Sashe 26
Alwashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yau zai dake shi. Amma hakan ba zai hana shi komawa cikinsu gobe ba. Kullum dai sai ya je cikinsu, sai kuma ya dawo mini yana kuka.
Ban ta'ba yun'kurin d'aukar mataki ba. Na d'auke kaina kawai, amma zahiri ba na jin dad'in hakan.
Watarana ya shigo yana gursheken kuka wanda ya fi na koyaushe. Saman goshinsa ya kumbura har ya yi 'kululu! Na kama shi da sauri ina mulmula masa tare da tambayarsa.
Ya ce." Mama Turmuzi ne ya buga mini kai a bango."
Na ce." Me ka yi masa yau kuma?"
" Ban yi masa komai ba mama, ball ya bugo shine don na mayar masa. Ya kama ni da duka Mamansu tana kallonsa."
Kamalu da yake sanya mini zif a jakkunkunan da nake yi na sayarwa. yana huci Ya ce "
Wallahi mama ba zan yarda ba dubi fa ki ga yadda ya lun'kuma masa goshi, na rantse da Allah sai na rama masa."
Ya tashi da mugun sauri ya kama hanya fita. Na dinga 'kwala masa kira bai juyo ba.
Na yun'kura na tashi da saurin gaske na bi bayansa.
Sai kawai na same su a farfajiyar gidan suna dambe. Kamalu har ya kaishi kasa yana saman ruwan cikinsa yana ta dukan bakinsa. Kusan gabad'aya muka isa wurin da uwarsa da sauran yaran gidan.
ihu! ta kurma ganin jini a bakin yaronta gashi a kwance a kasa yana kuka. Ta yi kukan kura ta janyo Kamulu. Na je na fizge shi daga hannunta. Sai ta hau d'ura masa ashariya tana fad'in " Kashe mini shi za ka yi a gidan ubansa, wannan wane irin samun wuri ne, agola da zage k'wanji akan d'an gida. Na rantse da Allah ba zan yarda ba."
Anti Maimuna ta ce." To, wai me ya had'a su ne, Jamila, ba fa a shiga fad'an yarana, a bi komai a hankali."
Na ce." Ka da ki yarda Jamila, don Allah ki yi duk abinda za ki yi, wato ke yaranki ba su lefi ko? Kin taba tuhumar dalilin da ya sanya Turmuzi yake dukan Yusi kullum, na san kin sani. Ki dubi goshinsa ki gani, a wurinki akayi kuma kuna kallo ya buga kansa da bango, ba ki mulmula masa ba. Yanzu kuma ko kunya ba ki ji ba kin zo kina kumfar baki, ki yi abinda za ki yi, ai ba tsoronki nake ji ba."
Aikuwa zan yi wallahi, ba za ki kawo mana alakakai cikin gida ba, shi yaron naki ai ba mu muka janyo shi ba, rashin zuciyarsa ne yake kawo shi wurina, ban ga dalilin da zai sanya ki kawo mana masifa cikin gida ba, dama an ce yaron nan mugu ne, sannan kuma 'barawo ne, duk mun samu labarin haka. Wallahi tallahi sai sun bar gidan."
Gabad'aya wurin ya yi tsit! domin Kalmar 'barawo da ta kira Kamalu ta girgiza kowa, har yaran. Anti Maimuna ta ce." Wace irin magana ce wannan Jamila, shin ke kin san me ki ka haifa, kada fa ki yi wa kaddarar wani dariya, tunda haihuwa ki ke, kuma kowa da k'uruciyarsa."
Na ce." Rabu da ita Anti Maimuna jahilace ai, bagidajiya mutuniyar kauye. Don kin kira yarona 'barawo ba zai dame ni ba, tunda kema kin haifa, kuma sai dai idan ke ce za ki bar gidan, amma Kamalu da Yusi zama daram, tunda ba na ubanki ba ne."
Wannan maganar tawa ta harzukata har sai da kwalla ta ciko a idonta. Muryata na rawa take cewa." An ce masa 'barawon, ai ba karya aka yi ba, ko za ki musanta ne, sau nawa ana kulleshi a Police station? Wallahi za ki ga matsayina a gidan nan na rantse da Allah sai kin yi dana sanin kirana da jahila, 'yar iska mai suffar karuwai."
Na ce." Na ji dai, ni na je makaranta, kuma ba 'yar kauye ba ce ni, ina da ilimi, sannan ba 'kazama ba ce."
Ta goge 'kwallar da ta d'igo a kumatunta. Ta tashi yaronta da yake kwance yana kuka ta ri'ke hannunsa suka kama hanyar barin wurin. Na dube ta tare da furta." Ina jiran matakin da za ki d'auka. Jahila bagidajiya kawai."
Tunda na lura ba ta so a kira ta da hakan, ni Kuma na ri'ke. Sai ta yi wani kukan kura za ta kawo mini cakuma. Anti Maimuna ta shiga tsakani.
Ta dinga d'ura mini ashariya sai ka ce bamagujiya. Na ce." Kin ga aikin jahilicin naki ko, a gaban ya ra ki ke wannan tumasamcin, ni ba zan yi kokawa dake ba saboda na je makaranta.
Anti Maimuna fad'i take don Allah Amina ki yi shiru, wallahi mu ba mu taba fad'a ba, da dadi babu dadi muna zaune lafiya."
Na ce." To ni ba sakarai ba ce, anti Maimuna ba zan zauna wannan bagidajiyar tana juya ni ba, ita din banza, ai ba tsoronta nake ji ba, kuma ba ita ta ajiye ni a gidan ba, wallahi daidai nake da ita, mu zuba shege ka fasa."
Ganin babu sassauci a tare da ni ya sanya ta juya wurinta tana rarrashinta. Ta tura ta wurinta tana bata ha'kuri.
Yaransu suka dinga ihu suna kiran Kamalu da 'barawo hooo! 'barawo ne."
Yusi ya fashe da kuka ya ruga da gudu ya shige wurina. Shi kuwa Kamalu Yana tsaye durmin danya babu alamun firgici, ko nadamar abinda ya aikata. Kuma ihun da yaran suke yi masa bai sanya zuciyarsa ta yi rauni ba.
Na ja hannunsa muka bar wurin zuciyata na 'kuna, duk abinda yake faruwa a gidan, ban tana gaya masa ba, yau kam idan ya dawo zan zayyane masa, ba zan iya ba wallahi.
A ranar dama girkin anti Maimuna ne, na yi ta Allah-Allah gari ya waye ya shigo domin da b'acin ran abin na kwana a raina.
Ko da ya shigo da safe sama-sama muka gaisa gabad'aya na kasa sakar masa fuska. Ga yaran su ma duk sun damu ganin yanayina sun takure kansu wuri d'aya. Hakan ya kara dasa mini kunci tare da dakacen auran gabad'aya, domin da na tabbatar da cewa bai fi karfin gidansa ba wallahi ba zan aure shi ba.
Yanayi na shi ya tabbatar masa da cewa akwai matsala.
Ya fara tambayata. Na dube shi takaicinsa na 'kara nu'kurkusata.
Na kalli yaran tare da cewa." Ku shiga d'aki." Suka tashi da sauri domin cika umarnina.
Na sake kallonsa a karo na biyu Na ce." Ka zauna domin maganar tana da girma, kuma ni ban d'auketa karama ba."
Ya dubi agogon da yake daure a hannunsa.
"Ban 'ki zaman ba ai, ina da uzuri mai girma a waje, ba na son doguwar magana Amina kada dai ki ce mini kema fad'an yaran za ki shiga."
Na ce." Ashe an gaya maka abinda ya faru?"
"Kwarai an gaya mini, Ammaa ban d'auki hakan a matsayin komai ba face zaman tare, dole idan Yara suka had'u sai an yi wannan, muma da haka duk muka tashi, ki yi hakuri kin ji ko".
Idona ya ciko da ruwan hawaye na ce." Ni fa ba wannan ne damuwata ba, yadda Jamila take Kiran Kamalu da b'arawo shine abinda ya bata mini rai, ai itama ta haifa, kuma ba ta san abinda za ta haifa ba nan gaba."
Ya 'bata fuska yana cewa." Kin ga don Allah ki san irin maganar da za ki furta, wane irin lafazi ne wannan? kina fatan na haifi lalatacce kenan?"
Hawaye suka fara gudana a kumatuna, na ce." Amma dai ka san da ciwo ko? kuma a'ina ta samu labarin tsalle-tsallen da Kamalu ya yi sai dai idan kaine ka tara su ka gaya musu."
"Kada ki zarge ni akan abinda ban yi ba, me zai sanya na gaya musu yaronki ba ya ji, wata'kila ta samu labari ne a wani wuri, kuma kema tun farko sai da na gaya miki ki zauna lafiya da su, kuma ki bi duk abinda suke so domin samun daidaito, su ki ka zo ki ka samu, ba zai yiwu ace kin zo da wani tsari ba."
Na dube shi raina a bace." Wallahi tallahi babu wadda zan bi a cikinsu, akan wane dalili? Ai lokacin da za ka aureni ba ka fad'a mini cewa matanka sun fi karfinka ba, ba zan jure ba, akan yarana zan iya komai, idan ba za ka siya mini mutunci ba, ka sawwake mini ba."
Ya ja tsaki Yana fad'in." Ai aure ba wasan yara ba ne, duka sati hud'u kacal, kin fara bayyana mini halinki, ba zan sake ki ba, saboda ina sonki, Yara kuma ni na ce ki zo da su zan ri'ke, idan hakan be yi miki ba, ki tattarasu ki kai su wani wurin, ni babu rabuwa a tsakanina dake."
"Cikin kuka sosai na ce." Wallahi ba zan iya ba, muddin ta kara aibata mini yaro sai na yi sharia da ita, ai tunda ya zo gidan bai ta'ba shiga wurinta ba balle ta ce ta nemi wani abu ta rasa, wallahi 'yansanda ne za su raba mu."
Kuka nake yi sosai. Hakan ya sanyayyar masa da jiki. Ya ce." To na ji zan ja mata kunne, ki yi hakuri, sannan kuma ki bi shawarar da na baki, ki zauna lafiya da su, bayan wannan kuma idan kin yi girki ki dinga rabawa da hannunki, ki daina kiran Maimuna, duk abinda ki ka san zai janyo zargi kada ki yi shi."
Na goge hawayen kumatuna tare da cewa." Ni fa na gaya maka babu wadda zan yi wa biyayya, Kai ka ajiye ni, kaine dole, tsakanina da su girmamawa ce kawai, amma ba zan bi son zuciya ba."
"To shikkenan, ki daina kukan haka, ya isa." Ya fad'a da sigar lallashi. Sai da ya tabbatar na yi shiru tukkuna ya kama hanyar fita yana fad'in."Ashe haka ki ke da rigima dama.
Ban ta'ba yun'kurin d'aukar mataki ba. Na d'auke kaina kawai, amma zahiri ba na jin dad'in hakan.
Watarana ya shigo yana gursheken kuka wanda ya fi na koyaushe. Saman goshinsa ya kumbura har ya yi 'kululu! Na kama shi da sauri ina mulmula masa tare da tambayarsa.
Ya ce." Mama Turmuzi ne ya buga mini kai a bango."
Na ce." Me ka yi masa yau kuma?"
" Ban yi masa komai ba mama, ball ya bugo shine don na mayar masa. Ya kama ni da duka Mamansu tana kallonsa."
Kamalu da yake sanya mini zif a jakkunkunan da nake yi na sayarwa. yana huci Ya ce "
Wallahi mama ba zan yarda ba dubi fa ki ga yadda ya lun'kuma masa goshi, na rantse da Allah sai na rama masa."
Ya tashi da mugun sauri ya kama hanya fita. Na dinga 'kwala masa kira bai juyo ba.
Na yun'kura na tashi da saurin gaske na bi bayansa.
Sai kawai na same su a farfajiyar gidan suna dambe. Kamalu har ya kaishi kasa yana saman ruwan cikinsa yana ta dukan bakinsa. Kusan gabad'aya muka isa wurin da uwarsa da sauran yaran gidan.
ihu! ta kurma ganin jini a bakin yaronta gashi a kwance a kasa yana kuka. Ta yi kukan kura ta janyo Kamulu. Na je na fizge shi daga hannunta. Sai ta hau d'ura masa ashariya tana fad'in " Kashe mini shi za ka yi a gidan ubansa, wannan wane irin samun wuri ne, agola da zage k'wanji akan d'an gida. Na rantse da Allah ba zan yarda ba."
Anti Maimuna ta ce." To, wai me ya had'a su ne, Jamila, ba fa a shiga fad'an yarana, a bi komai a hankali."
Na ce." Ka da ki yarda Jamila, don Allah ki yi duk abinda za ki yi, wato ke yaranki ba su lefi ko? Kin taba tuhumar dalilin da ya sanya Turmuzi yake dukan Yusi kullum, na san kin sani. Ki dubi goshinsa ki gani, a wurinki akayi kuma kuna kallo ya buga kansa da bango, ba ki mulmula masa ba. Yanzu kuma ko kunya ba ki ji ba kin zo kina kumfar baki, ki yi abinda za ki yi, ai ba tsoronki nake ji ba."
Aikuwa zan yi wallahi, ba za ki kawo mana alakakai cikin gida ba, shi yaron naki ai ba mu muka janyo shi ba, rashin zuciyarsa ne yake kawo shi wurina, ban ga dalilin da zai sanya ki kawo mana masifa cikin gida ba, dama an ce yaron nan mugu ne, sannan kuma 'barawo ne, duk mun samu labarin haka. Wallahi tallahi sai sun bar gidan."
Gabad'aya wurin ya yi tsit! domin Kalmar 'barawo da ta kira Kamalu ta girgiza kowa, har yaran. Anti Maimuna ta ce." Wace irin magana ce wannan Jamila, shin ke kin san me ki ka haifa, kada fa ki yi wa kaddarar wani dariya, tunda haihuwa ki ke, kuma kowa da k'uruciyarsa."
Na ce." Rabu da ita Anti Maimuna jahilace ai, bagidajiya mutuniyar kauye. Don kin kira yarona 'barawo ba zai dame ni ba, tunda kema kin haifa, kuma sai dai idan ke ce za ki bar gidan, amma Kamalu da Yusi zama daram, tunda ba na ubanki ba ne."
Wannan maganar tawa ta harzukata har sai da kwalla ta ciko a idonta. Muryata na rawa take cewa." An ce masa 'barawon, ai ba karya aka yi ba, ko za ki musanta ne, sau nawa ana kulleshi a Police station? Wallahi za ki ga matsayina a gidan nan na rantse da Allah sai kin yi dana sanin kirana da jahila, 'yar iska mai suffar karuwai."
Na ce." Na ji dai, ni na je makaranta, kuma ba 'yar kauye ba ce ni, ina da ilimi, sannan ba 'kazama ba ce."
Ta goge 'kwallar da ta d'igo a kumatunta. Ta tashi yaronta da yake kwance yana kuka ta ri'ke hannunsa suka kama hanyar barin wurin. Na dube ta tare da furta." Ina jiran matakin da za ki d'auka. Jahila bagidajiya kawai."
Tunda na lura ba ta so a kira ta da hakan, ni Kuma na ri'ke. Sai ta yi wani kukan kura za ta kawo mini cakuma. Anti Maimuna ta shiga tsakani.
Ta dinga d'ura mini ashariya sai ka ce bamagujiya. Na ce." Kin ga aikin jahilicin naki ko, a gaban ya ra ki ke wannan tumasamcin, ni ba zan yi kokawa dake ba saboda na je makaranta.
Anti Maimuna fad'i take don Allah Amina ki yi shiru, wallahi mu ba mu taba fad'a ba, da dadi babu dadi muna zaune lafiya."
Na ce." To ni ba sakarai ba ce, anti Maimuna ba zan zauna wannan bagidajiyar tana juya ni ba, ita din banza, ai ba tsoronta nake ji ba, kuma ba ita ta ajiye ni a gidan ba, wallahi daidai nake da ita, mu zuba shege ka fasa."
Ganin babu sassauci a tare da ni ya sanya ta juya wurinta tana rarrashinta. Ta tura ta wurinta tana bata ha'kuri.
Yaransu suka dinga ihu suna kiran Kamalu da 'barawo hooo! 'barawo ne."
Yusi ya fashe da kuka ya ruga da gudu ya shige wurina. Shi kuwa Kamalu Yana tsaye durmin danya babu alamun firgici, ko nadamar abinda ya aikata. Kuma ihun da yaran suke yi masa bai sanya zuciyarsa ta yi rauni ba.
Na ja hannunsa muka bar wurin zuciyata na 'kuna, duk abinda yake faruwa a gidan, ban tana gaya masa ba, yau kam idan ya dawo zan zayyane masa, ba zan iya ba wallahi.
A ranar dama girkin anti Maimuna ne, na yi ta Allah-Allah gari ya waye ya shigo domin da b'acin ran abin na kwana a raina.
Ko da ya shigo da safe sama-sama muka gaisa gabad'aya na kasa sakar masa fuska. Ga yaran su ma duk sun damu ganin yanayina sun takure kansu wuri d'aya. Hakan ya kara dasa mini kunci tare da dakacen auran gabad'aya, domin da na tabbatar da cewa bai fi karfin gidansa ba wallahi ba zan aure shi ba.
Yanayi na shi ya tabbatar masa da cewa akwai matsala.
Ya fara tambayata. Na dube shi takaicinsa na 'kara nu'kurkusata.
Na kalli yaran tare da cewa." Ku shiga d'aki." Suka tashi da sauri domin cika umarnina.
Na sake kallonsa a karo na biyu Na ce." Ka zauna domin maganar tana da girma, kuma ni ban d'auketa karama ba."
Ya dubi agogon da yake daure a hannunsa.
"Ban 'ki zaman ba ai, ina da uzuri mai girma a waje, ba na son doguwar magana Amina kada dai ki ce mini kema fad'an yaran za ki shiga."
Na ce." Ashe an gaya maka abinda ya faru?"
"Kwarai an gaya mini, Ammaa ban d'auki hakan a matsayin komai ba face zaman tare, dole idan Yara suka had'u sai an yi wannan, muma da haka duk muka tashi, ki yi hakuri kin ji ko".
Idona ya ciko da ruwan hawaye na ce." Ni fa ba wannan ne damuwata ba, yadda Jamila take Kiran Kamalu da b'arawo shine abinda ya bata mini rai, ai itama ta haifa, kuma ba ta san abinda za ta haifa ba nan gaba."
Ya 'bata fuska yana cewa." Kin ga don Allah ki san irin maganar da za ki furta, wane irin lafazi ne wannan? kina fatan na haifi lalatacce kenan?"
Hawaye suka fara gudana a kumatuna, na ce." Amma dai ka san da ciwo ko? kuma a'ina ta samu labarin tsalle-tsallen da Kamalu ya yi sai dai idan kaine ka tara su ka gaya musu."
"Kada ki zarge ni akan abinda ban yi ba, me zai sanya na gaya musu yaronki ba ya ji, wata'kila ta samu labari ne a wani wuri, kuma kema tun farko sai da na gaya miki ki zauna lafiya da su, kuma ki bi duk abinda suke so domin samun daidaito, su ki ka zo ki ka samu, ba zai yiwu ace kin zo da wani tsari ba."
Na dube shi raina a bace." Wallahi tallahi babu wadda zan bi a cikinsu, akan wane dalili? Ai lokacin da za ka aureni ba ka fad'a mini cewa matanka sun fi karfinka ba, ba zan jure ba, akan yarana zan iya komai, idan ba za ka siya mini mutunci ba, ka sawwake mini ba."
Ya ja tsaki Yana fad'in." Ai aure ba wasan yara ba ne, duka sati hud'u kacal, kin fara bayyana mini halinki, ba zan sake ki ba, saboda ina sonki, Yara kuma ni na ce ki zo da su zan ri'ke, idan hakan be yi miki ba, ki tattarasu ki kai su wani wurin, ni babu rabuwa a tsakanina dake."
"Cikin kuka sosai na ce." Wallahi ba zan iya ba, muddin ta kara aibata mini yaro sai na yi sharia da ita, ai tunda ya zo gidan bai ta'ba shiga wurinta ba balle ta ce ta nemi wani abu ta rasa, wallahi 'yansanda ne za su raba mu."
Kuka nake yi sosai. Hakan ya sanyayyar masa da jiki. Ya ce." To na ji zan ja mata kunne, ki yi hakuri, sannan kuma ki bi shawarar da na baki, ki zauna lafiya da su, bayan wannan kuma idan kin yi girki ki dinga rabawa da hannunki, ki daina kiran Maimuna, duk abinda ki ka san zai janyo zargi kada ki yi shi."
Na goge hawayen kumatuna tare da cewa." Ni fa na gaya maka babu wadda zan yi wa biyayya, Kai ka ajiye ni, kaine dole, tsakanina da su girmamawa ce kawai, amma ba zan bi son zuciya ba."
"To shikkenan, ki daina kukan haka, ya isa." Ya fad'a da sigar lallashi. Sai da ya tabbatar na yi shiru tukkuna ya kama hanyar fita yana fad'in."Ashe haka ki ke da rigima dama.