Sashe 8
Yar Zaman Wanka Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kai dai da ka san hakan amma Imirana mai ya sani yaron nan banda ƙafafa da nuna shi mai gida ne"
"Imran ko Inna"
"Shi mana, bari ma na baka labarinsa, amma sai na fara baka daga farko ranar da na kwana ban yi bacci ba"
"Baki yi bacci ba fa Inna, garin yaya?"
"Wallahi fa Abida, haka kawai ban ji ba ban gani ba,ina ranar da ka kawo mu daga asibiti har nake baka labarin abokin Imirana wanda ke wasarere da jikinsa"
"Eh Inna na tuna"
"To wallahi a ranar nan ni na san irin kwanan da na yi a gidan nan" Ta faɗa tana share ƙwallah.
"Subhanallahi Inna ba dai a waje kika kwana ba da sanyin nan?"
"Haba Abida ana ga yaƙi kana ga ƙura yo ba gwara a saka ni a randa ba in kwana da irin kwanan da na yi ranar nan kai ni dai sai da na ji ina ma ban taho ZAMAN WANKAN nan ba, ni da na kwana a tsakanin katako sama katako ya tokare ƙasana katako "
"Katako kuma Inna"
"Yo a ƙarƙashin gado fa na kwana, bayan nna nawa da gado ya matse yadda ka san an yiwa mota lodin shanu haka na ji, wallahi ba dan na shafa man zafi ba da Allah kaɗai ya san me zai faru.
" Ta faɗa tana ɓantarar goron da fa ɗauka daga cikin wanda aka kawo mata ta ƙulle ledar.
"Garin yaya?"
Shiru ta ɗan yi dan bata son faɗar gaskiyar dalilin da ya sa ta kwana a ƙasan gado dan har yau bata daina jin tsoron aljanin ba kuma har yau tana ganin kamar dai yana kallonta a gidan.
"Sanyin garin nan ya sa na kwana a ƙasan gado" Ta faɗa tana ƙara gutsurar goro fuskarta ɗauke da damuwa.
"Sanyi fa Inna, lallai sanyi bai kyauta ba" Ya faɗa yana dariya dan ya fuskanci bata faɗi gaskiyar abin da ya sa ta kwana a ƙasan gadon ba dan daga yadda ta faɗa ya san ta faɗa ne kawai, ga kuma
yadda take bada labarin ma kaÉ—ai abin dariya ne.
"Sanyi mana, ai ba fa shi ne abin da na fuskanta ba kaɗai, ka san Hassan ya zo da baiwa a jikinsa wato haka kawai sai yaro ya ringa saɓaɓa-saɓa ya bar ainihin halittarsa ya koma ta miciji"
"Miciji Inna" Ya faÉ—a da yana son tabbatarwa dan ya san dai Imran ya xe fatar bayan yaron ta miciji ce.
"Miciji mana, ai a washe gari da haihuwarsa ya koma miciji da kan mutum amma saboda rashin imani na Imirana haka ya garƙameni da micijin nan a ɗaki tun ina neman ɗauki har na gaji, ya sanya na rinƙa karanta alif an baki waw zal, kai daga ƙarshe dai sai ga Azumi a saman drower na hau can tsililiko ina reto"
Dariya kawai yake, da jin labarin ya san dama tabbas a rina wai an saci zanin mahaukaciya dan ba za a ƙarƙe ƙalaw ba da Inna da Imran saboda basa jituwa.
.
"Lallai Inna kin yi ƙoƙari" Ya faɗa had lokacin ya kasa tsaida dariyarsa, Ashrof ma sai tayashi take duk da Sadiya ta bata labari amma sai ta ji kamar yanzu ne ake farkon jin labarin.
"Kai Abida baka cin ribar zance ne, ka tsaya ka ji yadda ta kaya mana tsakanin ni da Imirana ai bai fa ci bulus ba, mutuminka na sanya Sadiya ta ƙwala masa kira lokacin ya sha dariyarsa ya more, a raina na ce bakin dariya shi ne na kuka, ai yana shiga ɗakin na shammacesa a janyo Halima muka fito na bankeshi a ɗakin, kira yake Inna ki buɗe dan Allah, aikuwa na yi kunne uwar shegu na ce sai na rama sai da ya horu sosai a ɗakin na buɗe, ka san ya na ga Imirana" Ta faɗa tana dariya, su ma dariyar suke har Sadiya da ta kasa riƙe tata dariyar, hakan ya sanya Imran ya shigo yana ta sallama basu ji ba da yake bai wani ɓuga maganar ba dama jikinsa ya bashi ana cin namansa a gidan tun da ya ga motar Abid a waje ya san Inna tana nan tana bada labarinsa.
"Yana laɓe a jikin bango yadda ka san ƙadangare ya rakuɓe a waje ɗaya sai maƙyarƙyata yake kamar kazar da bazai ya kamata" Ai gabaɗaya suka ɗauki dariya har Inna a dai dai nan Imran ya shigo falon sai haɗe rai yake kamar zai kai musu duka.Ɗif suka daina dariyar sai Abid da ke ƙoƙarin danne dariyar taƙi tsayawa har ruwa idanunsa suka kawo saboda dariya sosai yake hango yadda abokin nasa ya yi, a rakuɓe a ɗakin ga kuma miciji a gefe, tsaf Inna ta iya bada labari yadda mai sauraro zai ji kamar a gabansa ake yi.
"Abokina ka dawo? Ka ganni kamar an jefoni daga sama ko ban maka waya ba" Cewar Abid yana goge ƙwallar idonsa da dariya ta sa ta taru. Wani mugun kallo Imran ya masa wanda ya sanya wata dariya ta ƙwacewa Abid aikuwa ya sakikayarsa dan ya kasa riƙeta.
"Ai abin akwai abin dariya Abida dan ma ba a gabanka aka yi ba" Inna ta faɗa tana dariyar dan ganin Imran ma sai ta sake ƙara ƙarfin dariyarta dan ta ƙular dashi tun da shi bai san abin arziƙi ba.
"Yo da kana siyo min É—an goro da turmin zane, ai da na É—an rangwanta maka ka san zuciya tana son a kyautata mata" Cewar Inna a zuciyarta a fili kuma ta ce.
"Kallai abin arziƙin da abokinka ya kawo min, wancan na gaban Asharofa kuma ya ƴaƴanka ne da matarka"
"Ta faɗa tana kallon Imran da ke ƙoƙarin ajiye ledojin da ya shigo da su.
"An gode" Kawai ya ce tare da juyawa zai fita.
"Amma kuwa yau nan tabbatar ta mugun halin ka Imirana ace a kawo wannan uban kayan kuɗi amma ka yi godiya ƴar mitsitsiya, ina laifin ma ka ce an gode madalla Allah amfana Allah saka da alkairi ya bar zumunci, ka ƙara da cewa kai amma kayan sun yi kyau sosai har da Inna ma aka kawo wa to madalla, amma dan baƙinciki kake min kuma da baƙin halinka Imirana shi ne ka ce an gode a takaice" Cewar Inna tana gatsinen gefen hanci.
"Haba Inna ai tsakaninmu ba godiya" Cewar Abid a fili yana ƙara maƙe dariyarsa. A zuciyarsa kuma ya ce na tabbata Imran ya ji Inna tana bada labari amma babu yadda zai yi da ita, kuma gashi magana take faɗa masa a kan ƙin doguwar godiya kuma ba yadda zai yi da ita lallai Inna ita ce maganin Imran.
"Ka ji ɗan arziƙi irin albarka, wallahi kana birgeni Abida...
"Idan ka gama neman maganar ka same ni a waje" Imran ya katsewa Inna maganarta yana kallon Abid tare da ficewa cikin ɓacin rai.
"To ina fitowa " Cewar Abid yana bin bayan Imran da kallo dariya na cinsa.
"Kai rabu da shi yana ta ƙuncin rai ka yi zamanka a nan mu sha hira in maka abin ban faɗa maka ba" Cewar Inna tana kallon Abid.
"To Inna"
"Ashrof miƙa masa yaran ya gan su" Sadiya ta faɗa cikin sanyin murya dan yadda ta ga Imran na harararta da ya shigo hakan ya sanya ta gane bata kyauta ba da aka zauna da ita ana bada labarinsa suna dariya.
"Lah ta barsu ma tun da bacci suke kar a tashe su, ai ni nan tunda gidan zuwa na ne na gansu wata rana"
"Kana ji ko Abida jiya kurman abokin nan naka ya kawo abokinsa Sojojo"
"Inna meye kuma Sojojo ko suna ne?"
"Ina kai ka, baka cin ribar zance"
"To ina jinki Inna"
"Nake faÉ—a maka Sojojo ne dan bana kirashi Soja ba saboda ragwantarsa"
"Ragwanta kuma Inna"
"I mana" Inna ta faÉ—a tana kwashe duk yadda aka yi da Abdallah da ya zo barka da matarsa.
"Inna haka aka yi ashe haÉ—e su kika yi, kai abokina ba dama" Ya faÉ—a yana dariya
"Kai dai bari yo shi ma Imiranan ranar nan fa suma ya yi saboda Hassan ya sawaya ya zama miciji a jikinsa" Ta faɗa tana dariya. Haka suka sha ta dariyarsu har cikin Abid yana ƙullewa dan ya ma manta Imran na jiransa a waje. Sai can ua tuna ya musu sallama ya sanya hannu a aljihu ya ɗakko dubu ɗaya ya miƙawa Inna. Hannu ta sanya ta karɓa tana washe baki.
"Haba Abid ai da ka barshi hidimar ai ta yi yawa " Cewar Sadiya cikin jin nauyin Abid.
"Lah ba kamai ai...
"Rabu da ita kawai in banda baƙinciki meye wata dubu ɗaya dan ya bani kyauta zaki wani haƙiƙice kina cewa ya yi hidima ai dama kowa ya san ya yi hidima musamman da ya fi mijinki da bai san ya siye zuciyar mutane da kyauta ba sai baƙin hali da na zuciya fal ransa" Ta faɗa tana sanya dubun a cikin ƴar pos ɗinta.
Dariya Abid ya yi jin abin da Inna ta ce haka kawai shi ds a ce za a barshi da Inna da ya huta d shiga damuwa ko ɓacin rai, saboda ita bakinta ba ya shiru kuma bata gajiya da abin dariya duk da ita tana yin komai dan raha ne.
"To Inna sai kwana biyu"
"Kwana biyu fa Abida sai ka ce an maka baki, yanzu sai ka iya kwana biyu baka zo mun gaisa ba, ai baka ji daÉ—in da na ji ba da ka bani bugun Abujar nan"
" To Inna idan na samu dama da lokaci zan ke leƙowa "
"To nagaode sosai" Ta faɗa lokacin da ta fito har ƙofar falon Abid ya sanya takalminsa ya fita.
"Oh ɗan nan da kirki yake Sa'adiyya ya fi min mijinki Imirana sau miliyan ma" Cewar Inna lokacin da ta zauna a kan kujera tana ƙara ganin atamfarta.
"Inna dan Allah kike iya bakin ki idan abokan Imran sun zo kin ga ko a fuska ya nuna ba ya so kina shiga shirginsu" Cewar Sadiya cikin lallaɓawa dan ta san Inna hukuma ce sai da lallashi.
"Imran ko Inna"
"Shi mana, bari ma na baka labarinsa, amma sai na fara baka daga farko ranar da na kwana ban yi bacci ba"
"Baki yi bacci ba fa Inna, garin yaya?"
"Wallahi fa Abida, haka kawai ban ji ba ban gani ba,ina ranar da ka kawo mu daga asibiti har nake baka labarin abokin Imirana wanda ke wasarere da jikinsa"
"Eh Inna na tuna"
"To wallahi a ranar nan ni na san irin kwanan da na yi a gidan nan" Ta faɗa tana share ƙwallah.
"Subhanallahi Inna ba dai a waje kika kwana ba da sanyin nan?"
"Haba Abida ana ga yaƙi kana ga ƙura yo ba gwara a saka ni a randa ba in kwana da irin kwanan da na yi ranar nan kai ni dai sai da na ji ina ma ban taho ZAMAN WANKAN nan ba, ni da na kwana a tsakanin katako sama katako ya tokare ƙasana katako "
"Katako kuma Inna"
"Yo a ƙarƙashin gado fa na kwana, bayan nna nawa da gado ya matse yadda ka san an yiwa mota lodin shanu haka na ji, wallahi ba dan na shafa man zafi ba da Allah kaɗai ya san me zai faru.
" Ta faɗa tana ɓantarar goron da fa ɗauka daga cikin wanda aka kawo mata ta ƙulle ledar.
"Garin yaya?"
Shiru ta ɗan yi dan bata son faɗar gaskiyar dalilin da ya sa ta kwana a ƙasan gado dan har yau bata daina jin tsoron aljanin ba kuma har yau tana ganin kamar dai yana kallonta a gidan.
"Sanyin garin nan ya sa na kwana a ƙasan gado" Ta faɗa tana ƙara gutsurar goro fuskarta ɗauke da damuwa.
"Sanyi fa Inna, lallai sanyi bai kyauta ba" Ya faɗa yana dariya dan ya fuskanci bata faɗi gaskiyar abin da ya sa ta kwana a ƙasan gadon ba dan daga yadda ta faɗa ya san ta faɗa ne kawai, ga kuma
yadda take bada labarin ma kaÉ—ai abin dariya ne.
"Sanyi mana, ai ba fa shi ne abin da na fuskanta ba kaɗai, ka san Hassan ya zo da baiwa a jikinsa wato haka kawai sai yaro ya ringa saɓaɓa-saɓa ya bar ainihin halittarsa ya koma ta miciji"
"Miciji Inna" Ya faÉ—a da yana son tabbatarwa dan ya san dai Imran ya xe fatar bayan yaron ta miciji ce.
"Miciji mana, ai a washe gari da haihuwarsa ya koma miciji da kan mutum amma saboda rashin imani na Imirana haka ya garƙameni da micijin nan a ɗaki tun ina neman ɗauki har na gaji, ya sanya na rinƙa karanta alif an baki waw zal, kai daga ƙarshe dai sai ga Azumi a saman drower na hau can tsililiko ina reto"
Dariya kawai yake, da jin labarin ya san dama tabbas a rina wai an saci zanin mahaukaciya dan ba za a ƙarƙe ƙalaw ba da Inna da Imran saboda basa jituwa.
.
"Lallai Inna kin yi ƙoƙari" Ya faɗa had lokacin ya kasa tsaida dariyarsa, Ashrof ma sai tayashi take duk da Sadiya ta bata labari amma sai ta ji kamar yanzu ne ake farkon jin labarin.
"Kai Abida baka cin ribar zance ne, ka tsaya ka ji yadda ta kaya mana tsakanin ni da Imirana ai bai fa ci bulus ba, mutuminka na sanya Sadiya ta ƙwala masa kira lokacin ya sha dariyarsa ya more, a raina na ce bakin dariya shi ne na kuka, ai yana shiga ɗakin na shammacesa a janyo Halima muka fito na bankeshi a ɗakin, kira yake Inna ki buɗe dan Allah, aikuwa na yi kunne uwar shegu na ce sai na rama sai da ya horu sosai a ɗakin na buɗe, ka san ya na ga Imirana" Ta faɗa tana dariya, su ma dariyar suke har Sadiya da ta kasa riƙe tata dariyar, hakan ya sanya Imran ya shigo yana ta sallama basu ji ba da yake bai wani ɓuga maganar ba dama jikinsa ya bashi ana cin namansa a gidan tun da ya ga motar Abid a waje ya san Inna tana nan tana bada labarinsa.
"Yana laɓe a jikin bango yadda ka san ƙadangare ya rakuɓe a waje ɗaya sai maƙyarƙyata yake kamar kazar da bazai ya kamata" Ai gabaɗaya suka ɗauki dariya har Inna a dai dai nan Imran ya shigo falon sai haɗe rai yake kamar zai kai musu duka.Ɗif suka daina dariyar sai Abid da ke ƙoƙarin danne dariyar taƙi tsayawa har ruwa idanunsa suka kawo saboda dariya sosai yake hango yadda abokin nasa ya yi, a rakuɓe a ɗakin ga kuma miciji a gefe, tsaf Inna ta iya bada labari yadda mai sauraro zai ji kamar a gabansa ake yi.
"Abokina ka dawo? Ka ganni kamar an jefoni daga sama ko ban maka waya ba" Cewar Abid yana goge ƙwallar idonsa da dariya ta sa ta taru. Wani mugun kallo Imran ya masa wanda ya sanya wata dariya ta ƙwacewa Abid aikuwa ya sakikayarsa dan ya kasa riƙeta.
"Ai abin akwai abin dariya Abida dan ma ba a gabanka aka yi ba" Inna ta faɗa tana dariyar dan ganin Imran ma sai ta sake ƙara ƙarfin dariyarta dan ta ƙular dashi tun da shi bai san abin arziƙi ba.
"Yo da kana siyo min É—an goro da turmin zane, ai da na É—an rangwanta maka ka san zuciya tana son a kyautata mata" Cewar Inna a zuciyarta a fili kuma ta ce.
"Kallai abin arziƙin da abokinka ya kawo min, wancan na gaban Asharofa kuma ya ƴaƴanka ne da matarka"
"Ta faɗa tana kallon Imran da ke ƙoƙarin ajiye ledojin da ya shigo da su.
"An gode" Kawai ya ce tare da juyawa zai fita.
"Amma kuwa yau nan tabbatar ta mugun halin ka Imirana ace a kawo wannan uban kayan kuɗi amma ka yi godiya ƴar mitsitsiya, ina laifin ma ka ce an gode madalla Allah amfana Allah saka da alkairi ya bar zumunci, ka ƙara da cewa kai amma kayan sun yi kyau sosai har da Inna ma aka kawo wa to madalla, amma dan baƙinciki kake min kuma da baƙin halinka Imirana shi ne ka ce an gode a takaice" Cewar Inna tana gatsinen gefen hanci.
"Haba Inna ai tsakaninmu ba godiya" Cewar Abid a fili yana ƙara maƙe dariyarsa. A zuciyarsa kuma ya ce na tabbata Imran ya ji Inna tana bada labari amma babu yadda zai yi da ita, kuma gashi magana take faɗa masa a kan ƙin doguwar godiya kuma ba yadda zai yi da ita lallai Inna ita ce maganin Imran.
"Ka ji ɗan arziƙi irin albarka, wallahi kana birgeni Abida...
"Idan ka gama neman maganar ka same ni a waje" Imran ya katsewa Inna maganarta yana kallon Abid tare da ficewa cikin ɓacin rai.
"To ina fitowa " Cewar Abid yana bin bayan Imran da kallo dariya na cinsa.
"Kai rabu da shi yana ta ƙuncin rai ka yi zamanka a nan mu sha hira in maka abin ban faɗa maka ba" Cewar Inna tana kallon Abid.
"To Inna"
"Ashrof miƙa masa yaran ya gan su" Sadiya ta faɗa cikin sanyin murya dan yadda ta ga Imran na harararta da ya shigo hakan ya sanya ta gane bata kyauta ba da aka zauna da ita ana bada labarinsa suna dariya.
"Lah ta barsu ma tun da bacci suke kar a tashe su, ai ni nan tunda gidan zuwa na ne na gansu wata rana"
"Kana ji ko Abida jiya kurman abokin nan naka ya kawo abokinsa Sojojo"
"Inna meye kuma Sojojo ko suna ne?"
"Ina kai ka, baka cin ribar zance"
"To ina jinki Inna"
"Nake faÉ—a maka Sojojo ne dan bana kirashi Soja ba saboda ragwantarsa"
"Ragwanta kuma Inna"
"I mana" Inna ta faÉ—a tana kwashe duk yadda aka yi da Abdallah da ya zo barka da matarsa.
"Inna haka aka yi ashe haÉ—e su kika yi, kai abokina ba dama" Ya faÉ—a yana dariya
"Kai dai bari yo shi ma Imiranan ranar nan fa suma ya yi saboda Hassan ya sawaya ya zama miciji a jikinsa" Ta faɗa tana dariya. Haka suka sha ta dariyarsu har cikin Abid yana ƙullewa dan ya ma manta Imran na jiransa a waje. Sai can ua tuna ya musu sallama ya sanya hannu a aljihu ya ɗakko dubu ɗaya ya miƙawa Inna. Hannu ta sanya ta karɓa tana washe baki.
"Haba Abid ai da ka barshi hidimar ai ta yi yawa " Cewar Sadiya cikin jin nauyin Abid.
"Lah ba kamai ai...
"Rabu da ita kawai in banda baƙinciki meye wata dubu ɗaya dan ya bani kyauta zaki wani haƙiƙice kina cewa ya yi hidima ai dama kowa ya san ya yi hidima musamman da ya fi mijinki da bai san ya siye zuciyar mutane da kyauta ba sai baƙin hali da na zuciya fal ransa" Ta faɗa tana sanya dubun a cikin ƴar pos ɗinta.
Dariya Abid ya yi jin abin da Inna ta ce haka kawai shi ds a ce za a barshi da Inna da ya huta d shiga damuwa ko ɓacin rai, saboda ita bakinta ba ya shiru kuma bata gajiya da abin dariya duk da ita tana yin komai dan raha ne.
"To Inna sai kwana biyu"
"Kwana biyu fa Abida sai ka ce an maka baki, yanzu sai ka iya kwana biyu baka zo mun gaisa ba, ai baka ji daÉ—in da na ji ba da ka bani bugun Abujar nan"
" To Inna idan na samu dama da lokaci zan ke leƙowa "
"To nagaode sosai" Ta faɗa lokacin da ta fito har ƙofar falon Abid ya sanya takalminsa ya fita.
"Oh ɗan nan da kirki yake Sa'adiyya ya fi min mijinki Imirana sau miliyan ma" Cewar Inna lokacin da ta zauna a kan kujera tana ƙara ganin atamfarta.
"Inna dan Allah kike iya bakin ki idan abokan Imran sun zo kin ga ko a fuska ya nuna ba ya so kina shiga shirginsu" Cewar Sadiya cikin lallaɓawa dan ta san Inna hukuma ce sai da lallashi.