← Book details Duniya Ta Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 66 OF 80

Sashe 66

Duniya Ta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Kamfaninsa fa?,yanzu lissafin shima tare kukeyi?". Dan qaramin murmushi me sauti hajja ta fidda tana aza hannunta saman kan budurwar dake kwance saman cinyarta tana amsa waya itama

"To meye a ciki?,nice uwarsa fa?,akwai wani abu da suka isa su boyemin?,koda cikin gidajensu akayi abu koda da darene da safe kuwa rana bata bullowa bansan komai ba......ke banda ma ina taka birki ma wasu abubuwan......ai hatta sunnar aure da matansu sai sanda na bada iznin a yita,kuma idan anyin sai an fada min"

"Innalillahi......ke hajja?" Maamah ta furta cikin tsananin mamaki

"Ke?.....zauna kina wasa da lamarin yaran yanzu,kina sake musu hanya sai linzaminsu ya koma hannun matansu,keda wahalar raino da daukan ciki amma wata ita keda d'an,kin zama 'yar kallo,sai abinda tace a tsakuro a sammiki.....tun daga kan yahaya na fara daukan izina.....ban kuma zauna ba har yau har magajin gobe" .

Duka mamaki ya gama kashe maamah,amma kuma bayanan hajja din sai suka gamsar da ita,ta kuma yarda cewa gaskiya ta fadi,gashi yanzun ita tana fafutukar karbar 'ya'yanta daga hannun wata ma tun basuyi aure ba?.

"Yanzun ya ake ciki?,komai ya tafi dai dai ko?" Ajiyar zuciya maamah ta saki tana maida hankalinta ga hajjan

"Hajja ba abinda sukaci fa?.....duk wahalar nan kin ganni da kayana suka barni....."

"Karki gaggawa,idan ba yau akwai gobe,idan ba gobe akwai wani satin"

"Haka nake gayawa kaina......kana iya target din abu amma shekara goma gaba kake hangowa.....zamu zuba dasu in sha Allah......wannan karon banga abinda ya isa ya hanani ko ya dakatar da burina ba" Ta fadi har qasan zuciyarta tana jin confidence akan wannan.

"Sirrin samun nasararmu dama itace jajircewa naci da kafiya". Hajjan ta qara mata qwarin gwiwa.

Sun tattauna sosai har na kusan mintuna talatin kafin su yanke kiran. Hajjan ta sauke wayar wani murmushi na fita daga fuskarta,tadan tsuke bakin ta lissafinta yana tafiya da nisa sosai.

"Mommy ga adeel zaku gaisa" Budurwar ta fadi tana daga kanta daga saman cinyarta hadi da miqa mata wayar. Sai data kalleta sannan ta amsa wayar ta sanya a kunnenta.

Ba yabo ba fallasa ta amsa gaisuwar nashi,ba jimawa sukayi sallama ta miqawa yarinyar wayar tana kallonta. Kallon hajja kawai a garesu yana da fassarori,don haka tayi masa sallama ta katse wayar ta ajiyeta a gefe tana kallon hajjan

"Momy lafiya?" Numfashi ta ajiye tana dubanta duba na kai tsaye

"Ina sake gaya miki......nayi miki tanadi,kada ki kuskura ki zurfafa a soyayya da kowa....don kowa a cikin rayuwarki temporary ne......akwai target dina.....kuma bazanyi missing target dina ba tabbas" Tayi maganar da sautin da zai gaya maka tayi maganar ne da gasken gaske daga zuciyarta,ta kuma yi maganar tana kafe autartata da idanu don ta sake jaddada mata girman maganar.
*D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

PAGE 66

Itama duban momyn nata take yi,ta sani tabbas momy din nata tana matuqar ji da ita.....kaman yadda ta sani taci buri sosai a kanta. Duk da hakan tana da buqatar qarin haske a maganarta,don haka ta motsa kadan

"Momy.....wanne irin buri ne?,ta yaya zan iya sallamar dukkan kuma wadanda muke tare dasu yanzu?"

"Bance ki sallamesu yanzu ba,tukunna dai.....amma dai abune da kika sani cewa.....ke din ba kalar qananun maza bace....ban haifeki don wani me jaririn arziqi a hannunsa ya aureki ba.....plan dina kuma idan lokaci yayi zakiji....don ku yaran yanzu kwata kwata bakusan me ake nufi da sirri ba".

*****Ta jima zaune gefan gadonta tana juya wayarta a hannu. Mikail takeson kira,ta kuma shirya haduwarsu kaman yadda ta tsara zata kammala da babinsa ta kuma rufeshi kwata kwata cikin shafukanta kamar yadda ta binne maza masu yawan gaske. To amma haka kawai duk sanda tayi attempting na kiran nashi sai taji kaman kada ta kira din.

Wani sashe na zuciyarta na bata qwarin gwiwar ta kira

"Ya cancanci ya fuskanci komai......ya kuma cancanci kowanne irin hukunci,jin kunyar mara kunya asara ce!" Ta sake jin wani sauti daga can qasan zuciyarta yana rada mata maganar har zuwa kunnuwanta.

Danna kiran tayi,ta kuma tattara dukka nutsuwarta akan wayar tana sauraren yadda Kiran ke tafiya kai tsaye zuwa layin mika'il din.

A kasalance yake shiryawa,kasancewar daren jiya ya shawu. Duk da ya tsagaita shan ma,bai wani sha yadda yakeso ba,saboda ya sani safiyar yau din litinin tana cikin ranaku masu muhimmanci da zai gana kai tsaye da CEO. Mutum na farko kaf rayuwarshi dake masa wani irin kwarjini,kwarjinin daya tabbatar yana da alaqa da kamewarsa......da yadda fara'a ko murmushi sukayi nesa da fuska dama rayuwarsa gaba daya.

Ya jima yana so ya shiga rayuwarsa fiye da matsayinsa,amma kuma ya gaza samun wannan fuskar. Mutum ne da idan ya zauna aiki kawai,baya daukan wata magana da ba cikin aiki take ba,kamar yadda baya daukan wasa ko kuma wargi.

Yadda dukkan ma'aikatan dake aiki qarqashin kamfanin suke da iyakoki......haka nan dukkan wata magana da zaiyi dakai akwai iya adadin lokacin da yake baka.

Qarar wayarsa ta ja hankalinsa sanda take saka links na rigarsa,sai ya dakata cak daga abinda yakeyi din cikin tsananin mamaki yana kallon wayar.

"What a wonderful day" Ya fada qasa qasa yana daukan wayar ya zauna gefan kujera. Wani mamakin yana sake kasheshi da idanunsa suka tabbatar masa eh itace take kiransa

"Yau kuma da kanta?,da wanne irin sa'a na tashi?" Ya yiwa kansa tambayar yana daga kiran ba tare daya tsawaita dogon tunani ba.

Kamar kowanne lokaci tayi masa sallama wadda shikam ba kasafai yake iya tunawa da ita ba. Sai yadan daburce kadan kafin ya amsa sallamar ya dora da fadin

"Good morning queen....nayi kira nayi kira har na gaji anqi a dagamin waya.... Kwatsam sai gashi na tsinci wani abu da ban taba kawowa zai faru ba".

Murmushi ta saki kadan wanda ko kusa da gefen zuciyarta bai kai ba,yayin da shi kuma kunnuwansa yaji kaman zasu narke da fitar sautin sassanyan murmushin nata. Kowanne tsiga na jikinsa sai ta shiga tashi

"Ka sani ko yanayin alaqa da dangantakarmu ne suka dauko hanyar sauyawa?"

"Da gaske!" Ya fada da wani irin murna daya kasa boyuwa yana fidda idanunsa waje

"Eh mana....." Ta amsa masa a taqaice.

"Yes!" Ya sake fadi da wani irin dadi yana mamayarsa

"Indai haka ne kiyimin proving mana......"

"Kamar?" Ta jefa masa tambayar da zazzaqar muryartan nan,don wajen da takeso azo kenan tana tunanin kuma ana gab da zuwa din,saidai ita ba zata iya requesting ba har sai ya nema da kanshi

"Mu hadu yau.......don Allah kada kicemin aah". Shuru tayi cikin salon jan aji,kaman bataso

"Please mana.....please,kice to" Ya fadi murya a raunane cike da fatan samun amincewarta

"Shikenan"

"Oh god......" Ya sake fadi yana dukan kujera da hannunsa,yana kuma ji duk duniya ba wani d'a namiji da yakaishi sa'a yau dai a duniya. Yana nashi bidirin amma nata qasan zuciyar a quntace. Wani mugun tsanarshi take ji da haushinsa. Da gaske wannan din dabi'arsa ce bazai kuma taba canzawa ba,ko shin mata nawa ya lalata da kalar wannan mummunar dabi'ar tasa?.

"Bansan da wanne irin yare zan gode miki ba....amma zakiga godiya a aikace har saikin rasa da meye zaki maye min gurbin hidimata a gareki......tabbas zan ninka darajarki.....zan daukaka martabarki a idanun duniya......zan maidake tauraruwa cikin mata....zan miki ado da gold irin adon da sai 'yar gata...."

"Thank you......thanks" Kawai tace dashi don tanaso ya dakata daga zubo wannan dogon sharhin nasa. Tana tausaya masa a daren yau irin barnar da zatayi masa,ta tabbatar wadannan maganganun da yake jerowa a yanzu saisun koma sumbatu.

"Zan shiga company akwai lissafin da zamuyi da boss dina.....duk inda la'asar yayi koda bamu gama ba zan dauki excuse......zan kama mana daki a Bristol,zan tura miki details da komai da komai".

Baki ta tabe tana jin wani haushi yana cikata. A daren yau bashi ba,hatta da boss din nasa saita sakasu a lissafin da babu fita. Tanaji a jikinsa ma shi da boss din basa zaiyi wahala idan ba zamuje ta tadda muje mu ba. A yadda yakan bata labarinsa lokaci bayan lokaci......irin kudaden da yake wasa dasu da kuma shekarunsa talatin da bakwai a duniya amma ace ba macen aure?,to idan ba sheqe ayarsa yakeyi ba me yakeyi kenan?.

Ture wannan tunanin tayi daga zuciyarta don a halin yanzu bashi da amfani,abu guda daya ta sani ba sassauci,kuma a yau din takeso mika'il ya zama tarihi cikin rayuwarta,shi kuma ta bashi darasin da zai sanya rayuwarsa tayi laushi da kyau.

"Ba laifi...." Ta amsa mass,bata kuma jira cewarsa ba ta dora

"Ina fata kasan rule din.....zaka rigani isa gurin da wasu mintuna......kuma bana buqatar kowa yasan muna tare ne da kai"

"Dukka dokoki da qa'idojinki kisa a ranki an gamasu......ranki ya dade.....da zaki bani dama da kin fadi inda zan aiko driver ya daukomin ke.....don bana buqatar kiyi wahala" . Wani sirrintaccen murmushi ta saki

"Na maka uzuri saboda baka jima cikin rayuwata ba bare ka fahimci wacece ni......zanzo da kaina,bana buqatar kowanne driver"

"As you wish.....saidai zan saka kudin transportation.......please karkice min aah" Idanunta ta lumshe sannan ta budesu,har ta fara gajiya da dogon hirarsa

"Alright....byee" Ta furta a taqaice tana tsinke wayar.

Ajiyeta tayi gefe tana furzar da iska daga bakinta. Inda ace dukka haka mazan aure suke ba shakka a jiya da kunnuwanta basu jiye mata abinda taji ba saman dogon layin masu lalurar ciwon zuciya dake dakon ganin likita......tabbas da idanunta basu gane matan auren da hawan jinin bacin rai da baqincikin d'a namiji ya jefa musu hawan jinin daya juye musu zuwa ciwon zuciya ba......da bataga matar data yanke jiki a wajen ta fadi ba......wadda daga qarshenta gawarta aka fitar a asibitin 'yaruwata na kuka dukka sanadin baqinciki namiji.

Ita kuwa me zatayi da aure?......wanne tsautsayi ne zai kaita damqa rayuwarta hannun d'a namiji guda daya yayita hajijiya da rayuwarta ba gaira ba dalili?.

Abubuwan data gani din dasu ta kwana,su suka yita yiwa kunnuwa da idanuwanta gizo,kuma suka hanata komawa duba ayshatu.....suka kuma sanyata jin ta matsu ta kora mika'il mashkur harma da ya'aqoub din daga rayuwarta gaba daya.
Chapter 66 · 0% Book details