← Book details Duniya Ta Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 25 OF 80

Sashe 25

Duniya Ta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Connection" Ta fada a gajarce

" A daren nan?"

"Haka abun yazo,mashkur......mashkur alqali abdulkreem"

"Done.......wancan aikin ya kusa kammala......akwai ragowar information dana kasa accessing.....but...."

"Karka damu.....mu sanya wancan a mala.....wannan din shine yafi muhimmanci a yanzu"

"An gama.....bani code......let me write it" Ya fada yana dan riqe wayar kadan kafin yace

"Okay.....karanto" A nutse ta karanta masa wasi gajerun lambobi guda uku sannan ta katse kiran. Ta jawo locker madubinta ta ciro Bluetooth tayi danne danne saman wayar tata ta bada wasu sakanni sannan ta maqala a kunnenta. Saita aje wayar,ta dauki wancan Samsung din ta kunnata sannan ta fara yunqurin kira.

Bugu daya tak tayi aka daga,ta kalli wayar da mamaki sanda yake cewa

"Am ready to go princess......ina zaune a mota nida driver a parking lot na gida"

"Yayi.....but if possible ka taho kai daya mana"

"An gama" Ya amsa mata cikin farinciki hankali kwance.

Tana kammala saka takalma huda na shigowa dakin. Kallo daya tak tayi mata taga yanayinta ya sauya. Hudan tadan ritsata da idanu tana dubanta,saidai tun kafin takai ga tambayarta ta bata amsa

"Zan dan fita kadan amma yanzu zan dawo" Iya abinda ta gaya mata kenan ta fara takawa zata fice.

A jikinta taji yarinyar kallonta take,a jikinta taji tana tsaye ne kawai har yanzu,don haka ta tsaya cak sannan ta waiwayo. Ido suka hada,sai a sannan hudan ta kauda kanta. Iya hakan ya gayawa Sabreen maganganune sosai cikin zuciyarta,wataqila girma da kimarta kadai zai hanata ta furta mata su. Taku hudu tayi ta iso gaban hudan

"Dole ce ta saka zan fita huda......amma bazan wuce awa daya ba,idan na dade biyu"

"Amma anty...." Hudan ta furta fuskarta fal damuwa.

Yatsanta ta dora saman lips tana duban hudan,sai kuma daga bisani ta dauke yatsan tana aza dukka hannuwanta saman kafadarta,ta kuma zaunar da ita saman stool na madubin dakin

"Ke daya ce tal cikin mutanen da sukasan wace Sabreen gaba daya baya,kada kiyi tunanin na canza......ban canza ba huda.....kuma har abada bazan canza ba.....nayi alqawari......mommu da abba dake qarqashin qasa bazan bari suyi kaico dani ba" Kai ta gyada a hankali tana kallon Sabreen kamar yadda itama ita din take kallo. To amma a hankali tana rasa wannan yardar wanda tasirin maganganu daga kowanne saqo da lungu na layinsu dama unguwarsu ke kai kawo a kunnuwanta

"Don't lose hope huda......alqawari na.....bazan karyashi ba,ki kula da nadra da haneefa" Ta fadi mata daga qarshe ta juya tana fita a dakin. Nata ruhin yana motsuwa.

Har abada ba zata daina zargin maraici ba......har abada ba zata daina kuka dashi ba......a wani sashen na duniya,a irin wannan lokacin,diya kamarta tana qarqashin kulawar mahaifanta ne guda biyu.......ko kuma qarqashin kulawar wasu amintattun mutane da zasu zame mata makwafin iyayen.......sai gashi tata DUNIYAR ba haka bane,dukka kafadunta dauke suke da wani irin nauyi dakeson fin qarfinta ya kaita qas.

Daga baya baya ta sanya busari ya ajeta kafin akai ga shiga gurin a yanayi salo na kula da takunta kanta dama dukka wani motsi nata.

Sallamar busari tayi tace zata nemeshi idan hakan ta taso,sannan ta fara takawa a hankali tana nufar wajen.

A hankali take ratsa wajen cikin nutsuwa data zame mata dabia,tana takawa a hankali qamshinta da kuma yadda shigar ta amsheta kadai suka soma jan hankulan matasa da yawa wajen. Guri ne da yakan hada matasa maza da mata,wayayyu da suke da gogewa a fannin rayuwa kudi da kuma ilimi. Wajene kebantacce da yawansu suka maidashi gurin nishadi da kuma debe kewarsu,wasunsu a duk daren duniya,wasu kuma jifa jifa.

Yadda take daukan hankulansu haka kwarjininta ke dukansu,wannan ya sanya duk wani dakeson kawo mata caffa ya gaza yin hakan,saidai tazo ta ratsashi ta wuce shi kuma ya bita da kallo.

Tun daga nesa ta hangeshi,ya fita yayi tsaf cikin wani lafiyayyen jeans da shirt da suka dace da takalmin qafarsa. Kanshi pcap ce daya sauko da ita tadan rufe masa fuska. Hannunsa dauke da wayarsa yana latsawa a hankali ba tare daya damu da abinda ke kai kawo a wajen ba.

Ta sani,hankalin gomayyar 'yan mata dake wajen tabbas suna kanshi. Mashkur din ba irin mazan da mace me muradin jinsin maza irinsu zata kall sau daya bane ta iya kauda kai kota wofantar,kusan zata iya cewa ya hada dukkan komai,abubuwa da dama da mazan da suka taba ratsa rayuwarta ba wanda ya gama cikasu irin haka. Yana da kyau daidai gwargwado wanda kudi suka sake qawatashi,yayi karatu har zuwa matakin degree,hakanan dan wulaqanci ne shi,wulaqancin daya zame masa ado a idanun mata marasa kamun kai. Idanunsa a bude suke tarwai,yana da wata irin wayewa data zarta shekaru da kuma iliminsa,wanda hakan baya rasa nasaba da fita qasashen waje da yake yawan yi,musamman qasashen turawa.

Dab da zata iskeshi ya daga kansa sai suka hada ido. Zumbur ya miqe yana zube mata idonshi,har cikin zuciyarsa yana jin wani abu daya qarasa mamaye gangar jikinsa.

Karon farko daya soma jin ra'ayinsa akan mace na neman canzawa. A yanzun kallo daya tak.....cikin qasa da minti daya kacal ya soma ji a ransa kamar ya aureta shine abinda yafi dacewa dashi da ita gaba daya. Kamar alaqar daya shirya da dangantakar daya shirya ginawa a tsakaninsu ba ita ta dace ba,duk da har yanzu gaza fuskantar AINIHINTA....a wanne mataki na 'yammatan wannan zamanin take?. Wasu abubuwan nata na masa kama da dabi'un mace ta musamman.....amma wani motsin nata a wani lokacin sai ya sanya masa shakku akan haka. Kamar dai yanzun,yadda duk da duhun dare ya lullube sararin subhanana amma hakan bai dasa mata shakku ko ya zama dalilin qin fitowa su hadu ba.

A maimakon kujerar daya ja mata don ta zauna saita matsa kujera ta gaba,saidai kuma fuskarta a sake tana maida masa martanin murmushinsa.

*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*

*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*

*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*

*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*

*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*

*ZAFAFA BIYAR*

*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*

*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*

_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_

_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_

_K'ALBIM Mamuhghee_

_AJIYA A DUHU Billynabdul_

_DUNIYATA Huguma_

_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_

*hudu 2k*

*uku 1500*

*Biyu 1k*

*Daya 500*

_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_

*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*

*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*

*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*

*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*

*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*

*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*🇳🇪🇳🇪

89825722
Nousaiba lawali maradi
1000cf

*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*

*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*🥰🥰
*D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

*Arewabooks:@Huguma*

https://www.arewabooks.com/book?id=675041625c3130f457519997

PAGE 27
_________________________
*_ALBISHIR A GAREKU!!_*

*_SHIN KUNSAN UMMUMAHNOOR LUXURIES TA TANADAR MUKU INGANTATTUN KAYAN ADO NA FITA KUNYA KUWA?_*

*_KAMAR SU_*

Atamfofi
Laces
Shadda
Materials
Takalma
Jakunkuna
Mayafai
Trolley
Sarka da dan kunne
Oil perfumes

*_karki tsaya sanya har ayi babu ke,maza garzaya ta nan_*

Numbers
08034469681
08135142610

Handles
Instagram @ummu_mahnoor_luxuries
TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries
Facebook ummu_mahnoor_luxuries

*_inganci da kwalliya shine muradinmu_*
_________________________

Duk da a qasan zuciyarta ba haka bane.

Idanunsa a kanta kaman bazai iya daina kallonta ba yana nashi seat din ya zauna

"Finally dai after wasu watanni......har na debe tsammani sai gashi......" Ya fada yana dan watsa hannayensa irin na gogaggun samari

"Me ma bahaushe yake cewa?.....me haquri ko?" Ya aza mata nauyin amsa tambayar ta hanyar kallonta da idanunsa.

Qaramin murmushi kawai ta saki tana maida bayanta ta jingina sosai da kujerar da take kai din,yayin data daba hankalinta gida biyu. Wani a gurinsa,wani kuma yana kan yanayin wajen dake cike da 'ya'ya mata. Tayi imanin dukkaninsu uwaye ne suka haifesu,koda ace akwai na gaba da fatiha to kadanne. Son rai son zuciya kwadayi su sukayi musu jagora zuwa ga turbar da suke kai a yanzu?. Ko kuma suma kamar ita dinne?.

"Yauwa......thanks" Taji ya furta,saita maido dubanta kanshi.

Idanu ya kashe mata cikin salon jan hankali me zafi,ya kuma sake matsowa sosai har yana rungumar table din da suke kai zuwa qirjinsa,sannan ya aje manual din da aka kawo ta hannun waitress.

"Choose babe" Ya fadi yana lanqwashe murya kamar wani mace gami da kanne mata idanu. Manual din da ya tura mata ta sauke idanu a kai. Tarin abinciccika ne iri daban daban,wanda ko kaffara ba zatayi ba idan ta qiyasta maqudan kudaden da za'a lasa ta sanadiyyar cinsu. Sai data qare musu kallo gaba da baya,yayin da shi da waitress din ke jiransa ba tare da sun qosa ba,saita maida ta ajiye saman table din. Ta motsa bakinta zatayi magana kenan sallamar da akayi da wata raunanniyar muryar taja hankalansu.

Dukkansu shi da ita suka maida dubansu ga wajen. Matashiya ce mai matsakaicin haske wadda idan ka kalleta a qiyasin da zaka fara yi mata duka duka shekarunta ba zasu haura ashirin da bakwai zuwa da takwas ba da haihuwa. Sanye take fallen zanin atamfa da kai tsaye zaka kirata da atamfa leda ko roba,duba da yadda ta cukuikuye a jikinta saboda tsufa da rashin quality da kuma yanayi na dan busawar iska data hadu dashi. Qasan zanin a cinye yake abinda zai wassafa maka kenan shekarun da atamfar ta dauka a duniya ana amfanarta. Hijabi ne a jikinta daya fara gajiya da rayuwa,tsananin sussuqewarsa ya sanya ya baiwa me kallo daman hango yaloluwar rigar dake a jikinta.

"Ke kuma fa?,daga ina wa kike nema?" Mashkur dake dubanta sama da qasa da wani irin qasqantaccen kallo ya jefa mata tambayar.

Rusunawa qasa tayi cikin matuqar taushi da karyar dakai ta hade hannuwanta biyu waje daya

"Taimako nake buqata yallabai......don Allah ka taimaka min da duk abinda Allah......"

"Wait.....wait mana" Ya fada a tsawace har hakan ya sanyata miqewa ta tsaya saman qafafunta. Waiwayawa yayi zuwa ga waitress din

"Yaushe wajen nan naku ya lalace?,yaushe kuka fara bawa mutane irin wadannan daman shigowa gurin nan.....wait.....wai bakusan kowa na zuwa irin nan bane don ya huta ya kuma yi uzurin gabanshi ba tare da kowa da komai yayi disturbing nashi ba?".
Chapter 25 · 0% Book details