Sashe 24
Rahima Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read
23
Karfe goma sha daya na dare ya isa gida amma har zuwa lokacin Zuwaira bata koma ba, ya tube ya shiga wanka ya fito ya hada ruwan shayi tukunna kafin ya zauna kallon tv
Sai sha biyu saura na dare yaji maigadi na bude mata gate din gida ta shigo da motarta.
Ko da ta shigo falon bata lura yana kwance bisa settee ba, tana tafe tana 'yan wake-wakenta, sai wani irin kamshin turare Mai shegen haea Kai take, har zata wuce bedroom ta gansa taja ta tsaya masa kerere bisa Kai "Oh ashe ka dawo ban lura da motarka ba."
Ance tankawa yabawa biyan bashin matsiyaci, bai ce Mata uffan ba, ta fasa shiga ciki ta dawi ta zauna kusa dashi ta fara kame-kame, kusan minti biyar tana ta surutu ba tareda ya tanka ba ta gaji tayi shuru.
Ya kalli matar da suka shafe shekaru fiye da takwas da aure Amma m har zuwa lokacin Nan bai San dadin auren ba, bai San me zai karas ba, ya kanji dai abokansa na hirar hidimar da matayensu keyi musu.
Ya sake kallonta ya rasa me zaice Mata, to bata jin wa'azi, in anyi mata fada ta tashi tana masifa tace an tsaneta, idan aka rarrasheta ta zake har tafi da don haka ya zabi yin biris da ita kawai yafi masa alkhairi ya ci gaba da yi mata addua
Da taga yaki ce mata komi ta mike zata shige ciki harda sakin dogon tsaki...
Takaici ya kamashi kawai ya sakin mata bom "Zuwaira Ina sanar dake Zan Kara aure."
Tayi wani irin juyi gaba daya, hankalinta ya dawo garesa sosai taga Yana kwance lakadan kamar bashi ya furta Mata wadannan kalaman masu dacin gaske ba, ta buga kirji "Aure! Aure fa kace??
Ya amsa "Kwarai ba kince gara inyi ba zai fi Miki nono fari?"
Ta sake buga kirji "Ni din wace sakaryar macece zata ce da mijinta ya kawo Mata kishiya?".
" Sai ke Kuma shawarar taki na dauka."
Amsarsa ya sake tunzurata "Oh ashe zargina ya Zan gaskiya da wace ka aje a waje that's why kake wulakanta ni kana nuna min halin ko in kula."
Yace "Ni ban wulakanta ki ba, ban Kuma ajiye kowacce mace a waje ba don Ni ba fasiki bane."
Tayi tafi " Abokiyar yin naka dai zaka auro a tahi a cakuda min 'ya'ya da shegu."
Ya tashi daga kwance da yaji zata wuce gona da iri yace "Kinga karki batawa yarinyar mutane suna, ba wata daban da baki sani ba Zan aura, ai kinsan Rahima maman Abdul ko,Allah yai nufin ita Zan aura "
Taji dum amma hakan bai hanata yin shewa ba "Ahayye girma ya Fadi, su Yaya babba anji kunya, to daman kace ka gani ka kyasa tuni ba damar yi masa snatching ne da ransa, yo Ashe duk shan mur da kau da Kai na munafunci ne ana so ana kaiwa kasuwa, to me yasa tun farko bka aureta ka barshi ta aureta. Gaske naga danta ya zama dan lelenka sabida son uwa ke sa na d"a. Amma wallahi ka ban mamaki ka bani kunya, ka rasa matar da zaka aura sai matar kaninka Haseeb, wannan abun kunya dame ye kama?"
Maimakon yaji haushin magsnganunta dariya suka bashi yace "Zuwaira wane irin kunya Kan abinda addininmu ya halasta bayan kinsan ance babu kunya a addini? Abinda ya halasta ne mu mutane muke haramtawa kanmu sabida jahilci, to in ba tsintsar jahilci ba Ubangiji ya halasta abu Kai bawa ka kawo al'ada da wasu shirme ka gindaya? So ki fahimci akwai aure tsakanin wa da matar kaninsa idan ya rasu za Kuma ayi shine na sanar dake don shi Alhajinku ma rokona yayi ayi da wuri Kar a dauki lokaci, to na bi shawararsa sai kije kiyi tunanin me kike bukata inyi miki ma fadar kishiya?
Ta tabe baki "Idan duk jikina kunnuwane ba Zan taba yarda cewan Alhajinmu da kanshi zai goyi bayan ka yiwa diyarsa kishiya ba.
"Me zai hana tunda diyar bata neman albarka bata faranta ran iyayenta?"
Ta balla masa harara "Don zaka auro wannan yarinyar ce kake fada min magana?"
Yace "Ke Kika ja yai nisa, and ki bar tunani cewan yarinya karama zan auro shekaru nawa kika bata?"
Ta gatsina hanci "Yo Ashe ma tsohuwa ce kake wannan rawar jikin da dimirgishi Wai dafa kauri ba da."
"Nima ai tsohon ne tinda na na Kai 41 yes Kinga za mu yiwa juna daidai kenan."
Ta kallesa ta watsar "Kaji dashi Wai ciwon ajali a Dan yatsa."
Ya dagi ya kalleta "Please shiga ciki ki kwanta kin dameni da surutu sai da safe."
Tayi kwata "Surutu yanzun na bude chapter sai dai Kuma idan dinke bakina za kayi tunda baka da tausayi a zucci ka yanka ka dinke, Kuma gobe gidanmu za ni."
Ya amsa "Allah ya Kai mana rai suma nemanki suke kije kije ki kwaso yaran da kika zube a can tamkar basu da gata."
Yana fadin haka ya gyara kwanciyar sa nan alamun ba zai ma shiga bedroom din ba balle taci gaba da bala'in.
Ta gaji da zama taja jiki ta nufi ciki tana Kun kunai kamar wata yarinya karama.
10/09/2020, 12:29 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by jami
24
Gari na wayewa ko wanka bata yi ba tana idar da sallah ta nufi gidansu, Kai tsaye ta wuce dakin mahaifiyarta, Hajiyar na zaune tana lazumi don al'adarta kenan.
Ta dago taga Zuwaira ce taci gaba da karatunta ba tare da sake kallon inda take ba, ita kuwa ta haye bisa gadon uwar ta kwanta.
Ba a jima ba taji muryar mahaifinta ya shigo yadda yake yi duk safe ya zagaya dakin kowacce mata yaga yadda ta kwana tareda iyalinta yaji ko tana da wata matsala su tattauna hanyar da zasu bullowa al'amarin.
Ya zauna falon uwargidansa Hjy Lami yana jiran ta kare adduointa, Zuwaira taji muryarsa ta taso ta fito ta durkusa ta gaishe shi. Ya kalleta cike da mamaki "Ba dau Zuwaira nike gani yanzun ba, tun yaushe kika shigo gidan Nan?"
Ta sunkuyar da kai tace "Ban dade da shigiwa ba, ina kwana?"
Ya kalli agogon hannunsa yaga ko karfe takwas bata cika ba cikin tsawa yace "Wace irin sakayyar yarinya ce, ki baro gidan mijinki tun sassafe ki zo me zaki dauka?"
Ta marairaice "Karansa na kawo Baba, wallahi duk ya canza, yanzun ma wai aure zai yi, da karya ma har yana cewa ka bashi goyon baya?"
Uwar ta shafa adduarta ta fito ta durkusa gaban mijinta ta gaisheshi ya amsa kana cikin bacin rai yace "Ya akayi kika Kyaleta a zauna har tana kwanciya miki a dak?"
Hjy Lami ta kada Kai "Yadda ka ganta hakan na ganta ko gaisawa ba muyi ba."
Yace "Mutumiyar banza kina nufin kin kwaso kafafunki ne kinzo muyi miki mene, mu hana sa aure? Wallahi Mamana (haka yake kiranta saboda sunan mahaifiyarsa yasa mata) kin ban kunya, ban taba tunanin ba zaki zauna gidan aureki cikin mutunci ba,yarinya kin zama sai kace goyon arna?"
Hjy Lami tace "Ya za ayi mijinki ya kalleki da mutunci bayan kin zama tamkar maras mafadi?"
Ta saka kuka "Wallahi Mama Haseeb kazafi yake mini."
Alh Muhd ya sake daka mata tsawa "Rufa min baki ko in tashi in tattakaki, wallahi muddin baki canza dabi''unki ba daga yau mun sa kafar wando daya ni dake, bar ganin na sake miki ina ksunarki, zata koma kiyayya tsakaninmu Kuma kin sanni sarai kamar yunwar cikinki, wallahi ko ke kadai na haifa ina iya yafeki har abada don banga amfaninki ba."
Hjy Lami ta kalleta cikin bacin rai tace "Dubeki yarinyarki dake kin bata rayuwarki da kanki ga kinan duk kin jeme kin lalace, Kuma da kike cewa kazafi likitan ke miki su mutanen duniya da kike mu'amala da kawayen banzan da kike hulda dasu duk kazafin ne? Duk inda kika shiga ana ga 'yar wance da wane."
Alh Muhd yace "Dalili kenan da muka bashi goyon bayan ya auro mai mutunci tunda ke kin zubar da naki, idan kinga ba Zaki iya zama dashi ba ga hanya nan bude to banga amfanin zama da igigiyar aurensa a kanki ba, sai kije kiji da zunubi daya."
Uwar ta fashe sa kuka "Alhaji kalli yarinyar nan ka gani ba abinda ta sawa gaba sai burin duniya da kyale-kyale, dan rayuwar da take takaitatta. Wai don Allah wane irin gata ne ba a nuna miki ba? Me kika nema kika rasa a gidanku ko na mijinki? Allah ya hore dukiyar da ake taimakawa wasu ma, to me kike nema ne?"
Maimakon ta nuna alamun nadama sai ta dauko wani zancen da bai danganci fadar da ake Mata "Mama ni gaskiya ba Zan zauna da kishiya ba, kishiyar ma yarinyar data san sirrina, bayan duk wata takama da Haseeb ke yi da wani ji da kai, mahaifina ne silar duk abinda ya samu, duk abinda yake takama dashi Kai dinnan Baba kaine sanadin, ko yana nufin anci moriyar ganga ne za a yarda kaurenta, to gaskiya Baba da sake...
Bata ga mikewarsa ba, ji tayi kawai an dauketa da tafi ta kifa kasa, ya bita ya taka yana zagi, uwar ma ta rufeta da duka, Nan ta fara kwarma ihu sauran matan gidan suka taru don cetonta..
Da kyar da rarrashi aka kwaceta, ko kafin ayi haka fuska ta kumbura jiki ya murzu da duka.
Alh Muhd ya fara haki, jiri ya kwashe shi, matan suka tareshi, akayi hanzarin dauko masa maganin hawan jininsa aka bashi yasha kana suka kamashi ya koma daki ya kwanta.
Hjy Lami ta dawo dakinta ta cimma 'yar nata kuka tace "Ya jikin Baban?"
Ta kalleta ta watsar "Tashi ki bace min da gani, ina ruwanki da jikinsa? Ai kinsan yanada hawan jinin don kece sanadi, to ki dage ki zama kece ajalinsa."
Ta Kara fashewa da kuka "Don Allah Mama ku yafe min, Allah zan daina komi, bacin raine yasa Ni fadin wannan maganar."
"Da gangar kika yi tunda an Sha gargadinki kan furucin da kike yi, yau kika yiwa mijinki gorin? Maras tunani, da kike fadin ubanki ne silar arzikinsa yanzun hidimar da yake mana ya zama ke Kika sa shi? Yarone dan halas da yasan darajar iyayensa da naki."
Karfe goma sha daya na dare ya isa gida amma har zuwa lokacin Zuwaira bata koma ba, ya tube ya shiga wanka ya fito ya hada ruwan shayi tukunna kafin ya zauna kallon tv
Sai sha biyu saura na dare yaji maigadi na bude mata gate din gida ta shigo da motarta.
Ko da ta shigo falon bata lura yana kwance bisa settee ba, tana tafe tana 'yan wake-wakenta, sai wani irin kamshin turare Mai shegen haea Kai take, har zata wuce bedroom ta gansa taja ta tsaya masa kerere bisa Kai "Oh ashe ka dawo ban lura da motarka ba."
Ance tankawa yabawa biyan bashin matsiyaci, bai ce Mata uffan ba, ta fasa shiga ciki ta dawi ta zauna kusa dashi ta fara kame-kame, kusan minti biyar tana ta surutu ba tareda ya tanka ba ta gaji tayi shuru.
Ya kalli matar da suka shafe shekaru fiye da takwas da aure Amma m har zuwa lokacin Nan bai San dadin auren ba, bai San me zai karas ba, ya kanji dai abokansa na hirar hidimar da matayensu keyi musu.
Ya sake kallonta ya rasa me zaice Mata, to bata jin wa'azi, in anyi mata fada ta tashi tana masifa tace an tsaneta, idan aka rarrasheta ta zake har tafi da don haka ya zabi yin biris da ita kawai yafi masa alkhairi ya ci gaba da yi mata addua
Da taga yaki ce mata komi ta mike zata shige ciki harda sakin dogon tsaki...
Takaici ya kamashi kawai ya sakin mata bom "Zuwaira Ina sanar dake Zan Kara aure."
Tayi wani irin juyi gaba daya, hankalinta ya dawo garesa sosai taga Yana kwance lakadan kamar bashi ya furta Mata wadannan kalaman masu dacin gaske ba, ta buga kirji "Aure! Aure fa kace??
Ya amsa "Kwarai ba kince gara inyi ba zai fi Miki nono fari?"
Ta sake buga kirji "Ni din wace sakaryar macece zata ce da mijinta ya kawo Mata kishiya?".
" Sai ke Kuma shawarar taki na dauka."
Amsarsa ya sake tunzurata "Oh ashe zargina ya Zan gaskiya da wace ka aje a waje that's why kake wulakanta ni kana nuna min halin ko in kula."
Yace "Ni ban wulakanta ki ba, ban Kuma ajiye kowacce mace a waje ba don Ni ba fasiki bane."
Tayi tafi " Abokiyar yin naka dai zaka auro a tahi a cakuda min 'ya'ya da shegu."
Ya tashi daga kwance da yaji zata wuce gona da iri yace "Kinga karki batawa yarinyar mutane suna, ba wata daban da baki sani ba Zan aura, ai kinsan Rahima maman Abdul ko,Allah yai nufin ita Zan aura "
Taji dum amma hakan bai hanata yin shewa ba "Ahayye girma ya Fadi, su Yaya babba anji kunya, to daman kace ka gani ka kyasa tuni ba damar yi masa snatching ne da ransa, yo Ashe duk shan mur da kau da Kai na munafunci ne ana so ana kaiwa kasuwa, to me yasa tun farko bka aureta ka barshi ta aureta. Gaske naga danta ya zama dan lelenka sabida son uwa ke sa na d"a. Amma wallahi ka ban mamaki ka bani kunya, ka rasa matar da zaka aura sai matar kaninka Haseeb, wannan abun kunya dame ye kama?"
Maimakon yaji haushin magsnganunta dariya suka bashi yace "Zuwaira wane irin kunya Kan abinda addininmu ya halasta bayan kinsan ance babu kunya a addini? Abinda ya halasta ne mu mutane muke haramtawa kanmu sabida jahilci, to in ba tsintsar jahilci ba Ubangiji ya halasta abu Kai bawa ka kawo al'ada da wasu shirme ka gindaya? So ki fahimci akwai aure tsakanin wa da matar kaninsa idan ya rasu za Kuma ayi shine na sanar dake don shi Alhajinku ma rokona yayi ayi da wuri Kar a dauki lokaci, to na bi shawararsa sai kije kiyi tunanin me kike bukata inyi miki ma fadar kishiya?
Ta tabe baki "Idan duk jikina kunnuwane ba Zan taba yarda cewan Alhajinmu da kanshi zai goyi bayan ka yiwa diyarsa kishiya ba.
"Me zai hana tunda diyar bata neman albarka bata faranta ran iyayenta?"
Ta balla masa harara "Don zaka auro wannan yarinyar ce kake fada min magana?"
Yace "Ke Kika ja yai nisa, and ki bar tunani cewan yarinya karama zan auro shekaru nawa kika bata?"
Ta gatsina hanci "Yo Ashe ma tsohuwa ce kake wannan rawar jikin da dimirgishi Wai dafa kauri ba da."
"Nima ai tsohon ne tinda na na Kai 41 yes Kinga za mu yiwa juna daidai kenan."
Ta kallesa ta watsar "Kaji dashi Wai ciwon ajali a Dan yatsa."
Ya dagi ya kalleta "Please shiga ciki ki kwanta kin dameni da surutu sai da safe."
Tayi kwata "Surutu yanzun na bude chapter sai dai Kuma idan dinke bakina za kayi tunda baka da tausayi a zucci ka yanka ka dinke, Kuma gobe gidanmu za ni."
Ya amsa "Allah ya Kai mana rai suma nemanki suke kije kije ki kwaso yaran da kika zube a can tamkar basu da gata."
Yana fadin haka ya gyara kwanciyar sa nan alamun ba zai ma shiga bedroom din ba balle taci gaba da bala'in.
Ta gaji da zama taja jiki ta nufi ciki tana Kun kunai kamar wata yarinya karama.
10/09/2020, 12:29 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by jami
24
Gari na wayewa ko wanka bata yi ba tana idar da sallah ta nufi gidansu, Kai tsaye ta wuce dakin mahaifiyarta, Hajiyar na zaune tana lazumi don al'adarta kenan.
Ta dago taga Zuwaira ce taci gaba da karatunta ba tare da sake kallon inda take ba, ita kuwa ta haye bisa gadon uwar ta kwanta.
Ba a jima ba taji muryar mahaifinta ya shigo yadda yake yi duk safe ya zagaya dakin kowacce mata yaga yadda ta kwana tareda iyalinta yaji ko tana da wata matsala su tattauna hanyar da zasu bullowa al'amarin.
Ya zauna falon uwargidansa Hjy Lami yana jiran ta kare adduointa, Zuwaira taji muryarsa ta taso ta fito ta durkusa ta gaishe shi. Ya kalleta cike da mamaki "Ba dau Zuwaira nike gani yanzun ba, tun yaushe kika shigo gidan Nan?"
Ta sunkuyar da kai tace "Ban dade da shigiwa ba, ina kwana?"
Ya kalli agogon hannunsa yaga ko karfe takwas bata cika ba cikin tsawa yace "Wace irin sakayyar yarinya ce, ki baro gidan mijinki tun sassafe ki zo me zaki dauka?"
Ta marairaice "Karansa na kawo Baba, wallahi duk ya canza, yanzun ma wai aure zai yi, da karya ma har yana cewa ka bashi goyon baya?"
Uwar ta shafa adduarta ta fito ta durkusa gaban mijinta ta gaisheshi ya amsa kana cikin bacin rai yace "Ya akayi kika Kyaleta a zauna har tana kwanciya miki a dak?"
Hjy Lami ta kada Kai "Yadda ka ganta hakan na ganta ko gaisawa ba muyi ba."
Yace "Mutumiyar banza kina nufin kin kwaso kafafunki ne kinzo muyi miki mene, mu hana sa aure? Wallahi Mamana (haka yake kiranta saboda sunan mahaifiyarsa yasa mata) kin ban kunya, ban taba tunanin ba zaki zauna gidan aureki cikin mutunci ba,yarinya kin zama sai kace goyon arna?"
Hjy Lami tace "Ya za ayi mijinki ya kalleki da mutunci bayan kin zama tamkar maras mafadi?"
Ta saka kuka "Wallahi Mama Haseeb kazafi yake mini."
Alh Muhd ya sake daka mata tsawa "Rufa min baki ko in tashi in tattakaki, wallahi muddin baki canza dabi''unki ba daga yau mun sa kafar wando daya ni dake, bar ganin na sake miki ina ksunarki, zata koma kiyayya tsakaninmu Kuma kin sanni sarai kamar yunwar cikinki, wallahi ko ke kadai na haifa ina iya yafeki har abada don banga amfaninki ba."
Hjy Lami ta kalleta cikin bacin rai tace "Dubeki yarinyarki dake kin bata rayuwarki da kanki ga kinan duk kin jeme kin lalace, Kuma da kike cewa kazafi likitan ke miki su mutanen duniya da kike mu'amala da kawayen banzan da kike hulda dasu duk kazafin ne? Duk inda kika shiga ana ga 'yar wance da wane."
Alh Muhd yace "Dalili kenan da muka bashi goyon bayan ya auro mai mutunci tunda ke kin zubar da naki, idan kinga ba Zaki iya zama dashi ba ga hanya nan bude to banga amfanin zama da igigiyar aurensa a kanki ba, sai kije kiji da zunubi daya."
Uwar ta fashe sa kuka "Alhaji kalli yarinyar nan ka gani ba abinda ta sawa gaba sai burin duniya da kyale-kyale, dan rayuwar da take takaitatta. Wai don Allah wane irin gata ne ba a nuna miki ba? Me kika nema kika rasa a gidanku ko na mijinki? Allah ya hore dukiyar da ake taimakawa wasu ma, to me kike nema ne?"
Maimakon ta nuna alamun nadama sai ta dauko wani zancen da bai danganci fadar da ake Mata "Mama ni gaskiya ba Zan zauna da kishiya ba, kishiyar ma yarinyar data san sirrina, bayan duk wata takama da Haseeb ke yi da wani ji da kai, mahaifina ne silar duk abinda ya samu, duk abinda yake takama dashi Kai dinnan Baba kaine sanadin, ko yana nufin anci moriyar ganga ne za a yarda kaurenta, to gaskiya Baba da sake...
Bata ga mikewarsa ba, ji tayi kawai an dauketa da tafi ta kifa kasa, ya bita ya taka yana zagi, uwar ma ta rufeta da duka, Nan ta fara kwarma ihu sauran matan gidan suka taru don cetonta..
Da kyar da rarrashi aka kwaceta, ko kafin ayi haka fuska ta kumbura jiki ya murzu da duka.
Alh Muhd ya fara haki, jiri ya kwashe shi, matan suka tareshi, akayi hanzarin dauko masa maganin hawan jininsa aka bashi yasha kana suka kamashi ya koma daki ya kwanta.
Hjy Lami ta dawo dakinta ta cimma 'yar nata kuka tace "Ya jikin Baban?"
Ta kalleta ta watsar "Tashi ki bace min da gani, ina ruwanki da jikinsa? Ai kinsan yanada hawan jinin don kece sanadi, to ki dage ki zama kece ajalinsa."
Ta Kara fashewa da kuka "Don Allah Mama ku yafe min, Allah zan daina komi, bacin raine yasa Ni fadin wannan maganar."
"Da gangar kika yi tunda an Sha gargadinki kan furucin da kike yi, yau kika yiwa mijinki gorin? Maras tunani, da kike fadin ubanki ne silar arzikinsa yanzun hidimar da yake mana ya zama ke Kika sa shi? Yarone dan halas da yasan darajar iyayensa da naki."