne,kaman zai rasa wannan babbar damar ne a yau,wadda muddin ya rasata din baisan ranar da zai sake samunta ba. Sake danna wayarsa yayi ta kawo haske,lokacin da suka tsara zasu hadun yana dab da cika.
Wajen SMS ya shiga,ya rubuta gajeran saqo ya tura mata,idanunsa suna kan wayar yana fatan samun amsa daga wajenta,duk da kuwa yasan abune me wahalan gaske.
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
PAGE 68
Tunda suka dawo daga makarantar hankalinta yana kan wayar,dama kawai take nema da sabreen din zata fita ta samu ta fidda wayar. Ta tabbatar yayi kiranta har ya gaji,yanzun haka qila yana cike ne da kewarta.
Sunyi hira me tsaho dashi jiya cikin toilet,wanda ta dinga mamakin yadda yasan wasu abubuwan a kansu,saidai amsar daya bata ta cire dukkan wani zargi nasa daga ranta
"Indai zakiyi mamakin yadda akayi nasan rayuwarki huda ashe son da nake miki ma baikai nan ba......kina wasa da kalar soyayyar da nakeyi miki ko?" Idanunta ta lumshe har cikin zuciyarta tana jin a yau din bayan yaa sabreen din ta sake samun wani barin zuciyar wanda ya damu da rayuwarta ya kuma damu da damuwarta. Har yake iya sanin wacece ita a rayuwa ba tare data sani ba saboda tsananin son da yake mata
"Inason na daukeki daga gidanku huda.....na killaceki daga rayuwar da kike ciki......na hana kunnuwa da idanuwanki ji ko ganin duk wani mummunar kalma duk don saboda yaa sabreen....". Ta riga tayi amanna yasan komai kawai a kansu har akan sabreen din,don haka sai ta lumshe ido zuciyarta tana karyewa
"Ba rayuwar da tafi rayuwar aure daraja da martaba a wajen mace.....qila idan yaa sabreen dinki taga zakiyi aure itama tayi" Ya fada cikin salon karya harshe dason nuna yadda zuciya ta karye,saidai a gefe guda yana sone kawai ya cusa wani kakkaifan abu a zuciyarta.
"Banji dadin shaidar dana ji daga bakunan mutane a kanta ba.....don nima a yanzun ina daukarta kamar yaya take a gareni".
"Hameed....." Ta katseshi cikin rauni.
"Muyi kowacce magana dakai amma banda ta yaa sabreen,don zuciyata me rauni ce a kanta,ita din komai namu ce....."
"I know huda.....i know,but inason na killaceki huda na daukaka darajarki.....inason ta silarki ya sabreen dinki ta zauna waje daya,ta samu martaba irinta....." Sai kuma yayi shuru bai qarasa ba,shurun da itama hudan da zuciyarta ke mata zugi ta zabi yinsa.
"Zamuyi waya anjima idan kin samu lokaci.....i so much love you....please take care" Ya fadi yana katse kiran ya barta da yawa a hannu.
Zare wayar tayi daga kunnenta jikinta yana yin sanyi. Kenan kowa ma yana dora tuhuma akan yaa sabreen?,kowa ma yana da zargi a kanta?. Idan dai har Hameed da yake baqo a unguwar dama rayuwarsu gaba daya zai iya samun wani abu a kanta to ya kenan sauran jama'a suke kallonta?.
Shin gaskiya Hameed yake fadi?,tayi aurenta kawai ko hankalin yaa sabreen dinta zai dawo daidai?. To shin me yasa yaa sabreen din ba zata zauna kaman kowacce mace ba?. Me yasa bayan ta samu kudaden da sun isa ta riqe musu rayuwa?.....me yasa ba zata haqura ba?....me yasa?,meye dalilinta?,idan a baya tana da hujja tana da dalili yanzun meye dalilinta?.
Wadannan tarin tambayoyin su suka dinga yi mata kai kawo,sannu a hankali sai taji kaman tana da ja akan sabreen din,tana kuma qalubalantarta duk da harshe ko aikinta bai nuna ba....... Amma tun daga sannan can qasan zuciyarta wutar hakan tana ruruwa sannu a hankali.
Kamar wadda ke ciwon jiki haka ta dinga aiwatar da komai. Duk da tana da daukan lokaci wajen wanka da shirinta amma a yau din sai abun ya sake ninkuwa.
Ta gyare gashinta ta kuma dameshi cikin band madaidaici,ta gama shafa cream dinta na musamman dake qarawa fatarta glowing cikin kowanne yanayi,amma kuma saita kasa ci gaba da yin komai.
Bata taba ayyukan da suka tsaye mata a rai takejin ta takura ba irin aikin Mikhail dana mashkur da cikin qarshen satin nan zata yishi. Batasan dalili ba......amma ta alaqanta hakan da canzawar salon aikin. Ma'ana kowannensu zata kasance dashi cikin dakin hotel daga awa daya har zuwa sanda aikin zai kammala. Shin tana da tabbacin kubuta daga hannun miyagun kurayen da dama dama suke nema irin wannan?,mutanen da suke kallon diya mace cikin idanuwansu da wani irin duba kwatankwacin duban da mayunwacin zaki kewa nama a yayin da sukayi arangama?.
Tana zaunen amma tana lura da yawan shige da ficen da huda keyi tsakanin falon zuwa dakinsu. Kaman zatayi mata magana sai kuma ta basar,don tana da wani irin dabi'a nabin komai da idanu har sai sanda ta samu cikakken hujja ko makama a kanshi.
Qarar yar siririyar wayar da tasan kiranta na dabanne shine ya dauki hankalinta. Wanda ta zata din shine kuwa,Jib ne,sai ta daga kiran tana rage volume na kiran.
"Hello jib?" Ta furta daidai sanda huda ke ficewa a dakin. Samun kanta tayi da jan qaramin tsaki can qasan ranta. Jib?....ko waye kuma da wannan sunan?,zai iya yiwuwa wannan shirin da takeyi ma fita zatayi,kuma wajensa zata je,idan mace da namiji suka kebanta a waje daya kuma me zai biyo baya?,idan taje gurinsa me zasu aikata?..... Tambayar data yiwa kanta kenan ta qarshe data sanya bugun zuciyarta qaruwa,saita samu kanta tana saurin dakatar da kanta daga wannan tunanin tana furta
"A'uxubillah" Wani sashen na zuciyarta kuma yana gaya mata
"Yaa sabreen ce fa?" Idanunta ta lumshe tana son sake jaddadawa kanta eh.....ya sabreen ce,amma wani sashen kuma yana qoqarin maidata baya.
"Yadda kika tsara abun bazai yiwu ba sister.....dole ya kasance kuna tare nan da awa guda......mafi kyau kuma ku isa wajen tare koda xaku shiga ta qofa daban dabanne......don na bincika a yanzun kamar suna dakin meeting da boss dinsu..... Meeting din kuma zai zamana sun tattauna muhimman abubuwa.....na lissafa zasu soma lissafi na kudaden da company ke dashi a qasa......zasuyi musayar documents da bayanai,zaa tashi ba tare da sun kammala ba don bayanan yana da yawa,kuma owner na kamfanin jadda baya saba lokaci......wadannan bayanan da zasu kasance tare dashi ina da buqatar wasu abubuwa a ciki da zasu sauqaqamin kutsa kai cikin account din muyi aikinmu da wurwuri mu gama.......inaso kuma aikin na gamashi ne a daidai lokacin da masu kula da komai nasu suka tafi hutun fitowa daga meeting din....idan zaiyiwu ki samu kaiwa office dinsa,akwai wani ajiyayyen code cikin files na office din da zaki ciromin,kin fahimta?"
Dukkanin bayanan sa ta fahimta ta kuma gamsu,to amma kimarta fa?. Bata saba yin magana ta dawo ta warware ta ba
"Kada kiyi tunanin komai.....wannan ce rana ta qarshe tsakaninki dashi.....kuma wadannan sune awannin qarshe da aishatu keda chance na tsallakewa siradinta".
"Ba damuwa" Ta bawa jib amsa a taqaice tana yanke kiran.
Wayar ta aje a gabanta kawai tana kallonta tare da tunanin da yadda zata sake requesting wa mika'il din su kasance tare tun yanzu?. Kaman ana jira ta yiwa kanta tambayar saiga shigowar saqonsa.
Tana duba saqon tana jin sanyi da yadda komai yazo mata a sauqaqe. Duk da hakan ya faranta mata amma saita ajiye wayar bayan ta gama dubawa,ta miqe kawai ta isa wardrobe dinta tana laluben suturar da zata dace da jikinta da kuma yanayin.
Shurun nata da rashin samun amsarta ya qara masa yawan rashin sukuni. Ya dinga duba wayarsa duk bayan wucewar wasu mintuna,har sai daya kasa jurewa ya sake tafa massage dij har sau biyu ya tura mata a jere.
Saqon ya shigo mata sanda take daura agogon hannunta ne,tun taga sunan tasan shine,bata bi takai ba sai data gama daurawar,ya qara barima a kunnenta tayi Rolling mayafin Turkish dress din,ta kuma jawo kimono din kayan da suke zuwa tare da shirt me dogon hannu da skirt din ta aza saman kayan sannan ta dauki wayar ta bude tana maida masa amsa
"What's the adress?.....zan taddaka har inda kake don farincikinka".
Sai data maimaita karanta saqon kusan sau hudu,tana mamakin yau itace da kanta zata turawa wani d'a namiji saqo da yayi kama da wannan?. Ji tayi kaman ba zata iya turawar ba,ta aje wayar saman madubi tana furzar da iska daga bakinta
"No way out" Taji zuciyarta na gaya mata,dole ta tura muddin tanason cika mission din. Tana so ta rabu ne da mikail.....ba kuma zata iya barinsa salin alin ya wuce hakanan ba,sai ta miqa hannunta ta sake bude wayar,ta danna send sannan ta maida wayar ta ajiye.
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
PAGE 69
Bayan maimaita karanta saqon da yayi,har sai data kaishi ga murza idanun nasa don ya tabbatar daidai ya gani ko kuwa akasin hakan?.
Jikinsa har rawa yake wajen maida mata reply,har bai lura da yadda Muhammed jadda ya zuba masa idanu ba yana karantar yanayinsa.
"Mr mika'il" Ya kirayi sunansa da husky voice dinsan nan dake ratsa zukata su kuma maida hankalin mutum zuwa jikinsa.
"Alright.....na gode" Ya fada da salon daya sake sanyawa kowa nutsuwa da qaunarsa a zuciya.
Boyayyar ajiyar zuciya mika'il din ya saki,gumi yana fara tsatsatsafo masa. Yafi kowa son samun kusanci da jadda......yafi kowa son ganin yafi kusancin dashi,yanaso yafi kowa samun fada da dama,don haka shi yafi cancanta ya nuna zallar biyayyarsa ga boss din ba wasu ba,don haka ya saki wani murmushi
"As you wish sir.....mu duka muna qarqashin cewarka ne". Kadan fuad ya waiwaya ya kalleshi,sai ya gyada masa kai ba tare da yace komai ba.
Gyara zamansa yayi saman kujerar kamar tana mintsininsa ne,yana jin kamar babbar asara tana shirin samunsa ne,kaman zai rasa wannan babbar damar ne a yau,wadda muddin ya rasata din baisan ranar da zai sake samunta ba. Sake danna wayarsa yayi ta kawo haske,lokacin da suka tsara zasu hadun yana dab da cika.
Wajen SMS ya shiga,ya rubuta gajeran saqo ya tura mata,idanunsa suna kan wayar yana fatan samun amsa daga wajenta,duk da kuwa yasan abune me wahalan gaske.
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
PAGE 68
Tunda suka dawo daga makarantar hankalinta yana kan wayar,dama kawai take nema da sabreen din zata fita ta samu ta fidda wayar. Ta tabbatar yayi kiranta har ya gaji,yanzun haka qila yana cike ne da kewarta.
Sunyi hira me tsaho dashi jiya cikin toilet,wanda ta dinga mamakin yadda yasan wasu abubuwan a kansu,saidai amsar daya bata ta cire dukkan wani zargi nasa daga ranta
"Indai zakiyi mamakin yadda akayi nasan rayuwarki huda ashe son da nake miki ma baikai nan ba......kina wasa da kalar soyayyar da nakeyi miki ko?" Idanunta ta lumshe har cikin zuciyarta tana jin a yau din bayan yaa sabreen din ta sake samun wani barin zuciyar wanda ya damu da rayuwarta ya kuma damu da damuwarta. Har yake iya sanin wacece ita a rayuwa ba tare data sani ba saboda tsananin son da yake mata
"Inason na daukeki daga gidanku huda.....na killaceki daga rayuwar da kike ciki......na hana kunnuwa da idanuwanki ji ko ganin duk wani mummunar kalma duk don saboda yaa sabreen....". Ta riga tayi amanna yasan komai kawai a kansu har akan sabreen din,don haka sai ta lumshe ido zuciyarta tana karyewa
"Ba rayuwar da tafi rayuwar aure daraja da martaba a wajen mace.....qila idan yaa sabreen dinki taga zakiyi aure itama tayi" Ya fada cikin salon karya harshe dason nuna yadda zuciya ta karye,saidai a gefe guda yana sone kawai ya cusa wani kakkaifan abu a zuciyarta.
"Banji dadin shaidar dana ji daga bakunan mutane a kanta ba.....don nima a yanzun ina daukarta kamar yaya take a gareni".
"Hameed....." Ta katseshi cikin rauni.
"Muyi kowacce magana dakai amma banda ta yaa sabreen,don zuciyata me rauni ce a kanta,ita din komai namu ce....."
"I know huda.....i know,but inason na killaceki huda na daukaka darajarki.....inason ta silarki ya sabreen dinki ta zauna waje daya,ta samu martaba irinta....." Sai kuma yayi shuru bai qarasa ba,shurun da itama hudan da zuciyarta ke mata zugi ta zabi yinsa.
"Zamuyi waya anjima idan kin samu lokaci.....i so much love you....please take care" Ya fadi yana katse kiran ya barta da yawa a hannu.
Zare wayar tayi daga kunnenta jikinta yana yin sanyi. Kenan kowa ma yana dora tuhuma akan yaa sabreen?,kowa ma yana da zargi a kanta?. Idan dai har Hameed da yake baqo a unguwar dama rayuwarsu gaba daya zai iya samun wani abu a kanta to ya kenan sauran jama'a suke kallonta?.
Shin gaskiya Hameed yake fadi?,tayi aurenta kawai ko hankalin yaa sabreen dinta zai dawo daidai?. To shin me yasa yaa sabreen din ba zata zauna kaman kowacce mace ba?. Me yasa bayan ta samu kudaden da sun isa ta riqe musu rayuwa?.....me yasa ba zata haqura ba?....me yasa?,meye dalilinta?,idan a baya tana da hujja tana da dalili yanzun meye dalilinta?.
Wadannan tarin tambayoyin su suka dinga yi mata kai kawo,sannu a hankali sai taji kaman tana da ja akan sabreen din,tana kuma qalubalantarta duk da harshe ko aikinta bai nuna ba....... Amma tun daga sannan can qasan zuciyarta wutar hakan tana ruruwa sannu a hankali.
Kamar wadda ke ciwon jiki haka ta dinga aiwatar da komai. Duk da tana da daukan lokaci wajen wanka da shirinta amma a yau din sai abun ya sake ninkuwa.
Ta gyare gashinta ta kuma dameshi cikin band madaidaici,ta gama shafa cream dinta na musamman dake qarawa fatarta glowing cikin kowanne yanayi,amma kuma saita kasa ci gaba da yin komai.
Bata taba ayyukan da suka tsaye mata a rai takejin ta takura ba irin aikin Mikhail dana mashkur da cikin qarshen satin nan zata yishi. Batasan dalili ba......amma ta alaqanta hakan da canzawar salon aikin. Ma'ana kowannensu zata kasance dashi cikin dakin hotel daga awa daya har zuwa sanda aikin zai kammala. Shin tana da tabbacin kubuta daga hannun miyagun kurayen da dama dama suke nema irin wannan?,mutanen da suke kallon diya mace cikin idanuwansu da wani irin duba kwatankwacin duban da mayunwacin zaki kewa nama a yayin da sukayi arangama?.
Tana zaunen amma tana lura da yawan shige da ficen da huda keyi tsakanin falon zuwa dakinsu. Kaman zatayi mata magana sai kuma ta basar,don tana da wani irin dabi'a nabin komai da idanu har sai sanda ta samu cikakken hujja ko makama a kanshi.
Qarar yar siririyar wayar da tasan kiranta na dabanne shine ya dauki hankalinta. Wanda ta zata din shine kuwa,Jib ne,sai ta daga kiran tana rage volume na kiran.
"Hello jib?" Ta furta daidai sanda huda ke ficewa a dakin. Samun kanta tayi da jan qaramin tsaki can qasan ranta. Jib?....ko waye kuma da wannan sunan?,zai iya yiwuwa wannan shirin da takeyi ma fita zatayi,kuma wajensa zata je,idan mace da namiji suka kebanta a waje daya kuma me zai biyo baya?,idan taje gurinsa me zasu aikata?..... Tambayar data yiwa kanta kenan ta qarshe data sanya bugun zuciyarta qaruwa,saita samu kanta tana saurin dakatar da kanta daga wannan tunanin tana furta
"A'uxubillah" Wani sashen na zuciyarta kuma yana gaya mata
"Yaa sabreen ce fa?" Idanunta ta lumshe tana son sake jaddadawa kanta eh.....ya sabreen ce,amma wani sashen kuma yana qoqarin maidata baya.
"Yadda kika tsara abun bazai yiwu ba sister.....dole ya kasance kuna tare nan da awa guda......mafi kyau kuma ku isa wajen tare koda xaku shiga ta qofa daban dabanne......don na bincika a yanzun kamar suna dakin meeting da boss dinsu..... Meeting din kuma zai zamana sun tattauna muhimman abubuwa.....na lissafa zasu soma lissafi na kudaden da company ke dashi a qasa......zasuyi musayar documents da bayanai,zaa tashi ba tare da sun kammala ba don bayanan yana da yawa,kuma owner na kamfanin jadda baya saba lokaci......wadannan bayanan da zasu kasance tare dashi ina da buqatar wasu abubuwa a ciki da zasu sauqaqamin kutsa kai cikin account din muyi aikinmu da wurwuri mu gama.......inaso kuma aikin na gamashi ne a daidai lokacin da masu kula da komai nasu suka tafi hutun fitowa daga meeting din....idan zaiyiwu ki samu kaiwa office dinsa,akwai wani ajiyayyen code cikin files na office din da zaki ciromin,kin fahimta?"
Dukkanin bayanan sa ta fahimta ta kuma gamsu,to amma kimarta fa?. Bata saba yin magana ta dawo ta warware ta ba
"Kada kiyi tunanin komai.....wannan ce rana ta qarshe tsakaninki dashi.....kuma wadannan sune awannin qarshe da aishatu keda chance na tsallakewa siradinta".
"Ba damuwa" Ta bawa jib amsa a taqaice tana yanke kiran.
Wayar ta aje a gabanta kawai tana kallonta tare da tunanin da yadda zata sake requesting wa mika'il din su kasance tare tun yanzu?. Kaman ana jira ta yiwa kanta tambayar saiga shigowar saqonsa.
Tana duba saqon tana jin sanyi da yadda komai yazo mata a sauqaqe. Duk da hakan ya faranta mata amma saita ajiye wayar bayan ta gama dubawa,ta miqe kawai ta isa wardrobe dinta tana laluben suturar da zata dace da jikinta da kuma yanayin.
Shurun nata da rashin samun amsarta ya qara masa yawan rashin sukuni. Ya dinga duba wayarsa duk bayan wucewar wasu mintuna,har sai daya kasa jurewa ya sake tafa massage dij har sau biyu ya tura mata a jere.
Saqon ya shigo mata sanda take daura agogon hannunta ne,tun taga sunan tasan shine,bata bi takai ba sai data gama daurawar,ya qara barima a kunnenta tayi Rolling mayafin Turkish dress din,ta kuma jawo kimono din kayan da suke zuwa tare da shirt me dogon hannu da skirt din ta aza saman kayan sannan ta dauki wayar ta bude tana maida masa amsa
"What's the adress?.....zan taddaka har inda kake don farincikinka".
Sai data maimaita karanta saqon kusan sau hudu,tana mamakin yau itace da kanta zata turawa wani d'a namiji saqo da yayi kama da wannan?. Ji tayi kaman ba zata iya turawar ba,ta aje wayar saman madubi tana furzar da iska daga bakinta
"No way out" Taji zuciyarta na gaya mata,dole ta tura muddin tanason cika mission din. Tana so ta rabu ne da mikail.....ba kuma zata iya barinsa salin alin ya wuce hakanan ba,sai ta miqa hannunta ta sake bude wayar,ta danna send sannan ta maida wayar ta ajiye.
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
PAGE 69
Bayan maimaita karanta saqon da yayi,har sai data kaishi ga murza idanun nasa don ya tabbatar daidai ya gani ko kuwa akasin hakan?.
Jikinsa har rawa yake wajen maida mata reply,har bai lura da yadda Muhammed jadda ya zuba masa idanu ba yana karantar yanayinsa.
"Mr mika'il" Ya kirayi sunansa da husky voice dinsan nan dake ratsa zukata su kuma maida hankalin mutum zuwa jikinsa.