← Book details Surbajo Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 26

Sashe 17

Surbajo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

tsawon shekara biyu da auransu bata taba zuwa gidaba Amman yanxu tace zata shine zece tajirashi

Kiranta alameen yayi yanamata gargadi akan karta sake tatafi seyazo ayko rufe ido tayi tanata fada hardacewa in akan babynkane kahanani zuwa asalina tozanbarmakashi agida inje nikadai danna fahimci kana gudun innaje dashi ruga ze cutu ne to ni kabarni inje tunda ni dama acan nataso maganganude marasa dadi tafadamasa
alameen runtse ido kawai yayi yana sauraronta ranshi namishi kuna
kashe wayar yayi yahiga tunani
tabbas surbajo tayi gaskiya beso taje da Yusuf rigar gudun yakamu da wani ciwon shiyasa beson taje sedashi to amma ay Tunda befadamataba bedace tafadamasa maganaba har haka

itama surbajo sebayan yakashe wayarne hankalinta yatashi tuno irin maganganun data fadamasa tabbas bata kyautaba kiranshi tashigayi tabashi hakuri Amman fafur yaki daukar wayar
tamasa text shima baamsa
.hankalinta tashi yayi tashiga rusa kuka har mommy tashigo dakin tasameta tambayarta abinda yafaru tayi bata boyemataba tafadamata abinda tayimasa murmushi mommy tayi tacr baki kyautabs surbajo Amman kibari zanmasa mgn konan gaba Karki sake yimasa irin haka kinjiko
sosai surbajo tagamsu da zancan mommy i[truncated by WhatsApp]
🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀
*SURBAJO*
🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀

Zahra Muhammad mahmud

*page 57-58*

Waya mommy tadauka takira al-ameen,bayan sungaisa, hakuri tabashi akan abunda surbajo tamasa.
Godiya yayiwa mahaifiyartashi, sannan sukayi sallama bayan yatabbatarmata da yahakura.

Surbajo murna tayi dajin yahakuran, sabida duk abinda sukecewa taji don wayar a speaker take.itama godiya tayiwa mommy tare da alkawarin bazata kumaba.

Tundaga ranar,surbajo kotakirashi awaya,baya sakin jiki suyi hira kamarda, sede yatambayi lafiyar danshi shikenan.
Abun yanama surbajo zafi Dan bata Saba irin hakan dashiba.

Yauma kamar kullum,kiranshi tayi awaya suna gama gaisawa yafara kokarin kashe wayar,dasauri surbajo tace,
"Abban Yusuf Don girman Allah kayimin afuwa, nasan namaka laifi amma zuwa yanzu yadace kayimin afuwa kodan darajar mommy datasa baki please"
Karashe zancan tayi Tana kuka.
Al-ameen baze iya jure jin kukantaba,zuciyarshi zafi takeyi jin kukan surbajo akunnensa.dasauri yakashe water.

Surbajo kifewa tayi agurin Tana kuka,kukantane yatashi Yusuf dake baccinsa hankali kwance. Mika hannu tayi tadaukoshi tasamishi nono abaki yafara sha itakuma taci gaba da kukanta.

Al-ameen jiyayi gaba daya garin yaisheshi, dama next week yake saran zaa bashi hutu, Dan haka jiyayi kamar tayi tsuntsuwa yaje gareta yakeji.

Ranar jummaa dawuri yashirya yabar garin, Dan karfe takwas ta Safiya a kaduna tamasa, besanar Dakowa zuwanshiba Illa driver dinsa,kaitsaye gidan iyayensa yanusa, sunyi mamakin ganinsa,bayan yagaishesune yawuce dakin da madam take.

Tana kwance Tana kuka, yayinda yusuf keta bacci. karasawa yayi gurinta yazauna agefenta.
jin motsin mutum ne yasata fara goge hawayenta dasauri Dan tadauka mommy ce kosu munawwara.

Suman kwance tayi da ganinsa, fuskarta take mitsikewa Dan Tana zaton gizo yakemata

"kukan mekikeyi?

shuru tayi masa Tana goge hawayenta .
Kamota yayi yarungume,aykamar jira take ,rushemishi tayi dakuka Tana fadin
" haba dear,Ashe nangabama zaka iya rabuwa Dani har abada kenan,nace kayi hkr amma kaki Kayi, yakakeso inyi da raina?

Bakinsa yasa acikinnata, dan bayason maganar datakeyi, soyake yamantar da ita bacin ran,kuma dama yamata hakanne gudun karta samu kafar rainashi, tadunga fadamasa magana son ranta kamar Aisha.

surbajo jin bakinsa acikin bakinta yasa kukanta yatsaya, tuni gyaran da mommy taimata yafara ayki, dan sosai mommy take gyaratada magunguna masu kyau, shiyasa itama yana fara yimata kiss din, itama Tashiga maidarmishi da martani.

ganin suna neman wuce gurine yasa takwace kanta dakyar Tana maida numfashi.

shiko Al-ameen rasa yazeyi yayi, Dan gabadaya hankalinshi yagama tashi burinshi yakeba da matarshi.

Mikewa yayi yadauki Yusuf sannan yace mata

"dauko gyalenki mutafi gida"

surbajo jiki har Bari yake gurin neman gyalen, Dan harga Allah tagaji dazama gidan iyayensa,wajen watansu uku agidan.

jakar kayansu tajawo,yana gaba Tana biye dashi abaya har zuwa falo,boyewa tayi abayan Al-ameen, Dan abun da kunya,Amman bata da zabin dayawuce tabi mijinta.

gabadaya falon kallonsu kawai sukeyi,bakunya Al-ameen yace

"mu munwuce gida seda safenku"

dariya gabadaya falon akasa,itade surbajo Tana boye abayanshi tarufe fuska tamkar Amarya.

mommy tace "to Allah yabamu alkhairi shugaban marasa kunya,matar tazo wanka shine bazaka jira amaidatabako?

dariya yayi,sannan yace "mommy to aydama nine nakawota dakaina,kinga balaifibane danmuntafi kuma tare yanzu".

daddy dariya yayi sannan yace "baruwanki dasu, aminullahi kuje abinku Allah yatashemu Lfy".

Dagudu surbajo tafice afalon, mommy nacewa tatsaya suyi sallama, amma ina tuni tafice Dan batason Su hada ido da mommyn.

Al-ameen jakar kayan da surbajo tagudu tabari yaja da hannu daya, dayan hannun kuma yana dauke da Yusuf,yamusu sallama yafice yabarsu sunata faman tsokanarshi.

Amota yasameta,direbansa yasamasa jakar abaya, sannan yabude masa baya yashiga inda surbajo take,direban yazagayo yatada motar suka fice.

Seda taji anfara tafiya tadago fuskarta, Dan Tunda tafito take rufe da fuska. Murmushi tayi Tana kallon Al-ameen Wanda yadage dayiwa Yusuf wasa.dagowa yayi yakalleta sannan shima yayi dariya ,sannan yace,

"wallahi ko alabari bantaba cin Karo da mara kunyar mejego irinkiba.kubiyu kawai nasani, daga ke se indon kauye ta Ali nuhu, masu gudowa daga gida tunkamin amaidosu dakunan mazajensu .yafadi yana dariya.cuno bakinta tayi alamar shagwaba tace,

"au hakama zakaceminko? nagode .baka ma barni da kunyar su mommy ba, shine zaka soma yimin tsiya, ay gwanda ni akan indon kauyen, ni mijinane yaje yadaukoni,itako gudowa tayi,
Kuma ba laifinkabane, laifinane dana biyoka, Danhaka ni asaukeni Nakoma. Tafadi Tana shirin yin kuka.
Dasauri yarungumota tagefe, fadi yake,"kirufamin asiri my baby don Allah, inkika koma can kuma yakikeso inyi dawannan nauyin?

"kaje matarka tasaukemaka"
Tabashi amsa.

kara rukota yayi sannan yaradamata akunne," no baby wannan lodin nakine, Dan haka dole kece me saukeshi .

duka takaimasa nawasa hakade suketafaman raha a motar har suka [truncated by WhatsApp]
🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀
*SURBAJO*
🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀

Zahra Muhammad mahmud

*this page is dedicated to Aisha Usman,baidau,maman Huzaifa,jidda,baby,mrs smart,nafi Muhd Katsina,eshat Mustapha,fatima Muhd kaduna,raihanat,ummu basma,hajara Abdullahi, Fiddah,maman Mashkur thanks you all,I salute you all*👮

*page 63-64*

Yanzu Aisha laulayi yayi sauki,bakamar da ba,iskanci kuma da takama da cikin se abunda yayi gaba,musamman datayi scanning,akace mata namiji zata haifa, karkuso kuga rawar kafa, kawayenta kullum suna gidanta wai sunje jinyarta,abun namata dadi,yadda kawayennata ke bata kulawa,

Al-ameen tuni yagama siyayyar kayan baby,haihuwar kawai suke Jira,yanzu duk weekend a kaduna yakeyi sabida cikin Aisha daya tsufa,

Surbajo tamaida hankalinta kan karatunta, Sam bata wasa dashi ko kadan,shiyasa al-ameen kekara sonta,dan har cikin ranshi yana takaicin rashin karatun Aisha,Wanda ita ko ko ajikinta.

Wata safiyace aisha ta tashi da ciwon nakuda, Allah yataimaka lokacin Al-ameen yazo weekend,
Ihu tadunga yimasa kamar zatayi hauka, duk yabi yarude,agigice yayi asibiti da ita,suna zuwa aka shiga da ita dakin labour.

waya yaciro yakira mamanta, bajimawa tazo asibitin,shuru har yanzu Aisha bata haihuba,se addu'a sukeyi,zuwacan likitan ta fito dasauri,gurinta suka nufa suna tambayarta ya Aishan take,zufa tashare sannan tace musu bleeding takeyi ,dan haka Tana bukatar jini da gaggawa, inba hakaba anything can be happen,
Tahaihune? suka tambayeta arude, as tabasu amsa kuyi sauri kukawo Jinin ko kuma ku biya akwai nasiyarwa,
bamason nasiyarwa muje adebi nawa am group o±,
Donor ne ni,
Bamusu suka nufi lab dashi, bayan sun aunashi suka tabbatar bawata matsala, sannan suka dibi jinin,akaje akasawa Aisha,

Allah gamu gareka,aishafa nacikin mawuyacin hali, duk me imani yaganta ze tausaya ,likitoci sunyi iya yinsu wajen ganin tahaihu da kanta,amma ina dole se ammata cs.

Gurin al-ameen sukazo,wanda yazuba uban tagumi hankalinshi atashe,burinshi Allah yasauketa Lafiya,kiranshi office doctor din tayi,tayimasa bayanin abinda ke faruwa,ba musu yasa hannu a takardar cs din gami da fatan Allah yasa ayi asa'a.

Gurin mamanta yazo yamata bayani,kuka tasa, Tana adduar Allah yafito da Aishan Lfy,

Sunanan zaune akafito da Aishan fuskarta dauke da oxygen a hanci alamun numfashinta be wadataba,zaa kaita dakin operation,mamanta kuka tasa Tana mata addu'a,duk juriya irinta soja,Al-ameen komawa yayi kamar yaro, kuka yake sosai yana mikawa Allah rokonshi,

Ankwashe sama da awa biyu,sannan likitocin suka fito,dasauri,su al-ameen suka nufesu,tamvayarsu Al-ameen yake ya aisha take,daya daga cikin likitocinne yace,she is fine,but am sorry to say,we lost the baby,
Godiya ga Allah Al-ameen yayi, daya tsallakar da Aishan siratsi,yayinda agefe daya kuma yanajin dacin mutuwar babyn,gamida tausayawa Aishan duba da ganin yadda ta dora buri akan dan.

doctor ne yakatseshi dacewa yanason ganinsu a office akwai magana,dasauri suka bi bayanshi zuwa office din,hakuri yasoma basu sannan yace Aisha tawahala da yawa wanda hakan baason faruwarsa ga me nakuda, kuma hakan yafarune sakamakon shan kwayoyin hana daukar ciki datayi amfani dasu acan baya, sanadin hakanne yajawo mahaifarta tasamu matsala inde bawani ikon Allah ba ze wuya tasake haihuwa arayuwarta,
Al-ameen gaba daya rikicewa yayi ,dajin zancan likitan,haka mamantama,hakuri doctor din yadunga basu daga karshe yabasu takardar data tabbatar da bincikennasu,

Bayan Sun baro office din doctor, dakin daaka kwantar da Aishan bayan anfito da ita daga operation din suka shiga,tana kwance Tana bacci, har yanzu akwai oxygen din a hancinta,tausayintane yakamasu duka,

suna nan zaune aka kawo musu gawar babyn Rufe cikin shawul kamar me rai, Al-ameen ne yaamsheshi yabudeshi,wasu hawayen ne suka zubomasa, ganin babyn ba inda yabaro Yusuf, maana shima dashi yake kama,mamanta yaba itama tagani tamasa addu'a,wayarsa yaciro yadunga daukar babyn hoto,sannan yaamsheshi yatafi gida domin amasa sutura,

gidan iyayensa yakai gawar suma suntausayawa Aishan gamida yimata fatan samun sauki, shikuma Allah yajikansa, bayan sun shirya yaron suka masa sallah,makabarta suka nufa domin birneshi,itakuma Momy ita Da amal,da matar kabeer asibitin suka nufa,domin dubo[truncated by WhatsApp]
🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀
*SURBAJO*
🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀

Zahra Muhammad mahmud

*This page is dedicated to Maman gidado,juwairiyyatu,maman Irfana, Hafsat Dahir,maman Muallim, Mrs Lukuman,mrs Shamsur.thanks for the care and support am really appreciate it*

*page 61-62*

Tunda Al-ameen yadawo da surbajo gidan kullum ba
ranar banza da Aisha bazata nemi surbajo da rigimaba. Itako bata kulata ko kadan,lokuta da yawa dakinta take shigewa tabarta Tana 'ba'batu.

Yau asabar tun safe surbajo keta shiri,sabida Al-ameen yace, tashirya suje makarfi,murna gurin surbajo baa magana,kamin Tara tayi tuni tagama shiryawa ita Da Yusuf,oga kawai take jira yafito,dayake ba girkinta bane Aisha ce dashi,

Se karfe goma Al-ameen yafito cikin shirinshi na tafiya,lokacin surbajo duk tagama kosawa,koda yashigo dakinta, kauda kanta tayi gefe, ita ala dole tayi fushi.

Karasawa yayi kusa daita,yaruko hannunta yace,

"haba my charming princess, menayi kuma ake fushi Dani?

Turo bakinta tayi gaba, alamun shagwaba,tace,

"ay bandauka yanzu zaka fitoba,nadauka se wata safiyar,

Dariya yayi kawai,azuciyarshi yasan kishine yamotsa nanko batasan shikadai yakwanaba.amma afili cewa yayi,"am so sorry baby it will never happen again OK, yadaga mata gira daya😉ya kashe ido daya.
Chapter 17 · 0% Book details