Sashe 19
Rahima Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read
Rahima ta kanne mata ido guda "Aunty Maryam sarkin mita, ke din ai kike jawowa kanki katon ciki, inda halitta da rashin kulawa, irin naman da kike dankara lafiya ne, ki ci kowanne irin nama, kisha kayan Zaki, kefa duk inda kayan dake Kara kitse suke kina Nan ya ba zaki ajiye teba ba, gaki Nan haihuwa daya kin zama wata guzuma, idan kin Kara sai Alh Abbas ya auro daidai misali don har Hjy Suwaiba barakallsh Masha Allah."
Ta wurgeta da maficin dake hannunta "Shima din ba kiga yadda ya koma ba har tozon wuya ya fara fa."
Rahima tace "Hhmmmm da Rabiu na nan da ya kusan kibar Alhajinku, dubi yadda ya koma kafin rasuwarsa."
Maryam ta shareta, ta sake maimaitawa, a nan ta kalleta tace "Saboda Allah Rahima ba zaki bar wannan bawan Allah ya kwanta makwancinsa lafiya ba, ke kenan da duk aka tada magana sai kin sako zancensa, Ina amfanin haka, adduarmu kadai yake bukata."..
Ta nisa tareda dafe kanta "Nima bana sanin time din da nike ambatonsa Maryam, Ina kokarin dainawa."
. "Ah to gara ki yiwa tufka hanci don ba namijin da zai dauki Yana aurenki kina zancen wani wanda ya rigamu gidan gaskiya."
"Nace miki zan bari, da kike fadin hakan ai mijin fari wuyan mantuwa gareshi, balle ma kowa na aura dole yai hakuri dani."
Ta kalleta a shagube "Sai dai kuwa idan bai sonku, muddin Yana kaunarki zaku rinka Kai ruwa rana ne, Wai ma ba haka ba ya batun Dakta?"
Rahima ta canza nan take "Ki bar batun nan don Allah, ai don in nunawa Hajiyar ba Mai yuwwa bane in har hakan take nufi naki komawa gidanta, har Abdul na bar musu in dominsa suke son aikata abin kunya, ko hausawa sunce ana barin halas....
Maryam ta harareta " Jiya dominki nayi tambaya a islamiyya kan shirmen da kike yi Kuma in fada miki don kin auri Dakta ba abinda ya kaucewa shariar musulumci bane, Malam yace addininmu nai hana wa ya auri matan kani na idan Allah yai masa rasuwa hakan shuma kani na iya auren matsn Wan sa in haka ta kasance.. Har da misalin cewan ko suna da rai ce dayansu ya kamu da rashun lafiyar da ya hana yin sunna da matarsa an nemi magani an rasa na tsawon shekarun da aka gindaya masa zai sahale mata gashi ya yaba hankalinta bai son tabar gidan don kyakkyawar dabi',unta Yana iya yiwa danuwansa maganar cewan iin ya saki shu ya aureta idan sun daidaita tsakaninsu, Kuma auren ya halasta, ke dinma banga abun tada jijiyoyin wuya bayan da bakinki kika fada min kina son Daktan .
Ta kauda Kai "Na dai so mutumin da aka bani labarinsa, da lamarin ya juye Kuma na sanu canjun ra'ayi.
Ta wani kalleta 'Karki kawi mun burgar banza, karyarki wallahi, was yace Miki ana yiwa soyayya yankan kauna, yadda mashin son wancan ya soki kirjinki haka na Daktan zai huda zuciyark tunda batun mutum guda ake in dai dama ba karya kike ba Wanda a sanina ba a karyar so da kauna."
Da taji alamun ta kamo hanya zata kureta saita canza hirar cikin dabara....
Suna cikin hirar suka ji yar karamar muryar Abdul ya shigo a guje Yana fadin 'Mami Kinga jirgina baba ya saya min."
Murnan ganinsa ya rufeta, ta daukeshi tana sumbatarsa "Oyo-oyo Abdul Ina Hajiya?.
Hankalin yaron ma wajen Walida, ganin hakan ta sauke shi, Walidan ta fara kukan sai ya bata jirginsa. Rahima tace Baba ya hada rigima kenan dole gobe inje in sayo miki naki jirgin".
Wani yaro Dan makwabtansu ne ya shigo Yana sallama suka amsa "Wai ance ana Kiran maman Abdul a waje."...
Rahima ta kakki Maryam kinji Kuma Bala da gulma shi daya saba shigowa har cikin gida a gaisa ".
Maryam tace "May be sauri yake, fita kiji in zai koma da Abdul dinne tunda ban gansa da kayansa ba."
Maimakon ta tsaya saka hijab, katon gyalen Maryam ta dauka ta yafa ta fita cikin sauri.
08/09/2020, 13:42 - Anty saliha: ...RAHIMA...doc by jami
19
Tun daga kan soron farko kamshin turaren 'fame' ya fara dukan hancinta, zuciyarta ta fara bugawa cikin sauri, ba dai zarginta zai zan gaskiya ba?
Ta karisa cikin tsakiyar soron gidansu inda tayi arba da *HASEEB* in person, rawar da jikinta ya fara, bai hanata saurin durkusawa cikin ladabi tace "Barka da yini, ya su Aunty Zuwaira?"
Ko kallon arziki bata samu daga gareshi ba
Ya amsa a takaice "Lafiya." Ya shiru
Ta dan jima tsugunne tana jiran taji da wacce ya taho tunda bai taba zuwa gidansu ba.
Da ya tuna bai da wata mafita dole ya fadi dalilin zuwansa kamar yadda yaiwa Mahaifiyarsa alkawari,ya cije, cikin isa da miskillancisa ya tambayeta "Magana ta kawo ni ko zan sami damar Fadi?"
Kamar ta amsa cewan bata da lokacin saurarensa, saita tuna kaninsa,da irin girmansa da yake gani kamar uba ba wa ba, ta tuna dawainiyar da yake dasu, hakan yasa ta hadiye zuciyarta tace "Ba damuwa Ina saurarenka."
Ya gyara tsayiwarsa sosai ya jingine da bango tareda goya hannayensa a kirji yace "Hajiya tace tayi miki bayanin komi don haka ba zan tsaya wani dogon bayani ba tunda kin amince da shirinta nima hakan akan dole yanzun ya rage naki kiyi shawarar yaushe kike ganin ya dace a daura auren?"
Gabanta ya buga rugugu, aure? Haka ake zancen auren cikin isa da kasaitar mulki, aiki jawur, tun kafin tafiya tai nisa bata iya cewa ta fasa, daman ta amsa ne saboda bata san shine ba, wata zuciyar kuma tace zaki zan mai karya alkawari kenan wanda a addinance hakan ya zama munafuci, can ta nisa, tace "Bani da yancin kaina koda nike bazawara, iyayena keda hakkin wannan sai abinda kika ce."
Shi kansa yasan nai kyauta, bai dace ya furta mata wadannan kalaman ba, ba ita ta Kar zomon ba, yaja numfashi yace "Okay zan jira su zartas da shawarwarinsu, nawa iyayen zasu taho in Sha Allah."
Da yaji ba zata kara cewa komi ba,sai ya Kara gyara murya yace "Abdul kuwa bai ji dadi ba amma naga ya warware, dazun jikin yafi masa zafi."
Tana dai tsugunne kanta sunkuye har zuwa lokacin, maganar da yake yi bai sa ta dago ba balle tayi responding.
Ya kada Kai "Ni zan koma, na wani problem ko?'
Ta girgiza Kai.
"Ina Abdul, in koma dashi ko a bar shi?"
sai a nan ta amsa "A tafi dashi, sai an jima a gaida Hajiya Aunty da Zuwaira."
Tana gama magana ta yunkura ta mike ta shige cikin gida ta barshi nan a tsaye.
Tana shiga ta cewa Maryam "Don Allah dauki Abdul ki mika sa waje zasu koma gidane."
Ta kalleta taga fuskar nan tata a daure bata tsaya tambaya ba ta rike hannun yaron suka nufi kofar gidan. Ko da wasa ba tayi zaton shi zata gani ba amma ta danne mamakinta ta gaisheshi, Abdul ya ruga wajensa ya kama hannunsa suka shiga mota suka wuce.
Har tana tuntube wajen saurin komawa cikin gida inda ta isko Rahima ta cika tayi dam, ta kalleta ta tuntsure da dariya tace "Yau Allah ya hadani da famous Dr Abdul-Haseeb Junaid din da ake magana, he's very handsome, ashe ganinsa a zahiri yafi ganinsa a tv."
Rahima ta cafe "May be ganun baiwar kyaun da Allah yai masa da kirar jiki msi kyau ne yasa yake wani ji da kansa."
Maryam tace "Ke fa na lura ba zaki kwantar da hankali ki fahimcesa ba, to komin ji da kansa dai gashi ya taho har gida, ya kuka yi?"
Ta tabe baki "Maganar ma da kyar yake har Yana m fada min shi dole ne ya amince da batun auren Wai Kuma yaushe nike son a daura? Ke kinji wani galari, wallahi ba domin ina ganin mutuncinsu ba da yaji magana daga bakina, darajar Rabiu kawai yaci, ko an fada masa nima da son raina za ayi oho."
Maryam ta tausayawa 'yaruwarta tace 'Gaskiya al'amarin da rikitarwa Rahima amma kiyi hakuri ki rungumi kaddara,Allah da ya shirya faruwan haka daku yasan dalilinsa, mu 'yan tayaku addua ne, ki daure karki dorawa Dakta laifi, shima na tabbatar abin na damunsa dole yaji a jikinsa."
Ta share hawayen da suka gangaro tace "Ya zanyi hakuri ya zama dole but babban bakin cikina reaction din daya nuna min, koni na nemi auren nan iyakar cin fuskar da zai min kenan."
Maryam tace "Ni kuwa ban dauka wulakanci bane, kisa kanki a position dinsa ki kwatanta ya za kiji...
"Maganar ta wuce Maryam, I've already made up my mind and there is no going back, so zsn daure ko me zasu taso, hhmmm Allah dai yaji Kan Rabiu."
Maryam ta mike tsaye "Zaki fara ba, to ba dani ba, naga alamun su Umma sai dare zasu iso ko in dan saurara zuwa karfe tara ma tafi gida?"
"Yes idsn ba wani damuwa nasan suna gab da shigiwa insha Allah kinsan Baffa bai son tafiyar dare."
Takwas saura kwata na dare suka dawo, Baffa yace su tsahirta yayi sallah sannan su gaisa, Umma Kuma ta zauna suna hirar 'yanuwa da abokan arziki na garin Gumel.
Alh. Mamman ya shigo bayan ta fito daga masallaci ya fadawa Rahima tanada bako a waje, taso taki fita Umma ta fara fada.
Direban Daktan ne jingine da mota yana jiran fitowarta, tana isa ya durkusa ya gaisheta kana ya bude motar ya fiddo wasu manyan ledoji guda biyu ya mika Mata Wai sakon ubangidansa..
Ta karba a sanyaye tace ya jirata kadan, ta koma ciki ta dauko masa tukwici ta kawo masa ya karba da kyar yana godiya.
Ta sake komawa tana shifa dakin ta kwashi ledojin ta diresu gaban Umma "Gashi wai inji baban Abdul "
Kafin Umma tace komi Maryam ta zaburo "Masha Allah, iye 'yar gidan Daktan ba, bari mu gani Musa albarka."
Umma ta harareta "Wannan zarbabin na menene?"
Ta kalli Rahima "Kinji Umma tafi son ki bude kyautar da hannunki ko kin ban izni in bude?"
Rahima ta amsa "Idan kin ganin ki wuce dasu na baki banso."
Ta wurgeta da maficin dake hannunta "Shima din ba kiga yadda ya koma ba har tozon wuya ya fara fa."
Rahima tace "Hhmmmm da Rabiu na nan da ya kusan kibar Alhajinku, dubi yadda ya koma kafin rasuwarsa."
Maryam ta shareta, ta sake maimaitawa, a nan ta kalleta tace "Saboda Allah Rahima ba zaki bar wannan bawan Allah ya kwanta makwancinsa lafiya ba, ke kenan da duk aka tada magana sai kin sako zancensa, Ina amfanin haka, adduarmu kadai yake bukata."..
Ta nisa tareda dafe kanta "Nima bana sanin time din da nike ambatonsa Maryam, Ina kokarin dainawa."
. "Ah to gara ki yiwa tufka hanci don ba namijin da zai dauki Yana aurenki kina zancen wani wanda ya rigamu gidan gaskiya."
"Nace miki zan bari, da kike fadin hakan ai mijin fari wuyan mantuwa gareshi, balle ma kowa na aura dole yai hakuri dani."
Ta kalleta a shagube "Sai dai kuwa idan bai sonku, muddin Yana kaunarki zaku rinka Kai ruwa rana ne, Wai ma ba haka ba ya batun Dakta?"
Rahima ta canza nan take "Ki bar batun nan don Allah, ai don in nunawa Hajiyar ba Mai yuwwa bane in har hakan take nufi naki komawa gidanta, har Abdul na bar musu in dominsa suke son aikata abin kunya, ko hausawa sunce ana barin halas....
Maryam ta harareta " Jiya dominki nayi tambaya a islamiyya kan shirmen da kike yi Kuma in fada miki don kin auri Dakta ba abinda ya kaucewa shariar musulumci bane, Malam yace addininmu nai hana wa ya auri matan kani na idan Allah yai masa rasuwa hakan shuma kani na iya auren matsn Wan sa in haka ta kasance.. Har da misalin cewan ko suna da rai ce dayansu ya kamu da rashun lafiyar da ya hana yin sunna da matarsa an nemi magani an rasa na tsawon shekarun da aka gindaya masa zai sahale mata gashi ya yaba hankalinta bai son tabar gidan don kyakkyawar dabi',unta Yana iya yiwa danuwansa maganar cewan iin ya saki shu ya aureta idan sun daidaita tsakaninsu, Kuma auren ya halasta, ke dinma banga abun tada jijiyoyin wuya bayan da bakinki kika fada min kina son Daktan .
Ta kauda Kai "Na dai so mutumin da aka bani labarinsa, da lamarin ya juye Kuma na sanu canjun ra'ayi.
Ta wani kalleta 'Karki kawi mun burgar banza, karyarki wallahi, was yace Miki ana yiwa soyayya yankan kauna, yadda mashin son wancan ya soki kirjinki haka na Daktan zai huda zuciyark tunda batun mutum guda ake in dai dama ba karya kike ba Wanda a sanina ba a karyar so da kauna."
Da taji alamun ta kamo hanya zata kureta saita canza hirar cikin dabara....
Suna cikin hirar suka ji yar karamar muryar Abdul ya shigo a guje Yana fadin 'Mami Kinga jirgina baba ya saya min."
Murnan ganinsa ya rufeta, ta daukeshi tana sumbatarsa "Oyo-oyo Abdul Ina Hajiya?.
Hankalin yaron ma wajen Walida, ganin hakan ta sauke shi, Walidan ta fara kukan sai ya bata jirginsa. Rahima tace Baba ya hada rigima kenan dole gobe inje in sayo miki naki jirgin".
Wani yaro Dan makwabtansu ne ya shigo Yana sallama suka amsa "Wai ance ana Kiran maman Abdul a waje."...
Rahima ta kakki Maryam kinji Kuma Bala da gulma shi daya saba shigowa har cikin gida a gaisa ".
Maryam tace "May be sauri yake, fita kiji in zai koma da Abdul dinne tunda ban gansa da kayansa ba."
Maimakon ta tsaya saka hijab, katon gyalen Maryam ta dauka ta yafa ta fita cikin sauri.
08/09/2020, 13:42 - Anty saliha: ...RAHIMA...doc by jami
19
Tun daga kan soron farko kamshin turaren 'fame' ya fara dukan hancinta, zuciyarta ta fara bugawa cikin sauri, ba dai zarginta zai zan gaskiya ba?
Ta karisa cikin tsakiyar soron gidansu inda tayi arba da *HASEEB* in person, rawar da jikinta ya fara, bai hanata saurin durkusawa cikin ladabi tace "Barka da yini, ya su Aunty Zuwaira?"
Ko kallon arziki bata samu daga gareshi ba
Ya amsa a takaice "Lafiya." Ya shiru
Ta dan jima tsugunne tana jiran taji da wacce ya taho tunda bai taba zuwa gidansu ba.
Da ya tuna bai da wata mafita dole ya fadi dalilin zuwansa kamar yadda yaiwa Mahaifiyarsa alkawari,ya cije, cikin isa da miskillancisa ya tambayeta "Magana ta kawo ni ko zan sami damar Fadi?"
Kamar ta amsa cewan bata da lokacin saurarensa, saita tuna kaninsa,da irin girmansa da yake gani kamar uba ba wa ba, ta tuna dawainiyar da yake dasu, hakan yasa ta hadiye zuciyarta tace "Ba damuwa Ina saurarenka."
Ya gyara tsayiwarsa sosai ya jingine da bango tareda goya hannayensa a kirji yace "Hajiya tace tayi miki bayanin komi don haka ba zan tsaya wani dogon bayani ba tunda kin amince da shirinta nima hakan akan dole yanzun ya rage naki kiyi shawarar yaushe kike ganin ya dace a daura auren?"
Gabanta ya buga rugugu, aure? Haka ake zancen auren cikin isa da kasaitar mulki, aiki jawur, tun kafin tafiya tai nisa bata iya cewa ta fasa, daman ta amsa ne saboda bata san shine ba, wata zuciyar kuma tace zaki zan mai karya alkawari kenan wanda a addinance hakan ya zama munafuci, can ta nisa, tace "Bani da yancin kaina koda nike bazawara, iyayena keda hakkin wannan sai abinda kika ce."
Shi kansa yasan nai kyauta, bai dace ya furta mata wadannan kalaman ba, ba ita ta Kar zomon ba, yaja numfashi yace "Okay zan jira su zartas da shawarwarinsu, nawa iyayen zasu taho in Sha Allah."
Da yaji ba zata kara cewa komi ba,sai ya Kara gyara murya yace "Abdul kuwa bai ji dadi ba amma naga ya warware, dazun jikin yafi masa zafi."
Tana dai tsugunne kanta sunkuye har zuwa lokacin, maganar da yake yi bai sa ta dago ba balle tayi responding.
Ya kada Kai "Ni zan koma, na wani problem ko?'
Ta girgiza Kai.
"Ina Abdul, in koma dashi ko a bar shi?"
sai a nan ta amsa "A tafi dashi, sai an jima a gaida Hajiya Aunty da Zuwaira."
Tana gama magana ta yunkura ta mike ta shige cikin gida ta barshi nan a tsaye.
Tana shiga ta cewa Maryam "Don Allah dauki Abdul ki mika sa waje zasu koma gidane."
Ta kalleta taga fuskar nan tata a daure bata tsaya tambaya ba ta rike hannun yaron suka nufi kofar gidan. Ko da wasa ba tayi zaton shi zata gani ba amma ta danne mamakinta ta gaisheshi, Abdul ya ruga wajensa ya kama hannunsa suka shiga mota suka wuce.
Har tana tuntube wajen saurin komawa cikin gida inda ta isko Rahima ta cika tayi dam, ta kalleta ta tuntsure da dariya tace "Yau Allah ya hadani da famous Dr Abdul-Haseeb Junaid din da ake magana, he's very handsome, ashe ganinsa a zahiri yafi ganinsa a tv."
Rahima ta cafe "May be ganun baiwar kyaun da Allah yai masa da kirar jiki msi kyau ne yasa yake wani ji da kansa."
Maryam tace "Ke fa na lura ba zaki kwantar da hankali ki fahimcesa ba, to komin ji da kansa dai gashi ya taho har gida, ya kuka yi?"
Ta tabe baki "Maganar ma da kyar yake har Yana m fada min shi dole ne ya amince da batun auren Wai Kuma yaushe nike son a daura? Ke kinji wani galari, wallahi ba domin ina ganin mutuncinsu ba da yaji magana daga bakina, darajar Rabiu kawai yaci, ko an fada masa nima da son raina za ayi oho."
Maryam ta tausayawa 'yaruwarta tace 'Gaskiya al'amarin da rikitarwa Rahima amma kiyi hakuri ki rungumi kaddara,Allah da ya shirya faruwan haka daku yasan dalilinsa, mu 'yan tayaku addua ne, ki daure karki dorawa Dakta laifi, shima na tabbatar abin na damunsa dole yaji a jikinsa."
Ta share hawayen da suka gangaro tace "Ya zanyi hakuri ya zama dole but babban bakin cikina reaction din daya nuna min, koni na nemi auren nan iyakar cin fuskar da zai min kenan."
Maryam tace "Ni kuwa ban dauka wulakanci bane, kisa kanki a position dinsa ki kwatanta ya za kiji...
"Maganar ta wuce Maryam, I've already made up my mind and there is no going back, so zsn daure ko me zasu taso, hhmmm Allah dai yaji Kan Rabiu."
Maryam ta mike tsaye "Zaki fara ba, to ba dani ba, naga alamun su Umma sai dare zasu iso ko in dan saurara zuwa karfe tara ma tafi gida?"
"Yes idsn ba wani damuwa nasan suna gab da shigiwa insha Allah kinsan Baffa bai son tafiyar dare."
Takwas saura kwata na dare suka dawo, Baffa yace su tsahirta yayi sallah sannan su gaisa, Umma Kuma ta zauna suna hirar 'yanuwa da abokan arziki na garin Gumel.
Alh. Mamman ya shigo bayan ta fito daga masallaci ya fadawa Rahima tanada bako a waje, taso taki fita Umma ta fara fada.
Direban Daktan ne jingine da mota yana jiran fitowarta, tana isa ya durkusa ya gaisheta kana ya bude motar ya fiddo wasu manyan ledoji guda biyu ya mika Mata Wai sakon ubangidansa..
Ta karba a sanyaye tace ya jirata kadan, ta koma ciki ta dauko masa tukwici ta kawo masa ya karba da kyar yana godiya.
Ta sake komawa tana shifa dakin ta kwashi ledojin ta diresu gaban Umma "Gashi wai inji baban Abdul "
Kafin Umma tace komi Maryam ta zaburo "Masha Allah, iye 'yar gidan Daktan ba, bari mu gani Musa albarka."
Umma ta harareta "Wannan zarbabin na menene?"
Ta kalli Rahima "Kinji Umma tafi son ki bude kyautar da hannunki ko kin ban izni in bude?"
Rahima ta amsa "Idan kin ganin ki wuce dasu na baki banso."