Sashe 28
Duniya Ta Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_
*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*
*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*
*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*
*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*
*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*
*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*🇳🇪🇳🇪
89825722
Nousaiba lawali maradi
1000cf
*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*
*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*🥰🥰
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
*Arewabooks:@Huguma*
https://www.arewabooks.com/book?id=675041625c3130f457519997
PAGE 29
*SOUTH KOREA*
*_THE CAPITAL OF SOUTH KOREA (SEOUL)_*
*_Yanghwa-ro to hongdae geori_*
Yanghwa-ro daya daga cikin lafiyayyun street dake da wani irin daddaden yanayi a kowacce safiya cikin anguwar hongdae dake tsakiyar south Korea. Yanayi ne me me dadi dake wanzuwa a kowacce safiya cikin street din dake da wani irin shuru da nutsuwa gami da nisanta da kowacce irin hayaniya daka iya damun ruhi ko matsantawa nutsuwar dan adam.
Ga duk ma'a bocin fitowa da sassafe tsakanin yanghwa-ro zuwa hongdae geori zai zame masa abu me wahala baisan baqin fuskar matasan Nigerians din guda biyu ba. Zaratan matasa masu wani irin kyan zubi na halitta da kuma ajiyayyen kwarjini da kuma haiba. Yaya da qaninsa wanda fitowa jogging kusan kowaccw safiya ya zame musu kamar al'ada.
Muhammed FU'AD,da kuma musaddiq hamza kibiya wanda yake daga gefan Muhammed FU'AD din. Idan yayi kamar zasu daidaita wajen sassarfa me kama da gudun da sukeyi sai ya zame har sai FU'AD din ya wuceshi yana fadin
"Eheennn......don't stop.....don't stop" Da wata iriyar husky voice da Allah ya huwace masa wadda ke cakude da nishi kadan na gudun da suka dauko.
Yayi kaman zai tsaya din ya kusa sau biyar......hakanan shima yake zaburar tashi har zuwa sanda suka iso daidai wani guri. Guri ne da kusan kowacce unguwa take da nata wanda aka tanadeshi aka killaceshi domin hutawar jamaar unguwar cikin wasu kujeru da shimfidaddun tsirrai da suka wadatu da tsafta suke kuma samun kulawa yadda ya kamata.
Ruku'u musaddiq yayi yana cakewa a wajen,ya kama gwiwoyinsa da hannunsa yana sauke nishin wahala gumi yana fita daga sumarsa zuwa goshinsa.
"Oh shit" FU'AD ya fada yana jan birki,sannan yayi reverse yayo kwana da hanzari yana dawowa daidai inda musaddiq ya cake.
Baice masa komai ba ya kama wuyansa ya cafka yana tadashi tsaye sosai saman qafafunsa,abinda ya sanyashi sakin wata qaramar qara yana matse kafadunsa
"Sorry hamma......am really tired wallahi......i try hamma......kusan minti talatin tunda muka fito muke wannan gudun.....ko doki hamma sai haka"
"Shut your mouth.......malalaci kawai......da wanna halin da dabi'ar naku meye marabarku da mata?,inajin mun kusa baku jilban da dankwali kuna daurawa ko?". Sosai dariya taso murqushe musaddiq,amma yasan bai isa ya yita a gabansa ba. Duk wani training nasa suna shanyewa amma yanzun don ya gaza cikashe mintunan gudunsa shine ya zama malalaci har zasu fara dauka zani?.
Zanin da ya sake tunawa ya sanya dariyar da yake boyewa ta qwace masa da gaske,don ba wanda ya hango daure da zani sai saddiq.
Sakin qeyar nashi FU'AD yayi yana watsa masa wani irin kallo da lumsassun idanunsa dake da wani irin kaifaffen kallo me kashe duk wani zarra ta mutum
"Are you laughing?,da gaske baka gaji ba......zamu qarasa gida a haka,ko sau daya kuma ka sake tsayawa kasan sauran......salary dinka na wannan watan zan saka abba yayi sadakarshi" Ya fada yana gyara doguwar socks din qafarshi daya rufe mass har gwiwarsa. Kayan motsa jiki ne a jikinsa,amma yadda sukyi masa kyau zata tsammaci ya sanyasu ne don ado. Sun fidda duk wata qirar qarfi da Allah ya bashi,murdaddun muscles dinsa zuwa shaffen cikinsa da qirjin yafi cikin dagowa.
"Hamma......wallahi Allah ba abinda kake tunani bane" Ya fada cikin karya wuya da sanyaya murya
"......Allah hamma kawai musaddiq na hango daure da zani da dankwali......" Sai ya qarasa fadi yana bushewa da dariyar data sanyashi ya murmusa dole. Dariya yake sosai yana kuma kallon fuskar fu'ad din.
"Iyakarshi kenan" Ya furta a ransa. Murmushi shine maqurar dariya a wajensa ko yaya kuwa abu yakai. Kai ya girgiza kawai qasan ransa yana tuno wasu abubuwa na sadiq da musaddiq din. Suna da wani irin wasan da inda ace shima irin farouq ne baya jin yaran zasu shuka abun arziqi idan ba shiririta ba. Har kullum abba na jin dadin jajircewarsa a kansu,don shima din sun maidashi kakansu qarfi da yaji,yayita masifa yayita masifa amma a banza,maganae mutum guda ce take ratsasu.....zancan mutum daya ne yake zama daram saman kansu shine zancan muhammad fu'ad.
Bai sake ce masa komai ba sai ya miqe yana zaro wayarsa dake aljihun wandonsa. Iphone 16 sabuwar qira wanda babban hoton wata kyakkyawar matashiya ya mamaye ilahirin fuskar wayar. Kyakkyawar bafulatana me wani sassanyan kyau,cikin kamilalliyar shiga data qarawa hoton da Fuskarta kwarjini. Dududu shekarunta da suka nuna cikin idanunta da kuma fuskarta goma sha takwas ne.....sha takwas din da aka soma gangarawa cikin sha tara.
Kalmomin sirri ya sanya ya bude wayar,sannan kai tsaye ya tafi zuwa ajiyayyun lambobin da basu da yawa cikin wayar. Akan wata number dake dauke da sunan ABBA NA ya tsaya,ya danna kira sannan ya maidata aljihunsa yana gyara zaman Bluetooth guda daya dake manne a kunnensa yana bada hasken qyallin wuta time to time. Sai kuma ya fara takawa a hankali ba tare daya cewa musaddiq komai ba,wannan ya bawa musaddiq din daman biyo bayansa a nutse can qasan ransa yana murnar yadda aka haqura da jogging dinnan haka.
"Shi ya dauka kowa kamarshi ne me jikin qarfe da baya gajiya da motsa jiki......idan na hada qarfi ina zan kaishi" Yayi gulmarsa a ransa yana biye dashi tare da qare ma bayansa kallo.
Shi kansa yadda yake da ginannun muscles yana burgeshi yana kuma bashi sha'awa,amma bashi da juriya da qarfin halin da zai building muscles ma jikinsa kamar nashi.
"Abba ka farka?" Ya fada cikin matuqar nuna kulawa bayan yayi masa sallama.
"Okay gamu nan qarasowa" Sai ya katse kiran ta jikin Bluetooth din nasa sannna ya dan soma sassarfa yana cewa musaddiq
"Oya.... Mu qarasa gida" Kaman zaiyi kuka hakanan ya taka ya soma bin bayansa. Kafin su qarasa gidan sai da yaji kaman zai zube,cikin ransa yake ganin gaskiyar sadiq ashe da yakanyi ciwo ko ya qirqiro uzurin qarya duk sanda ya tasheshi ya rakashi jogging. Har gwara ku shiga gym room dashi,wannan idan suka faki idonshi sai su zabi machine daya su haye su kasheshi ko su rage gudunsa sosai.
A hankali suka qarasa hongdae geori cikij estate din dake unguwar. Gida me lamba ashirin,yayi tsaye yana danna bell yayin da qirjinsa ke dagawa sama da qasa yana fidda Zazzafan huci daga bakinsa. Ya jiqe sharkaf da gumi,musaddiq kuwa tuni ya zube saman step biyu dake bakin qofar gidan yana numfashi da sauri da sauri.
A hankali qofar ta bude,dattijon mutumin nan Alhaji hamza kibiya ya bayyana cikin wata lallausa kuma kyakkyawar abayar qasar morocco ruwan zuma. Ba abinda ya sauya tattare dashi sai shekaru da suka fara bayyana kansu a jikinsa.....bayyana ba me muni ba saboda daular rayuwa da kuma jin dadin da yake ciki daya zarta ya kuma ninka na shekarun baya ta hannun zaratan yaransa guda hudu dukka maza.
Da murmushi a fuskarsa kamar kullum yake kallonsa
"Ina dayan me babban suna?" Alhaji hamza ya tambaya saboda idanunshi basu hango musaddiq ba sam sam.
Da baki ya yiwa abba cunensa,abban ya dora hannu saman baki yana bushewa da dariya
"Kai......taso dalla.....dama babu me maganinku ai sai me babban suna......tashi nace mace kawai.....koni nan da shekaru suka fara turamin ina gudun nan,kuma ka gani da idanunka.....ina zakuyi qwarin damu uwayenku mukayi?,baku da aiki sai hawa mota sai ciye ciye da shaye shayen banza" Abban ya fada yana wurga hannu. Kai ya daga da qyar yana duban abban
"Abba wallahi.....bazan iya tashi ba da gaske,qafafuna kamar zasu tsinke.....gudun fanfalaqi yau hamma ya saka mukayi" Yadda yace gudun fanfalaqin ya tilastawa abba sakin dariya,yayin da FU'AD ya girgiza kai kawai. Suna ganin iskanci a gidan wajen sadiq da musaddiq,kullum kaman basa girma,kullum kallon kansu sukeyi kaman qananun yara.
"Tunda ba zaka tashi ba ai idan wancan qadangare ya shige maka riga ai ka nema hanyar gida" Wani mugun tsalle ya doka sai gashi a tsaye kyam
"Yauwa.....dan nema ja'iri,zo ka wuce kaji me babban suna" Abban ya fadi yana komawa ciki fuad yabi bayansa yana dariya qasan ranshi. Har yanzun musaddiq yana tsoron qadangare kenan tun yarinta?,abun ya dinga bashi mamaki don shi baiga wani abun tsoro a qadangare ba.
Suna shiga yana biyo bayansu yana dube dube yana fadin
"Wallahi abba ka kusa sakani na saki fitsari a wando......yanzu inda a gaban nasreen......" Tsaf ya kame bakinsa ba tare daya qarasa ba saboda kallon da FU'AD ya jefeshi dashi,ya sosa kanshi ya sauya akalarsa zuwa kitchen da kake iya hangensa tarwai ta falon.
Saman kujera ya zauna a nutse yana warware takalman qafarsa,abban ma ya koma inda ya tashi ya zauna yana daukar mug tare da ci gaba da kurbar zazzafan tea din dake ciki.
"Sannu da gida abba" Ya sake fada yana dan jingina bayansa da kujera
*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*
*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*
*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*
*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*
*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*
*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*🇳🇪🇳🇪
89825722
Nousaiba lawali maradi
1000cf
*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*
*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*🥰🥰
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
*Arewabooks:@Huguma*
https://www.arewabooks.com/book?id=675041625c3130f457519997
PAGE 29
*SOUTH KOREA*
*_THE CAPITAL OF SOUTH KOREA (SEOUL)_*
*_Yanghwa-ro to hongdae geori_*
Yanghwa-ro daya daga cikin lafiyayyun street dake da wani irin daddaden yanayi a kowacce safiya cikin anguwar hongdae dake tsakiyar south Korea. Yanayi ne me me dadi dake wanzuwa a kowacce safiya cikin street din dake da wani irin shuru da nutsuwa gami da nisanta da kowacce irin hayaniya daka iya damun ruhi ko matsantawa nutsuwar dan adam.
Ga duk ma'a bocin fitowa da sassafe tsakanin yanghwa-ro zuwa hongdae geori zai zame masa abu me wahala baisan baqin fuskar matasan Nigerians din guda biyu ba. Zaratan matasa masu wani irin kyan zubi na halitta da kuma ajiyayyen kwarjini da kuma haiba. Yaya da qaninsa wanda fitowa jogging kusan kowaccw safiya ya zame musu kamar al'ada.
Muhammed FU'AD,da kuma musaddiq hamza kibiya wanda yake daga gefan Muhammed FU'AD din. Idan yayi kamar zasu daidaita wajen sassarfa me kama da gudun da sukeyi sai ya zame har sai FU'AD din ya wuceshi yana fadin
"Eheennn......don't stop.....don't stop" Da wata iriyar husky voice da Allah ya huwace masa wadda ke cakude da nishi kadan na gudun da suka dauko.
Yayi kaman zai tsaya din ya kusa sau biyar......hakanan shima yake zaburar tashi har zuwa sanda suka iso daidai wani guri. Guri ne da kusan kowacce unguwa take da nata wanda aka tanadeshi aka killaceshi domin hutawar jamaar unguwar cikin wasu kujeru da shimfidaddun tsirrai da suka wadatu da tsafta suke kuma samun kulawa yadda ya kamata.
Ruku'u musaddiq yayi yana cakewa a wajen,ya kama gwiwoyinsa da hannunsa yana sauke nishin wahala gumi yana fita daga sumarsa zuwa goshinsa.
"Oh shit" FU'AD ya fada yana jan birki,sannan yayi reverse yayo kwana da hanzari yana dawowa daidai inda musaddiq ya cake.
Baice masa komai ba ya kama wuyansa ya cafka yana tadashi tsaye sosai saman qafafunsa,abinda ya sanyashi sakin wata qaramar qara yana matse kafadunsa
"Sorry hamma......am really tired wallahi......i try hamma......kusan minti talatin tunda muka fito muke wannan gudun.....ko doki hamma sai haka"
"Shut your mouth.......malalaci kawai......da wanna halin da dabi'ar naku meye marabarku da mata?,inajin mun kusa baku jilban da dankwali kuna daurawa ko?". Sosai dariya taso murqushe musaddiq,amma yasan bai isa ya yita a gabansa ba. Duk wani training nasa suna shanyewa amma yanzun don ya gaza cikashe mintunan gudunsa shine ya zama malalaci har zasu fara dauka zani?.
Zanin da ya sake tunawa ya sanya dariyar da yake boyewa ta qwace masa da gaske,don ba wanda ya hango daure da zani sai saddiq.
Sakin qeyar nashi FU'AD yayi yana watsa masa wani irin kallo da lumsassun idanunsa dake da wani irin kaifaffen kallo me kashe duk wani zarra ta mutum
"Are you laughing?,da gaske baka gaji ba......zamu qarasa gida a haka,ko sau daya kuma ka sake tsayawa kasan sauran......salary dinka na wannan watan zan saka abba yayi sadakarshi" Ya fada yana gyara doguwar socks din qafarshi daya rufe mass har gwiwarsa. Kayan motsa jiki ne a jikinsa,amma yadda sukyi masa kyau zata tsammaci ya sanyasu ne don ado. Sun fidda duk wata qirar qarfi da Allah ya bashi,murdaddun muscles dinsa zuwa shaffen cikinsa da qirjin yafi cikin dagowa.
"Hamma......wallahi Allah ba abinda kake tunani bane" Ya fada cikin karya wuya da sanyaya murya
"......Allah hamma kawai musaddiq na hango daure da zani da dankwali......" Sai ya qarasa fadi yana bushewa da dariyar data sanyashi ya murmusa dole. Dariya yake sosai yana kuma kallon fuskar fu'ad din.
"Iyakarshi kenan" Ya furta a ransa. Murmushi shine maqurar dariya a wajensa ko yaya kuwa abu yakai. Kai ya girgiza kawai qasan ransa yana tuno wasu abubuwa na sadiq da musaddiq din. Suna da wani irin wasan da inda ace shima irin farouq ne baya jin yaran zasu shuka abun arziqi idan ba shiririta ba. Har kullum abba na jin dadin jajircewarsa a kansu,don shima din sun maidashi kakansu qarfi da yaji,yayita masifa yayita masifa amma a banza,maganae mutum guda ce take ratsasu.....zancan mutum daya ne yake zama daram saman kansu shine zancan muhammad fu'ad.
Bai sake ce masa komai ba sai ya miqe yana zaro wayarsa dake aljihun wandonsa. Iphone 16 sabuwar qira wanda babban hoton wata kyakkyawar matashiya ya mamaye ilahirin fuskar wayar. Kyakkyawar bafulatana me wani sassanyan kyau,cikin kamilalliyar shiga data qarawa hoton da Fuskarta kwarjini. Dududu shekarunta da suka nuna cikin idanunta da kuma fuskarta goma sha takwas ne.....sha takwas din da aka soma gangarawa cikin sha tara.
Kalmomin sirri ya sanya ya bude wayar,sannan kai tsaye ya tafi zuwa ajiyayyun lambobin da basu da yawa cikin wayar. Akan wata number dake dauke da sunan ABBA NA ya tsaya,ya danna kira sannan ya maidata aljihunsa yana gyara zaman Bluetooth guda daya dake manne a kunnensa yana bada hasken qyallin wuta time to time. Sai kuma ya fara takawa a hankali ba tare daya cewa musaddiq komai ba,wannan ya bawa musaddiq din daman biyo bayansa a nutse can qasan ransa yana murnar yadda aka haqura da jogging dinnan haka.
"Shi ya dauka kowa kamarshi ne me jikin qarfe da baya gajiya da motsa jiki......idan na hada qarfi ina zan kaishi" Yayi gulmarsa a ransa yana biye dashi tare da qare ma bayansa kallo.
Shi kansa yadda yake da ginannun muscles yana burgeshi yana kuma bashi sha'awa,amma bashi da juriya da qarfin halin da zai building muscles ma jikinsa kamar nashi.
"Abba ka farka?" Ya fada cikin matuqar nuna kulawa bayan yayi masa sallama.
"Okay gamu nan qarasowa" Sai ya katse kiran ta jikin Bluetooth din nasa sannna ya dan soma sassarfa yana cewa musaddiq
"Oya.... Mu qarasa gida" Kaman zaiyi kuka hakanan ya taka ya soma bin bayansa. Kafin su qarasa gidan sai da yaji kaman zai zube,cikin ransa yake ganin gaskiyar sadiq ashe da yakanyi ciwo ko ya qirqiro uzurin qarya duk sanda ya tasheshi ya rakashi jogging. Har gwara ku shiga gym room dashi,wannan idan suka faki idonshi sai su zabi machine daya su haye su kasheshi ko su rage gudunsa sosai.
A hankali suka qarasa hongdae geori cikij estate din dake unguwar. Gida me lamba ashirin,yayi tsaye yana danna bell yayin da qirjinsa ke dagawa sama da qasa yana fidda Zazzafan huci daga bakinsa. Ya jiqe sharkaf da gumi,musaddiq kuwa tuni ya zube saman step biyu dake bakin qofar gidan yana numfashi da sauri da sauri.
A hankali qofar ta bude,dattijon mutumin nan Alhaji hamza kibiya ya bayyana cikin wata lallausa kuma kyakkyawar abayar qasar morocco ruwan zuma. Ba abinda ya sauya tattare dashi sai shekaru da suka fara bayyana kansu a jikinsa.....bayyana ba me muni ba saboda daular rayuwa da kuma jin dadin da yake ciki daya zarta ya kuma ninka na shekarun baya ta hannun zaratan yaransa guda hudu dukka maza.
Da murmushi a fuskarsa kamar kullum yake kallonsa
"Ina dayan me babban suna?" Alhaji hamza ya tambaya saboda idanunshi basu hango musaddiq ba sam sam.
Da baki ya yiwa abba cunensa,abban ya dora hannu saman baki yana bushewa da dariya
"Kai......taso dalla.....dama babu me maganinku ai sai me babban suna......tashi nace mace kawai.....koni nan da shekaru suka fara turamin ina gudun nan,kuma ka gani da idanunka.....ina zakuyi qwarin damu uwayenku mukayi?,baku da aiki sai hawa mota sai ciye ciye da shaye shayen banza" Abban ya fada yana wurga hannu. Kai ya daga da qyar yana duban abban
"Abba wallahi.....bazan iya tashi ba da gaske,qafafuna kamar zasu tsinke.....gudun fanfalaqi yau hamma ya saka mukayi" Yadda yace gudun fanfalaqin ya tilastawa abba sakin dariya,yayin da FU'AD ya girgiza kai kawai. Suna ganin iskanci a gidan wajen sadiq da musaddiq,kullum kaman basa girma,kullum kallon kansu sukeyi kaman qananun yara.
"Tunda ba zaka tashi ba ai idan wancan qadangare ya shige maka riga ai ka nema hanyar gida" Wani mugun tsalle ya doka sai gashi a tsaye kyam
"Yauwa.....dan nema ja'iri,zo ka wuce kaji me babban suna" Abban ya fadi yana komawa ciki fuad yabi bayansa yana dariya qasan ranshi. Har yanzun musaddiq yana tsoron qadangare kenan tun yarinta?,abun ya dinga bashi mamaki don shi baiga wani abun tsoro a qadangare ba.
Suna shiga yana biyo bayansu yana dube dube yana fadin
"Wallahi abba ka kusa sakani na saki fitsari a wando......yanzu inda a gaban nasreen......" Tsaf ya kame bakinsa ba tare daya qarasa ba saboda kallon da FU'AD ya jefeshi dashi,ya sosa kanshi ya sauya akalarsa zuwa kitchen da kake iya hangensa tarwai ta falon.
Saman kujera ya zauna a nutse yana warware takalman qafarsa,abban ma ya koma inda ya tashi ya zauna yana daukar mug tare da ci gaba da kurbar zazzafan tea din dake ciki.
"Sannu da gida abba" Ya sake fada yana dan jingina bayansa da kujera