Sashe 14
Alwashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Bacci ne ya d'auke ni mai nauyin gaske anan na bingire ba tare dana hau katifar dake shimfide a gefe ba. Wajan sha biyu da rabi anti Yagana ta tashe ni. Wai na hau katifa kada jikina ya yi ciwo. Sama sama nake jinta na ja jikina na hau katifar na kwanta ta kashe fitilar d'akin ta fita. Gefin asuba na tashi na zauna gabad'aya dan'kon baccin ya saki idona. Gabana ya dinga bugawa. Wani mafarki na yi mara kyau wai ga mutane a kofar gidanmu a tsaye anata hayaniya. Wani Yana cewa a tafi a nemo Kamalun duk inda ya shiga.
na sauka daga kan katifar na nufi bandakin da yake cikin d'akin cikin sanyi jiki da kiran Innalillahi wa'ina ilaihi! Ban kwanta da abin a Raina ba ballantana na ce. Gabad'aya sai hankalina ya yi gida don mafarkin ya tsorata ni sosai.
Muna karyawa da Anti Yagana na ce." Jira nake Babanmu ya tashi daga bacci anti yau za mu tafi tunda an daura aure, na bar din'kunan mutane wallahi, ga Kamalu, kin san abin sai a hankali."
Ta ce." Malama kya bari dai sai gobe wace irin tafiya ce wannan da gaggawa haka, Shi ma Babanmu haka yace sai gobe sai ku tafi a nutse, jiya ai mun jima dashi da daddare muna hira.
Kiran waya ya katse maganar da zan yi. Ina dubawa na ga Usaini. Gabana ya buga. Hannuna na rawa nasa a kunnena.
Ya ce." Anti Amina an tashi lafiya? Yau za ku dawo ko?"
Na ce." Lafiya Lou, wata'kila yau ko gobe, ina fatan dai lafiya, ina Kamalu ka bashi wayar mu gaisa."
Ya yi shiru bai ce komai ba."
Cikin mi'kawa Allah lamarin na ce." Usaini tunda na ga Kiranka na tabbatar da matsala, ka fad'a mini kawai, abinda ba sabon abu ba ne, me ya faru?"
A sanyaye ya ce." Anti abin ne babu dadi wallahi, da har na ce kada a gaya miki. Ummansu Hadiza ta ce a fad'a miki kawai, ki san abinda yake faruwa."
Na daga kai ina kallon Baba lokacin yana ko'karin shigowa. Na ce." Usaini gaya mini don Allah, ba na son kwane kwane Kamalun mutuwa ya yi ne?"
Ya ce." A a, da asuba ne da aka tashe su shi da Saminu domin su yi sallah, bayan sun fito daga massalaci sai suka je tu'ka-tu'kar kofar gidan Alhaji Lawan. Suka kwashe jarkokin mutane har da sababbi sun kai goma suka had'a da zungureriyar kurar ruwar wani dan garuwa. Suka nufi cikin kasuwa, su uku Saminu Kamalu da kuma Shamsu 'kanin Bashir abokina. To Allah dai Ya rufa asiri ba su sayar ba, Malam Maharazu na bayan gidanmu ya shiga kasuwar da wuri shine ya gansu a gurin masu sayarwa ana ta ciniki, to da yake akwai police station ana gane sato wa suka yi, gabad'aya su ukun aka kama su suna can a cell a kulle."
Ajiyar zuciya na sauke na ce." To Usaini Allah Ya kyauta, idan hali ya yi za mu iya dawowa yau, idan kuma hakan bai samu ba sai gobe idan Allah ya nufa ."
Ya ce." Shikkenan anti Amina, amma don Allah ki kwantar da hankalinki, na sanki da sanya damuwa a cikin rai, kin ga ba ke kad'ai ba ce, wallahi ba ki ga yadda Ummanmu take kuka ba yanzu ta yadda da cewar Saminu shine shugabaa cikinsu."
Na ce." To, zan danne Usaini, ba zan sanya damuwa ba, na gode kawai zan kira ka idan an jima, yanzu ya mu tattauna da Babanmu."
Na kashe wayar na dube su. Gabad'aya hankalinsu Yana kaina, ba sai na yi musu karin bayani ba sun ji komai tunda handsfree na sanya wayar rad'au duk sun ji komai.
Anti Yagana ta fashe da kuka tana fad'in." Wannan wace irin masifa ce, yaran nan suke nema su janyo mana, jarkokin ruwa uban me za su yi da kudin idan sun sayar, Yara k'ananu dasu."
Na bita da kallo ban ce komai ba, domin a lokacin ma ni kaina kullewa ya yi na rasa tunanin me zan yi, na san dai tun lokacin da Usaini ya fara yi mini bayanin abinda yake faruwa wani abu mai nauyi ya tokare mini a wuya.
Babanmu ya dubeta Yana fad'in." Ai ba sabon abu ba ne Yagana ke yanzu ki ka ji shine dalili. Ki daina yi musu kuka, yi musu addu'a kawai, Allah Ya tsayar musu iya nan, kuruciya ce kowa da irin tasa."
Tana goge hawaye wasu na sake zubowa. Gabad'aya ta rikice sai Kiran Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un take yi. Ya dube ni yana cewa." Tashi ki shirya mu tafi a samu a fito da su, zaman cell din ma wata masifar ce, bari na fita na yi sallama da jama'a."
Ya tashi ya fita da saurin gaske.
Na dubi anti Yagana da kanta yake a sunkuye hawaye na zuba tana sharewa na ce." Ashe ba ni kad'ai ba ce mai saurin kuka."
Ta kalle ni, na yi murmushin da babu nishadi a cikinsa. Na tashi kafafuna na rawa na shiga d'aki na fara had'a kayana. Cikin zuciyata ina ta kiran sunan makagina da ya kawo mini d'auki
***
Tafiya ce muka yi ta a gigice cikin rashin kintsi shiyasa ba kowa muka yi wa sallama ba. Allah Ya nufa muka samu mota mai kyau da rashin tsaye tsaye. La'asar sakaliya muka sauka a tasha nan kasuwar kwari.
Na kira Usaini domin jin karin bayani. Ya ce mini ai har yànzu yaran suna can cell a rufe domin jama'ar unguwa sun ce sai an shiga kotu an hukuntasu tunda an jima ana sace musu kayan ruwa."
Na ce." Kai kana ina yanzu, ko kana shago ne?"
Ya ce." E, ina shago anti kin san Babanmu da zaku tafi ni ya barwa dan mukkuli, idan an samu aiki na yi, nake basu kudin abinci, yanzu haka ma akwai aikin mutane a hannuna."
Na ce." To yi zamanka tunda kana da aiki, amma ka samu wani ka turo shi muna nan tashar kwari, ya zo ya d'auki kayan nan zan bashi kudin mota."
Ya ce." To yanzu kuwa anti." Na kashe wayar. Na dubi Babanmu da yake tsaye a jikin wata tumba ta wutar lantarki, tausayi ya ba ni kwarai, haka dai na daure na yi masa bayani duk yadda muka yi.
Ya ce." Ai dama da wuya jama'ar unguwar nan su ha'kura, kin san babu had'in kai, idan matsala ta faru a maimakon a had'u a kashe wutar sai a samu wasu a gefe suna rurata. Yaran nan kowa yana dasu sai addua."
Na ce." Baba tafi gida ka huta, ni zan wuce station din, in sha Allahu abin ba zai yi girma ba."
Ya ce." A'a, ba zan bari ki je ke kadai ba, mu je tare Amina, idan da namiji abin zai fi yin kyau."
A sanyaye na ce." To shikkenan Allah Ya taikaita, su kuma Ubangiji Allah Ya shirya mana su."
ya amsa da "Amin Ya Allahu......✍️
*1k on talgram*
*0542382124...Binta Umar gtbank*
*07084653262*
[11/19, 9:07 AM] Aunty B: *GUDUN AURE!*
*NA*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*M.W.A*
*Marubuciyar*
*Yar bangar siyasa*
*Ba'aboren namiji*
*Madadi*
*Ga irinta nan*
*Goje*
*Babban yaro*
*Sadauki Omar*
*Nida Yaya sadam*
*Da sauransu..!*
*TALLAH!*
'Yan uwa
Barkanku da zuwa FAMAS SCENTS OF LEGENDS,
duniyar turarukan wuta masu kamshi na musamman mai samar da nutsuwa da kwanciyar hankali.
Mun tanadar muku da turarukan wuta masu dadin kamshi kamar su
Sandal flakes
Hawee
Gabgab
Halut
Dorot
Coconut chips
Dufr(farce)
Black khumra
Brown khumra
White khumra
Oil perfumes da
Body sprays
Dan turara gidajenku,tufafinku da jikinku.
Ga duk mai buqata zai iya tuntuban mu ta lamba kamar haka
Call/WhatsApp
07037489958
Location:Gonan Ganye,zaria
Kaduna state
Nationwide Delivery
na sauka daga kan katifar na nufi bandakin da yake cikin d'akin cikin sanyi jiki da kiran Innalillahi wa'ina ilaihi! Ban kwanta da abin a Raina ba ballantana na ce. Gabad'aya sai hankalina ya yi gida don mafarkin ya tsorata ni sosai.
Muna karyawa da Anti Yagana na ce." Jira nake Babanmu ya tashi daga bacci anti yau za mu tafi tunda an daura aure, na bar din'kunan mutane wallahi, ga Kamalu, kin san abin sai a hankali."
Ta ce." Malama kya bari dai sai gobe wace irin tafiya ce wannan da gaggawa haka, Shi ma Babanmu haka yace sai gobe sai ku tafi a nutse, jiya ai mun jima dashi da daddare muna hira.
Kiran waya ya katse maganar da zan yi. Ina dubawa na ga Usaini. Gabana ya buga. Hannuna na rawa nasa a kunnena.
Ya ce." Anti Amina an tashi lafiya? Yau za ku dawo ko?"
Na ce." Lafiya Lou, wata'kila yau ko gobe, ina fatan dai lafiya, ina Kamalu ka bashi wayar mu gaisa."
Ya yi shiru bai ce komai ba."
Cikin mi'kawa Allah lamarin na ce." Usaini tunda na ga Kiranka na tabbatar da matsala, ka fad'a mini kawai, abinda ba sabon abu ba ne, me ya faru?"
A sanyaye ya ce." Anti abin ne babu dadi wallahi, da har na ce kada a gaya miki. Ummansu Hadiza ta ce a fad'a miki kawai, ki san abinda yake faruwa."
Na daga kai ina kallon Baba lokacin yana ko'karin shigowa. Na ce." Usaini gaya mini don Allah, ba na son kwane kwane Kamalun mutuwa ya yi ne?"
Ya ce." A a, da asuba ne da aka tashe su shi da Saminu domin su yi sallah, bayan sun fito daga massalaci sai suka je tu'ka-tu'kar kofar gidan Alhaji Lawan. Suka kwashe jarkokin mutane har da sababbi sun kai goma suka had'a da zungureriyar kurar ruwar wani dan garuwa. Suka nufi cikin kasuwa, su uku Saminu Kamalu da kuma Shamsu 'kanin Bashir abokina. To Allah dai Ya rufa asiri ba su sayar ba, Malam Maharazu na bayan gidanmu ya shiga kasuwar da wuri shine ya gansu a gurin masu sayarwa ana ta ciniki, to da yake akwai police station ana gane sato wa suka yi, gabad'aya su ukun aka kama su suna can a cell a kulle."
Ajiyar zuciya na sauke na ce." To Usaini Allah Ya kyauta, idan hali ya yi za mu iya dawowa yau, idan kuma hakan bai samu ba sai gobe idan Allah ya nufa ."
Ya ce." Shikkenan anti Amina, amma don Allah ki kwantar da hankalinki, na sanki da sanya damuwa a cikin rai, kin ga ba ke kad'ai ba ce, wallahi ba ki ga yadda Ummanmu take kuka ba yanzu ta yadda da cewar Saminu shine shugabaa cikinsu."
Na ce." To, zan danne Usaini, ba zan sanya damuwa ba, na gode kawai zan kira ka idan an jima, yanzu ya mu tattauna da Babanmu."
Na kashe wayar na dube su. Gabad'aya hankalinsu Yana kaina, ba sai na yi musu karin bayani ba sun ji komai tunda handsfree na sanya wayar rad'au duk sun ji komai.
Anti Yagana ta fashe da kuka tana fad'in." Wannan wace irin masifa ce, yaran nan suke nema su janyo mana, jarkokin ruwa uban me za su yi da kudin idan sun sayar, Yara k'ananu dasu."
Na bita da kallo ban ce komai ba, domin a lokacin ma ni kaina kullewa ya yi na rasa tunanin me zan yi, na san dai tun lokacin da Usaini ya fara yi mini bayanin abinda yake faruwa wani abu mai nauyi ya tokare mini a wuya.
Babanmu ya dubeta Yana fad'in." Ai ba sabon abu ba ne Yagana ke yanzu ki ka ji shine dalili. Ki daina yi musu kuka, yi musu addu'a kawai, Allah Ya tsayar musu iya nan, kuruciya ce kowa da irin tasa."
Tana goge hawaye wasu na sake zubowa. Gabad'aya ta rikice sai Kiran Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un take yi. Ya dube ni yana cewa." Tashi ki shirya mu tafi a samu a fito da su, zaman cell din ma wata masifar ce, bari na fita na yi sallama da jama'a."
Ya tashi ya fita da saurin gaske.
Na dubi anti Yagana da kanta yake a sunkuye hawaye na zuba tana sharewa na ce." Ashe ba ni kad'ai ba ce mai saurin kuka."
Ta kalle ni, na yi murmushin da babu nishadi a cikinsa. Na tashi kafafuna na rawa na shiga d'aki na fara had'a kayana. Cikin zuciyata ina ta kiran sunan makagina da ya kawo mini d'auki
***
Tafiya ce muka yi ta a gigice cikin rashin kintsi shiyasa ba kowa muka yi wa sallama ba. Allah Ya nufa muka samu mota mai kyau da rashin tsaye tsaye. La'asar sakaliya muka sauka a tasha nan kasuwar kwari.
Na kira Usaini domin jin karin bayani. Ya ce mini ai har yànzu yaran suna can cell a rufe domin jama'ar unguwa sun ce sai an shiga kotu an hukuntasu tunda an jima ana sace musu kayan ruwa."
Na ce." Kai kana ina yanzu, ko kana shago ne?"
Ya ce." E, ina shago anti kin san Babanmu da zaku tafi ni ya barwa dan mukkuli, idan an samu aiki na yi, nake basu kudin abinci, yanzu haka ma akwai aikin mutane a hannuna."
Na ce." To yi zamanka tunda kana da aiki, amma ka samu wani ka turo shi muna nan tashar kwari, ya zo ya d'auki kayan nan zan bashi kudin mota."
Ya ce." To yanzu kuwa anti." Na kashe wayar. Na dubi Babanmu da yake tsaye a jikin wata tumba ta wutar lantarki, tausayi ya ba ni kwarai, haka dai na daure na yi masa bayani duk yadda muka yi.
Ya ce." Ai dama da wuya jama'ar unguwar nan su ha'kura, kin san babu had'in kai, idan matsala ta faru a maimakon a had'u a kashe wutar sai a samu wasu a gefe suna rurata. Yaran nan kowa yana dasu sai addua."
Na ce." Baba tafi gida ka huta, ni zan wuce station din, in sha Allahu abin ba zai yi girma ba."
Ya ce." A'a, ba zan bari ki je ke kadai ba, mu je tare Amina, idan da namiji abin zai fi yin kyau."
A sanyaye na ce." To shikkenan Allah Ya taikaita, su kuma Ubangiji Allah Ya shirya mana su."
ya amsa da "Amin Ya Allahu......✍️
*1k on talgram*
*0542382124...Binta Umar gtbank*
*07084653262*
[11/19, 9:07 AM] Aunty B: *GUDUN AURE!*
*NA*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*M.W.A*
*Marubuciyar*
*Yar bangar siyasa*
*Ba'aboren namiji*
*Madadi*
*Ga irinta nan*
*Goje*
*Babban yaro*
*Sadauki Omar*
*Nida Yaya sadam*
*Da sauransu..!*
*TALLAH!*
'Yan uwa
Barkanku da zuwa FAMAS SCENTS OF LEGENDS,
duniyar turarukan wuta masu kamshi na musamman mai samar da nutsuwa da kwanciyar hankali.
Mun tanadar muku da turarukan wuta masu dadin kamshi kamar su
Sandal flakes
Hawee
Gabgab
Halut
Dorot
Coconut chips
Dufr(farce)
Black khumra
Brown khumra
White khumra
Oil perfumes da
Body sprays
Dan turara gidajenku,tufafinku da jikinku.
Ga duk mai buqata zai iya tuntuban mu ta lamba kamar haka
Call/WhatsApp
07037489958
Location:Gonan Ganye,zaria
Kaduna state
Nationwide Delivery