Sashe 54
Duniya Ta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kai ta jinjina kawai tana dubanta,tana jin inama ace itace hajja?.....tana hasashen ranar da wannan damar zata samu a hannunta?.....tabbas saita sanya aminatu kuka da idanunta........sai ta sanya zuciyar aminatu da hamza sun buga da qasqancin da zasu gani daga yaran da su suka rainesu har suka zama abinda suka zama a yanzu
(Tabbas gaskiya ne da akace ka guji sharrin wanda ka kyautatawa.......me makon jin dadi kyakkyawan fata da kyakkyawan mu'amala ta shiga tsakaninsu da mutanen da suka maida mata 'ya'ya mutum.....amma ga nata salon sakamakon,Allah kayi mana tsari daga sharrin dukkan wani abu me sharri mutum ko aljan,me rai ko maras rai ameen ya hayyu ya qayyumu).
Bugu daya tak aka daga kiran da hajjan tayi,muryarsa ta fito tarwai yana gaidata. Cikin kulawa ta amsa masa sannan tace
"Kaga yahaya.......naje unguwa ne sai na sallami driver da xummar zan tuqo kaina na dawo gida......."
"Me yasa hajja?,ta yaya zakiyi tuqi da kanki?" Ya fada a tsananin firgice kaman wanda akace masa ta hallaka. Murmushin qasaita ta aje
"To ai yanzu ma gashi na kasa dawowa din da kaina duk kasala ta rufeni...."
"Bari na kira driver din ya dawo ya maidaki" Ya furta da hanzari
"Kaga dakata.....wanne irin driver?" Ta fada tana bata rai
"Yi haquri hajja,me kk so?" Ya sake fada a rikirkice
"Matarka nakeso ka turomin ita zata maidani......kace ta kirani na bata kwatancen inda nake yanzu haka ina jiranta......kada kuma ta batamin lokaci" Ta fada tana bata rai
"An gama" Ya fada zuciyarsa na rawa.
Ta rigashi ajiye wayar ta waiwaya tana kallon maamah cikin murmushi
"Kinsan matar da nace a kiramin?" Kai maamah ta girgiza tana shakkar yiwuwar wanzuwar umarmin da hajjan ta bada yanzu yanzu
"Matarsa ce......itace taso dagamin yatsa taso tayi fito na fito dani,a zatonta tana da malaman da xasuyi mata aiki fiye da nawa......tanaso ta mallaki yahaya ta mallakeni.....har na sanya ya saketa na sakashi ya dawo da ita don tazo taga iyakarta......taga iya mizanin nawa aikin.....don tazo ta banbance tsakanin aya da tsakuwa,ta sake kuma fahimtar da gaske fa shi ruwa ba sa'an kwando bane......ita kanta a yanzun sai yadda nace mata,duk dana fahimci kanta yana fusga wani lokaci kaman wasu abubuwan idan nayi mata tana jin ciwonsu,shi yasa nakeson na qarasa horata da kyau" Kai kawai maamah take jinjinawa,abun yayi mata da kyau.....salon kuma ya burgeta yahau mizani da gwargwado na abinda take hasashen shimfidawa kanta. DA FUAD DA MUSADDIQ DAMA MATAYEN DA ZASU AURA SU ZAMA QARQASHIN IKONTA. wannan shine cikakken iko da isar UWA. Ta fada a ranta
"Wannan shine cikakken iko da isa.....ki katange komai kaman yadda sanda kk sha wahalar komai din ke daya kk sha" Hajja ta fada tana jinjina kai
"Indai ni na haifi fuad ya zama tilas ya fidda kudaden nan ya bani.....zan motsa masa qwanjina.....zan kuma banbance masa uwa da mahaifiya a wannan lokaci karo na farko" Maamah ta sake fada a ranta.
Ya jima riqe da wayar bayan gama waya da mahaifiyar tasa yana juya wayar a hannunsa. Sassa biyu na zuciyarsa kowanne na qalubalantar dan uwansa.
"Tayi daidai,ko mutuwa hajja tace muyi daidai ne......ai ta isa....girmanta yana da yawa,to laifin me ma tayi?,koni ta kira zuwa zanyi bare matata,komai tayi a kowanne lokaci ko yanayi daidai yake" Daya sashen yake fadi,yayin da daya sashen zuciyarsa yake cewa
"Ta yaya tana tsaka da hidimar gida,ya tabbatar yanzu haka tana can tana yiwa hajjan girkin rana daya zama wajibi aka kowacce matar danta tayi mata shi kulli yaumin rana da dare ba fashi......(tsarin girkin abincin gidan tsarin girki ne na bai daya,duk da irin girma da wadatar gidan tukunya daya ake dafa abincin safe rana dana dare,raba girki ne a tsakanin faccaloli tamkar kishiyoyi,kowacce zatayi kwana biyu 'yar uwarta ta karba,hakanan a tattare a babban dining room dake dauke da family dining table akecin dukka abincin. A nata fadin don a tattala mata dukiyar 'ya'ya,kuma dukkansu zasu samu sauqin kashe kudi a gidajensu,tunda kome zaa siyo hadin gwiwa zaayi a kawo......amma kuma ta gefe daya.....tsabar nuna isa izza da mulki ne,da kuma dabarar karantar motsin kowa cikin gidan ba tare data shiga sashen kowa ba don ta tattaro kowa din waje daya.
A yanzun ya tabbatar tana can tana wannan hada hada.....bama wannan ba......fita haka katsam a lokaci guda ba shiri?. Wannan sashen dake hango masa rashin dacewar shine sashe mafi rauni a zuciyarsa,don haka wancan bangaren ya rinjayeshi ya danna mata kira kanshi tsaye.
Sanda maamah ta bude baki da zummar sake magana kira ya shigo wayar hajja. Ta daga wayar tana kalla,sai ta sake wani murmushi me sauti
"Naja'atu ce" Ta fada cikin nishadi,saita daga wayar tana sanyata a hands free
"Salamu Alaikum hajja......daddynsu arfat yace kina buqatar nazo daukarki......kina daidai ina?" Fuska ta tsuke tamkar ba itace ta gama dariya yanzu ba
"Ke banason hauka......haka akeyi daga kiran waya ba gaisuwa ba komai?,duk kinzo kin gaidani dazu da safe amma yanzu mecece?,la'asar fa muke dosa?" Shuru yadan biyo baya kafin muryarta ta sake bayyana a karye
"Kiyi haquri,ina wuni?.....kin yini lafiya?"
"Lafiya lau" Ta furta a dake
"Ina 'yan kaba,kizo daidai bakin kasuwar turawa ki jirani" Daga haka ta katse wayar.
Dubanta maamah tayi tana mamaki
"Hajja me kuma zai kaimu 'yan kaba?,ai sam ba hanyarmu bace" Zamanta ta gyara tana sake sakin shu'umin murmushi
"Eh mana.....ai so nake ta sake gane girman izzar tawa......sai bayan mun isa gidan ki zaki fahimci sauran aikin". Sosai maamah ke duban hajja din,lallai dole tasha kan kowa da komai,dole ta murxa kambunta yadda takeso. Sai yanxu take tambayar kanta ya akayi tayi sanyi haka ta sake?,hajjan da a baya a wajenta take daukan courses na abubuwa amma yanzu nema take ta zama malamarta qarfi da yaji?.
"Kina mamaki ne mariya?" Ta tambayeta tana kallon hanya
"Ai duk wanda yayi bacci a wannan zamanin zaiga bacci.....ba yara na ba ba surukaina ba.....hatta da jikokina.....yara da manya dukka sai abinda hajja ta shimfida"........
Ji yayi tamkar an daka masa tsawa tsakiyar baccinsa ana kuma masa umarni da ya farka. A nutse ya farka saidai kuma yanajin wani irin sauti mara dadi yana amsa kuwwa cikin kunnuwansa tamkar dai a mafarki akayi masa tsawar. Idanunsa ya lumshe a hankali yana son tuna abinda ya faru din,amma kansa blank bai iya hasaso komai ba
"Hasbiyallahu la'ilaha illa huwhuw,alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azeem" Ya furta a hankali bakinsa yana motsawa.
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
PAGE 55
Tsam yayi da ransa yana jin yanayin jikinsa yana sauyawa daga ainihin yadda ya kwanta din a dazun. Numfashi ya aje a hankali ya yaye blanket din ya miqe,ya zauna sosai saman gadon. Duk da knocking din da akeyi din hakan bai hanashi hada hannuwansa guri guda yayi addua ba,ya shafa saman fuskarsa a nutse sannan ya zuro qafafunsa qasa ya miqe.
A nutse yake takowa zuwa ainihin falon nasa dake cike da nutsuwa,shuru tamkar ba cikin gidan yake ba,komai komai cikin matsananciyar tsafta a killace kamar yadd yakeso koda yaushe ya dinga ganin komai a hakan.
Yana ci gaba da jin jikinsa da wata 'yar maqalalliyar kasala har ya isa qofar falon,ya murza key ya bude qofar amma bai murza handle ba,ya barta a haka yana komawa da baya hadi da bada umarnin a shigo.
Tun bai zauna ba ta sako qafafunta falon,dauke da wani kyakkyawan kwando me qananun tayoyi,yana da mariqi tamkar na luggage ko trolley da zaka iya rageshi ko ka qarashi sannan ka jashi yadda kakeso.
Da sallama a bakinta da qanqanuwar nutsuwar nan da take samar da ita a gabansa.
"Wa'alaikumussalam" Ya amsa yana zama saman daya daga cikin qawatattun sofas din da suka yiwa falon qawanya masu tsananin taushi da kyau na gaske,yasa hannunsa yana lalubem remote na A.c din falon don ya rageta. Shi din ba kasafai ya fiya son ac ba ko ya qureta har haka ba,wannan din sai oga farouq,a nan ma zaka iya jin kansa dashi.
"Hamma barka da warhaka". Ta fada cikin shagwabarta da marairaitar nan tata data zama a halittarta. Labbansa ya motsa kadan da wani yanayi da yafi kama da murmushi
"Habibtyn hamma" Ya furta a nutse kaman yadda tsoron qarewar haruffan bakinsa. Sunan daya kiratan dashi ya sanyata ta sake rakwarkwabewa. Ta tabe fuska tana kallonsa
"....hamma na dauka ka daina yayi na......BB farouq yacemin ka samo wadda ta sace zuciyarka.....tunda ta sace zuciyarka wai kuma tayi snatching naka a wajen kowa....she owns you ita kadai". Qaramin murmushi ya sake subuce masa wanda yafi na baya. Rigimar amna yawa ne da ita,har yau bata girma baisan kuma sanda zata girma din ba,yafi tunanin aure ne kawai zai kawo mata wannan hankalin da girman. Gefe daya farouq,shikam a duniya yanaso yaga ya tubura amna din,wani lokacin yana yi ne kaman hankalinsu daya,abinda kuma bazai taba zama hakan ba
"Zo nan" Ya fada yana yafitota da hannu gami da nuna mata gefansa. Sai ta tako din a hankali ita da kwandon nata har ta iso gabansa ta zame ta zauna sosai
"Baki gaya masa tare zaku zabi mata da hamma ba?,baki gaya masa sai wadda kikace tayi kinaso sannan hamma ya aura ba?" Yayi mata tambayar yana kallon qwayoyin idanunta abinda ya qara mata karsashi da qwarin gwiwa. Murmushi ya subuce mata data tuna da wannan
"Na gaya masa hamma sai ya tabe baki,kasan me yace?" Kai ya girgiza yana qara girmama quruciyar amna din,tabbas auta ba wasa ba,ko yaya sai wannan quruciyar ta tabashi
"Wai ita soyayya ba ruwanta da jiran lokaci ko dacewa,sace zuciya takeyi ko an shirya ko ba'a shirya ba....." Ta qarasa maganar daidai sanda farouq din yayi knocking hadi da turo qofar yashigo gaba daya,don yaji muryarta alamun suna zaune daga falonne.
Tsaf kalaman nata da suka fito daga bakin farouq din duka zauna masa akai,sai ya daga kai yana dubansa sanda yake takowa falon. Ya bude baki zai fara mata tsiyan nashi fu'ad din ya tari numfashinsa
"Kai kakeso ka lalatamin kunnuwan qanwa?.....kai kake karanta mata yadda soyayya take ko?".
Wani dariya ya saki yana saka hannu ya dauki green apple guda daya cikin apple din dake ajiye cikin wani dan kwando nan saman fridge din dake kusa dashi yana takowa falon
(Tabbas gaskiya ne da akace ka guji sharrin wanda ka kyautatawa.......me makon jin dadi kyakkyawan fata da kyakkyawan mu'amala ta shiga tsakaninsu da mutanen da suka maida mata 'ya'ya mutum.....amma ga nata salon sakamakon,Allah kayi mana tsari daga sharrin dukkan wani abu me sharri mutum ko aljan,me rai ko maras rai ameen ya hayyu ya qayyumu).
Bugu daya tak aka daga kiran da hajjan tayi,muryarsa ta fito tarwai yana gaidata. Cikin kulawa ta amsa masa sannan tace
"Kaga yahaya.......naje unguwa ne sai na sallami driver da xummar zan tuqo kaina na dawo gida......."
"Me yasa hajja?,ta yaya zakiyi tuqi da kanki?" Ya fada a tsananin firgice kaman wanda akace masa ta hallaka. Murmushin qasaita ta aje
"To ai yanzu ma gashi na kasa dawowa din da kaina duk kasala ta rufeni...."
"Bari na kira driver din ya dawo ya maidaki" Ya furta da hanzari
"Kaga dakata.....wanne irin driver?" Ta fada tana bata rai
"Yi haquri hajja,me kk so?" Ya sake fada a rikirkice
"Matarka nakeso ka turomin ita zata maidani......kace ta kirani na bata kwatancen inda nake yanzu haka ina jiranta......kada kuma ta batamin lokaci" Ta fada tana bata rai
"An gama" Ya fada zuciyarsa na rawa.
Ta rigashi ajiye wayar ta waiwaya tana kallon maamah cikin murmushi
"Kinsan matar da nace a kiramin?" Kai maamah ta girgiza tana shakkar yiwuwar wanzuwar umarmin da hajjan ta bada yanzu yanzu
"Matarsa ce......itace taso dagamin yatsa taso tayi fito na fito dani,a zatonta tana da malaman da xasuyi mata aiki fiye da nawa......tanaso ta mallaki yahaya ta mallakeni.....har na sanya ya saketa na sakashi ya dawo da ita don tazo taga iyakarta......taga iya mizanin nawa aikin.....don tazo ta banbance tsakanin aya da tsakuwa,ta sake kuma fahimtar da gaske fa shi ruwa ba sa'an kwando bane......ita kanta a yanzun sai yadda nace mata,duk dana fahimci kanta yana fusga wani lokaci kaman wasu abubuwan idan nayi mata tana jin ciwonsu,shi yasa nakeson na qarasa horata da kyau" Kai kawai maamah take jinjinawa,abun yayi mata da kyau.....salon kuma ya burgeta yahau mizani da gwargwado na abinda take hasashen shimfidawa kanta. DA FUAD DA MUSADDIQ DAMA MATAYEN DA ZASU AURA SU ZAMA QARQASHIN IKONTA. wannan shine cikakken iko da isar UWA. Ta fada a ranta
"Wannan shine cikakken iko da isa.....ki katange komai kaman yadda sanda kk sha wahalar komai din ke daya kk sha" Hajja ta fada tana jinjina kai
"Indai ni na haifi fuad ya zama tilas ya fidda kudaden nan ya bani.....zan motsa masa qwanjina.....zan kuma banbance masa uwa da mahaifiya a wannan lokaci karo na farko" Maamah ta sake fada a ranta.
Ya jima riqe da wayar bayan gama waya da mahaifiyar tasa yana juya wayar a hannunsa. Sassa biyu na zuciyarsa kowanne na qalubalantar dan uwansa.
"Tayi daidai,ko mutuwa hajja tace muyi daidai ne......ai ta isa....girmanta yana da yawa,to laifin me ma tayi?,koni ta kira zuwa zanyi bare matata,komai tayi a kowanne lokaci ko yanayi daidai yake" Daya sashen yake fadi,yayin da daya sashen zuciyarsa yake cewa
"Ta yaya tana tsaka da hidimar gida,ya tabbatar yanzu haka tana can tana yiwa hajjan girkin rana daya zama wajibi aka kowacce matar danta tayi mata shi kulli yaumin rana da dare ba fashi......(tsarin girkin abincin gidan tsarin girki ne na bai daya,duk da irin girma da wadatar gidan tukunya daya ake dafa abincin safe rana dana dare,raba girki ne a tsakanin faccaloli tamkar kishiyoyi,kowacce zatayi kwana biyu 'yar uwarta ta karba,hakanan a tattare a babban dining room dake dauke da family dining table akecin dukka abincin. A nata fadin don a tattala mata dukiyar 'ya'ya,kuma dukkansu zasu samu sauqin kashe kudi a gidajensu,tunda kome zaa siyo hadin gwiwa zaayi a kawo......amma kuma ta gefe daya.....tsabar nuna isa izza da mulki ne,da kuma dabarar karantar motsin kowa cikin gidan ba tare data shiga sashen kowa ba don ta tattaro kowa din waje daya.
A yanzun ya tabbatar tana can tana wannan hada hada.....bama wannan ba......fita haka katsam a lokaci guda ba shiri?. Wannan sashen dake hango masa rashin dacewar shine sashe mafi rauni a zuciyarsa,don haka wancan bangaren ya rinjayeshi ya danna mata kira kanshi tsaye.
Sanda maamah ta bude baki da zummar sake magana kira ya shigo wayar hajja. Ta daga wayar tana kalla,sai ta sake wani murmushi me sauti
"Naja'atu ce" Ta fada cikin nishadi,saita daga wayar tana sanyata a hands free
"Salamu Alaikum hajja......daddynsu arfat yace kina buqatar nazo daukarki......kina daidai ina?" Fuska ta tsuke tamkar ba itace ta gama dariya yanzu ba
"Ke banason hauka......haka akeyi daga kiran waya ba gaisuwa ba komai?,duk kinzo kin gaidani dazu da safe amma yanzu mecece?,la'asar fa muke dosa?" Shuru yadan biyo baya kafin muryarta ta sake bayyana a karye
"Kiyi haquri,ina wuni?.....kin yini lafiya?"
"Lafiya lau" Ta furta a dake
"Ina 'yan kaba,kizo daidai bakin kasuwar turawa ki jirani" Daga haka ta katse wayar.
Dubanta maamah tayi tana mamaki
"Hajja me kuma zai kaimu 'yan kaba?,ai sam ba hanyarmu bace" Zamanta ta gyara tana sake sakin shu'umin murmushi
"Eh mana.....ai so nake ta sake gane girman izzar tawa......sai bayan mun isa gidan ki zaki fahimci sauran aikin". Sosai maamah ke duban hajja din,lallai dole tasha kan kowa da komai,dole ta murxa kambunta yadda takeso. Sai yanxu take tambayar kanta ya akayi tayi sanyi haka ta sake?,hajjan da a baya a wajenta take daukan courses na abubuwa amma yanzu nema take ta zama malamarta qarfi da yaji?.
"Kina mamaki ne mariya?" Ta tambayeta tana kallon hanya
"Ai duk wanda yayi bacci a wannan zamanin zaiga bacci.....ba yara na ba ba surukaina ba.....hatta da jikokina.....yara da manya dukka sai abinda hajja ta shimfida"........
Ji yayi tamkar an daka masa tsawa tsakiyar baccinsa ana kuma masa umarni da ya farka. A nutse ya farka saidai kuma yanajin wani irin sauti mara dadi yana amsa kuwwa cikin kunnuwansa tamkar dai a mafarki akayi masa tsawar. Idanunsa ya lumshe a hankali yana son tuna abinda ya faru din,amma kansa blank bai iya hasaso komai ba
"Hasbiyallahu la'ilaha illa huwhuw,alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azeem" Ya furta a hankali bakinsa yana motsawa.
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
PAGE 55
Tsam yayi da ransa yana jin yanayin jikinsa yana sauyawa daga ainihin yadda ya kwanta din a dazun. Numfashi ya aje a hankali ya yaye blanket din ya miqe,ya zauna sosai saman gadon. Duk da knocking din da akeyi din hakan bai hanashi hada hannuwansa guri guda yayi addua ba,ya shafa saman fuskarsa a nutse sannan ya zuro qafafunsa qasa ya miqe.
A nutse yake takowa zuwa ainihin falon nasa dake cike da nutsuwa,shuru tamkar ba cikin gidan yake ba,komai komai cikin matsananciyar tsafta a killace kamar yadd yakeso koda yaushe ya dinga ganin komai a hakan.
Yana ci gaba da jin jikinsa da wata 'yar maqalalliyar kasala har ya isa qofar falon,ya murza key ya bude qofar amma bai murza handle ba,ya barta a haka yana komawa da baya hadi da bada umarnin a shigo.
Tun bai zauna ba ta sako qafafunta falon,dauke da wani kyakkyawan kwando me qananun tayoyi,yana da mariqi tamkar na luggage ko trolley da zaka iya rageshi ko ka qarashi sannan ka jashi yadda kakeso.
Da sallama a bakinta da qanqanuwar nutsuwar nan da take samar da ita a gabansa.
"Wa'alaikumussalam" Ya amsa yana zama saman daya daga cikin qawatattun sofas din da suka yiwa falon qawanya masu tsananin taushi da kyau na gaske,yasa hannunsa yana lalubem remote na A.c din falon don ya rageta. Shi din ba kasafai ya fiya son ac ba ko ya qureta har haka ba,wannan din sai oga farouq,a nan ma zaka iya jin kansa dashi.
"Hamma barka da warhaka". Ta fada cikin shagwabarta da marairaitar nan tata data zama a halittarta. Labbansa ya motsa kadan da wani yanayi da yafi kama da murmushi
"Habibtyn hamma" Ya furta a nutse kaman yadda tsoron qarewar haruffan bakinsa. Sunan daya kiratan dashi ya sanyata ta sake rakwarkwabewa. Ta tabe fuska tana kallonsa
"....hamma na dauka ka daina yayi na......BB farouq yacemin ka samo wadda ta sace zuciyarka.....tunda ta sace zuciyarka wai kuma tayi snatching naka a wajen kowa....she owns you ita kadai". Qaramin murmushi ya sake subuce masa wanda yafi na baya. Rigimar amna yawa ne da ita,har yau bata girma baisan kuma sanda zata girma din ba,yafi tunanin aure ne kawai zai kawo mata wannan hankalin da girman. Gefe daya farouq,shikam a duniya yanaso yaga ya tubura amna din,wani lokacin yana yi ne kaman hankalinsu daya,abinda kuma bazai taba zama hakan ba
"Zo nan" Ya fada yana yafitota da hannu gami da nuna mata gefansa. Sai ta tako din a hankali ita da kwandon nata har ta iso gabansa ta zame ta zauna sosai
"Baki gaya masa tare zaku zabi mata da hamma ba?,baki gaya masa sai wadda kikace tayi kinaso sannan hamma ya aura ba?" Yayi mata tambayar yana kallon qwayoyin idanunta abinda ya qara mata karsashi da qwarin gwiwa. Murmushi ya subuce mata data tuna da wannan
"Na gaya masa hamma sai ya tabe baki,kasan me yace?" Kai ya girgiza yana qara girmama quruciyar amna din,tabbas auta ba wasa ba,ko yaya sai wannan quruciyar ta tabashi
"Wai ita soyayya ba ruwanta da jiran lokaci ko dacewa,sace zuciya takeyi ko an shirya ko ba'a shirya ba....." Ta qarasa maganar daidai sanda farouq din yayi knocking hadi da turo qofar yashigo gaba daya,don yaji muryarta alamun suna zaune daga falonne.
Tsaf kalaman nata da suka fito daga bakin farouq din duka zauna masa akai,sai ya daga kai yana dubansa sanda yake takowa falon. Ya bude baki zai fara mata tsiyan nashi fu'ad din ya tari numfashinsa
"Kai kakeso ka lalatamin kunnuwan qanwa?.....kai kake karanta mata yadda soyayya take ko?".
Wani dariya ya saki yana saka hannu ya dauki green apple guda daya cikin apple din dake ajiye cikin wani dan kwando nan saman fridge din dake kusa dashi yana takowa falon