Sashe 17
Rahima Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read
Cikin ikonsa Allah sarkin sarauta sai taga wani mashahurin haske ta ko'ina, wani doki Mai fuka-fuki da ya ratso ta cikin hasken nan a guje ya sauko daf da ita. Jikin dokin ba irin dawakan data sani bane, wannan ilahirin jikinsa kalar azurfa ne, gashin bayansa gazar-gazar da kwarar idanunsa ne kawai bakin kirin.
Tsananin ganin wannan halitta daya cikata yasa bata lura da mutumin dake Kan dokin ba, bata ankara ba taji an dagta sama an dorata bisa dokin nan ya tashi sama suna tafiya tamkar wasu tsuntsaye, basu dade ba taga sun sauka daf da kofar wani farin gida gewaye da furanni, hancinta ya shaki wani hadadden kamshin data rasa inda yake fitowa, kamar tafiyar slow motion ta tsinci kanta cikin wani lambu cike da kayan marmari, ta mika hannu don ciro nunanniyar goba tsawonta bai Kai ga iccen ba, Mai dokin Nan ne ya matso yasa hannunsa ya ciro goban Nan har zai Mika Mata sai dokin yai haniniya ya kada fukafukinsa sai ya fasa bata Saida ya saka a bakinsa ya gutsura kana ya mika Mata sauran ta karba cikin mamaki, har zata Kai bakinta ta tuna bata san ko waye ba, ko kafin ta dago Kai ya haye dokin ya fara tafiya, ta daga masa hannu tana kiransa da muryar data shake, waigo wan da yayi yasa taga fuskarsa a zahiri ... Ganin ko waye yasa ta nemi yar da rabin gwaibar da ya bata Amma abin mamaki taki faduwa kamar ansa gam an manne gwaibar a hannunta, cikin hanzari ta sake juyowa ko za tayi katarin sake ganin fuskar.. aka yi dace shima ya sake waigowan yana murmushi a gareta, kamar walkiya dokin da Mai dokin suka bace...
Alhamdulillah Hamdan Kaseeran...
A nan littafin RAHIMA na daya yazo karshe. Za mu ci gaba dana biyun insha Allah.
Ina godiya ga Masoyana a duk inda kuke ina muku adduar fatar alkhairi a gareku.
Nayi kuskure ban bada number waya ba a farkon wannan littafi, to ga masu son saye da nemana ta WhatsApp a neme ni a wannan num 08034243456 WhatsApp kawai plssðŸ™ðŸ¿
Masu son kirana Kuma a nemi a wannan num 07036391747
Kasancewar littafin RAHIMA na sayarwa ne masu son saye Acccnt number mu shine 0598537268
GT Bank.
07/09/2020, 21:32 - Anty saliha: ...ˆRAHIMA..doc by Jami
17
Ta farka cike da mamakin murdadden mafarkin da tayi, cikin gigita ta rinka karanto adduar shugaban ayoyin alqur'ani kana ta dora da adduar neman tsari daga mugun mafarki, tsorene ya hanata jin sautin muryar Maryam da take karatun qu'ani can gefe daya, ta kasa yin wani kwakwkwaran motsi, da kyar ta tashi ta nufi toilet ta sake dauro alwala ta gabatar da sallar dhuha sannan itama ta dauko qur'anin ta fara karatu .
Basu tashi Kan sallayarsu ba saida suka dauki dogon lokaci don sun saba tyn suna gida duk bayan sallar asubah sai sunyi karatun sa'annan su dora sa azkhar din safe don kwadayin dacewa da lokacin amsar addua.
Goma daidai sunyi wanka sun kintsa tsaf, Rahima ta kalli Maryam 'Ba zanyi breakfast ba, gida zan koma yanzun nasan Umma na zuba idon ganin na koma da wuri."
Ta kura mata ido "Akwai abinda ke damunki duk kin canza wayewar garin nan, ko baku hadu da surukin nawa a mafarki bane?"
Ta koma ta zauna jiki babu kwari kamar wace aka zare mata lakka tace "Ke dai bari 'yaruwa, nayi adduoi na roki Allah yadda kika sani but Wanda na gani cikin mafarkina... Kai!!! Ta girgiza Kai, na firgita wallahi."
Maryam ta kalleta "Shakka kike?"
Ta kada Kai "No mamaki nike ji da fargaban mafarkin nawa ya zama real."
Maryam ta kalleta cikin damuwa "Kinata kwanare, shin wa kika gani ne?"
Rahima ta jinjina "Hhmmmm bana jin zaki amince da abinda zan fada miki."
"Me zai hanani yarda after all Allah muka roka Ya amsa mana mene na al'ajabi? Ni wallahi ko waye na yarda na amince shi dinne zabin Allah."
Ta kauda Kai tayi shiru na dakika kana tace.. Maryam *Ya Haseeb* fa na gani a mafarkina."
Duk da dakewan da tayi itama taji mugun mamaki ta buga kirji "HASEEB! Ba dai Dr Haseeb wan Rabiu ba?".
Hawaye suka ciko a idanunta yayinda ta amsa " Shi din ne, me hakan ke nufi Maryam?"
Ta taso ta matso kusa da ita ta dafata cikin rarrashi "kwantar da hankalinki za kiyi mu saurari Hajiya muji nata manufar amma a hakikani mafarkinki gaskiya ne,zaiyi wuya aure bai shiga tsakaninku dashi ba Ina ganin tun farko shi Hajiyar ma ke nufi."
Cikin sheshekar kuka ta dago "In hakura dame? Haba Ina! Idan har shi take nufi na fasa amsa batunta, ba Zan iya zama dashi matsayin miji ba."
"Kina son zancen yai tsawo kenan, shikenan mu bari har zuwa sauran kwanaki ukun data diba miki mu gani, mu ci gaba da addua Allah ya tabbatar mana da khairan"
Hankalinta a tashe ta shiga tayi sallama da Hjy Suwaiba ta wuce gida.
Nan da Nan Umman ta gane akwai abinda ke damunta tana cikin matsala saboda tunda ta shigo ba walwala a tareda ita, abin mamaki ko Abdul bata tambaya ba.
Har zuwa karfe biyar na bayan la'asar babu canji a tareda Rahima hakan yasa a matsayinta na uwa Umma ta kira cikin daki ta yambayeta meke damunta.
Nan take ta musa cewa babu komi, Umman ta kalleta cikin damuwa tace "Shikenan tunda ban isa ki fada min matsalarki ba."
Rahima ta saka mata kuka tace "Idan ma akwai matsala nina janyowa kaina Umma imda nayi aurena tuni da ban shiga kangin Nan ba, yanzun ya zanyi da Raina?".
Umma ta Kara rudewa "Ya za ayi in baki amsa tunda ban san damuwar taki ba?"
Da yake sun saba basu boye Mata komi ta zayyane mata labarin mafarkinta da yadda suka yi da Maryam"
Ta dade bata iya magana saboda zancen ya daketa itama amma ta daure ta kalli 'yarta "To in banda shirmenki mene na tada hankali harda koke-koke? Aure ba nufin Allah bane, matar mutum kabarinsa, kin taba ganin mijin da bai auri matar da ba tasa ba? Idan Allah ya kaddaro Haseeb mijinki ne babu Wanda ya isa ya hana, don haka ki natsu ki barwa Allah muga abinda zaiyi tukunna."
Tasa handkerchief ta share hawayen dake fitowa tace "Ba abinda ke damuna irin alkawarin dana daukarwa Hajiya na amince da zabinta ba tare da tunanin wai shi take nufi ba, haba Umma ya za ayi wannan danyen aikin?"
Umma ta kalleta "Ta yaro kyau take bata karko, tashi jeki share hawayenki, Zan nemi Hajiyar mu tattauna mai yuwwa in har hakanne."
Tace "Don Allah Umma idan zaki, ki kwashe kayan Abdul ki Kai musu na hakura dashi, don ina ganin ita kanta Hajiyar sabida shi ta yanke hukuncin Nan, watau Kar in auri wani can daban in tafi dashi."
Ta bude baki tana mamakin kalaman diyarta, lakle sai sunyi da gaske, tace "To Ina Kuma ruwan Abdul da za ayi masa mai gaba daya, ki bari zan maidashi gidansu idan lokaci yayi Kuma don Allah kar in sake jin kin zargi Hajiya kinsan ba zata cuceki ba, ko alama bai dace kiyi furucin da kika yi ba."
Ta kwana ta yini cikin zulumi da fargaba abinda zau faru. Gaba daya komi yai mara dif, brain dinta ya hargitse, zuciyarta ta kasa sarrafa komi sai tunanin yadda akayi ta amince da so da kaunar wanda bata taba gani ba, to ai yanzun ta daina ikrarin haka, shin ba Ya Haseeb ne ta tsunduma cikin kogin soyayyarsa ba?
Satin data dauka tana adduoi suka cika amma ta kekasa kasa taki komawa gidan Hjy Kaltume, bata aika an dauko Abdul din ba ma, ko da tanada tabbacin Umma ta ziyarci Hajiyar amma bata ce mata komi, ita da Baffa sun sa mata ido sai wani lallabata suke, ta share kowa a gidan hatta Maryam data taho ta rasa gane kanta.
Babu Wanda bai san asibitin nan mai suna *HASEEB MEDICAL CENTRE* ba, ba don komi asibitin tayi fice ba sai domin kwarewan babban likitan(CMD). Dr Haseeb Junaid Galadanci dogo ne mai dan jiki, launin fatar jikinsa chocolate ne hakan yasa tsakar mallacin da aka yi masa suka fito sosai a gefen kumatunsa a 'yar doguwar fuskarsa wadanda suka kara fito da kyaunsa na zahiri.
Yana da zafin nama sosai, hanzarin nasa ya dace da irin aikinsa watau kwararren likitan da ya shahara yai suna bangaren daya shafi rashin lafiyar kwakwalwa, kashin baya da halittun da suka danganci wadannan ababe masu matukar muhimmanci a jikin Dan Adam
Dr H.J.G yadda ake kiransa yasan hallitar kwakwalwar bil adama tamkar yadda yasan tafin hannunsa, kazaliza don ya bude kan mutum ko baya ya mayar ya dinke ba wani abu ne mai wuya a wajensa ba, da taimakon Allah duk wata matsala da aka kawo masa akayi sa'a ya duba yai aiki ko bada magani a kanyi nasara.
Dalili kenan da sunansa ya bunkasa tun daga gida Nigeria har kasashen waje, manyan asibitocin ketare ma dashi suke takama don ba inda kafafunsa basu taka ba. Sabida yawace-yawacen da yake yi ne yasa shi jin harsuna daban-daban, yana jin harshen larabci, faransanci, jamusanci, dangane da yaren harsunan kasarmu kuwa tun Yana jami'a ya iya yaren yarbanci, fulatanci dana igbo, abin ban sha'awa duk yaren daya juya harshe Yana yi sai mutum ta rantse daman shine mother tongue dinsa.
Ganin yadda ayyuka suka yi masa yawa, zirga-zirga na neman tauyesa wajen sauke hakkin iyalinsa dana iyaye yasa ya yanke shawarar gina makekiyar asibiti Wanda ya nemi wasu kwararuj likitocin suka hadu suna gudanar da harkar asibitin gadan-gadan.
Babban abin shaawa da yawanci maganar da mutane suke fadi shine ma'aikatan asibitin nada karamci tun daga leburori zuwa nurses da doctor's dinsu balle shi kanshi uban tafiyar, ta ta shahara wajen tsabta sosai, babu wulakanci tsakaninsu da patients, sun dauki Mai kudi da talaka gudane, patient sunansa patient Kuma Abu guda suka zo nema (lafiya) don haka babu banbanci.
Ba nan ya tsaya ba da kyautatawa patients dinsa ba, da duk ya lakanci basu da halin biyansa hakkinsa ya kan taimaka yayi aikin kyauta tareda kulawa ta musamman.
Tsananin ganin wannan halitta daya cikata yasa bata lura da mutumin dake Kan dokin ba, bata ankara ba taji an dagta sama an dorata bisa dokin nan ya tashi sama suna tafiya tamkar wasu tsuntsaye, basu dade ba taga sun sauka daf da kofar wani farin gida gewaye da furanni, hancinta ya shaki wani hadadden kamshin data rasa inda yake fitowa, kamar tafiyar slow motion ta tsinci kanta cikin wani lambu cike da kayan marmari, ta mika hannu don ciro nunanniyar goba tsawonta bai Kai ga iccen ba, Mai dokin Nan ne ya matso yasa hannunsa ya ciro goban Nan har zai Mika Mata sai dokin yai haniniya ya kada fukafukinsa sai ya fasa bata Saida ya saka a bakinsa ya gutsura kana ya mika Mata sauran ta karba cikin mamaki, har zata Kai bakinta ta tuna bata san ko waye ba, ko kafin ta dago Kai ya haye dokin ya fara tafiya, ta daga masa hannu tana kiransa da muryar data shake, waigo wan da yayi yasa taga fuskarsa a zahiri ... Ganin ko waye yasa ta nemi yar da rabin gwaibar da ya bata Amma abin mamaki taki faduwa kamar ansa gam an manne gwaibar a hannunta, cikin hanzari ta sake juyowa ko za tayi katarin sake ganin fuskar.. aka yi dace shima ya sake waigowan yana murmushi a gareta, kamar walkiya dokin da Mai dokin suka bace...
Alhamdulillah Hamdan Kaseeran...
A nan littafin RAHIMA na daya yazo karshe. Za mu ci gaba dana biyun insha Allah.
Ina godiya ga Masoyana a duk inda kuke ina muku adduar fatar alkhairi a gareku.
Nayi kuskure ban bada number waya ba a farkon wannan littafi, to ga masu son saye da nemana ta WhatsApp a neme ni a wannan num 08034243456 WhatsApp kawai plssðŸ™ðŸ¿
Masu son kirana Kuma a nemi a wannan num 07036391747
Kasancewar littafin RAHIMA na sayarwa ne masu son saye Acccnt number mu shine 0598537268
GT Bank.
07/09/2020, 21:32 - Anty saliha: ...ˆRAHIMA..doc by Jami
17
Ta farka cike da mamakin murdadden mafarkin da tayi, cikin gigita ta rinka karanto adduar shugaban ayoyin alqur'ani kana ta dora da adduar neman tsari daga mugun mafarki, tsorene ya hanata jin sautin muryar Maryam da take karatun qu'ani can gefe daya, ta kasa yin wani kwakwkwaran motsi, da kyar ta tashi ta nufi toilet ta sake dauro alwala ta gabatar da sallar dhuha sannan itama ta dauko qur'anin ta fara karatu .
Basu tashi Kan sallayarsu ba saida suka dauki dogon lokaci don sun saba tyn suna gida duk bayan sallar asubah sai sunyi karatun sa'annan su dora sa azkhar din safe don kwadayin dacewa da lokacin amsar addua.
Goma daidai sunyi wanka sun kintsa tsaf, Rahima ta kalli Maryam 'Ba zanyi breakfast ba, gida zan koma yanzun nasan Umma na zuba idon ganin na koma da wuri."
Ta kura mata ido "Akwai abinda ke damunki duk kin canza wayewar garin nan, ko baku hadu da surukin nawa a mafarki bane?"
Ta koma ta zauna jiki babu kwari kamar wace aka zare mata lakka tace "Ke dai bari 'yaruwa, nayi adduoi na roki Allah yadda kika sani but Wanda na gani cikin mafarkina... Kai!!! Ta girgiza Kai, na firgita wallahi."
Maryam ta kalleta "Shakka kike?"
Ta kada Kai "No mamaki nike ji da fargaban mafarkin nawa ya zama real."
Maryam ta kalleta cikin damuwa "Kinata kwanare, shin wa kika gani ne?"
Rahima ta jinjina "Hhmmmm bana jin zaki amince da abinda zan fada miki."
"Me zai hanani yarda after all Allah muka roka Ya amsa mana mene na al'ajabi? Ni wallahi ko waye na yarda na amince shi dinne zabin Allah."
Ta kauda Kai tayi shiru na dakika kana tace.. Maryam *Ya Haseeb* fa na gani a mafarkina."
Duk da dakewan da tayi itama taji mugun mamaki ta buga kirji "HASEEB! Ba dai Dr Haseeb wan Rabiu ba?".
Hawaye suka ciko a idanunta yayinda ta amsa " Shi din ne, me hakan ke nufi Maryam?"
Ta taso ta matso kusa da ita ta dafata cikin rarrashi "kwantar da hankalinki za kiyi mu saurari Hajiya muji nata manufar amma a hakikani mafarkinki gaskiya ne,zaiyi wuya aure bai shiga tsakaninku dashi ba Ina ganin tun farko shi Hajiyar ma ke nufi."
Cikin sheshekar kuka ta dago "In hakura dame? Haba Ina! Idan har shi take nufi na fasa amsa batunta, ba Zan iya zama dashi matsayin miji ba."
"Kina son zancen yai tsawo kenan, shikenan mu bari har zuwa sauran kwanaki ukun data diba miki mu gani, mu ci gaba da addua Allah ya tabbatar mana da khairan"
Hankalinta a tashe ta shiga tayi sallama da Hjy Suwaiba ta wuce gida.
Nan da Nan Umman ta gane akwai abinda ke damunta tana cikin matsala saboda tunda ta shigo ba walwala a tareda ita, abin mamaki ko Abdul bata tambaya ba.
Har zuwa karfe biyar na bayan la'asar babu canji a tareda Rahima hakan yasa a matsayinta na uwa Umma ta kira cikin daki ta yambayeta meke damunta.
Nan take ta musa cewa babu komi, Umman ta kalleta cikin damuwa tace "Shikenan tunda ban isa ki fada min matsalarki ba."
Rahima ta saka mata kuka tace "Idan ma akwai matsala nina janyowa kaina Umma imda nayi aurena tuni da ban shiga kangin Nan ba, yanzun ya zanyi da Raina?".
Umma ta Kara rudewa "Ya za ayi in baki amsa tunda ban san damuwar taki ba?"
Da yake sun saba basu boye Mata komi ta zayyane mata labarin mafarkinta da yadda suka yi da Maryam"
Ta dade bata iya magana saboda zancen ya daketa itama amma ta daure ta kalli 'yarta "To in banda shirmenki mene na tada hankali harda koke-koke? Aure ba nufin Allah bane, matar mutum kabarinsa, kin taba ganin mijin da bai auri matar da ba tasa ba? Idan Allah ya kaddaro Haseeb mijinki ne babu Wanda ya isa ya hana, don haka ki natsu ki barwa Allah muga abinda zaiyi tukunna."
Tasa handkerchief ta share hawayen dake fitowa tace "Ba abinda ke damuna irin alkawarin dana daukarwa Hajiya na amince da zabinta ba tare da tunanin wai shi take nufi ba, haba Umma ya za ayi wannan danyen aikin?"
Umma ta kalleta "Ta yaro kyau take bata karko, tashi jeki share hawayenki, Zan nemi Hajiyar mu tattauna mai yuwwa in har hakanne."
Tace "Don Allah Umma idan zaki, ki kwashe kayan Abdul ki Kai musu na hakura dashi, don ina ganin ita kanta Hajiyar sabida shi ta yanke hukuncin Nan, watau Kar in auri wani can daban in tafi dashi."
Ta bude baki tana mamakin kalaman diyarta, lakle sai sunyi da gaske, tace "To Ina Kuma ruwan Abdul da za ayi masa mai gaba daya, ki bari zan maidashi gidansu idan lokaci yayi Kuma don Allah kar in sake jin kin zargi Hajiya kinsan ba zata cuceki ba, ko alama bai dace kiyi furucin da kika yi ba."
Ta kwana ta yini cikin zulumi da fargaba abinda zau faru. Gaba daya komi yai mara dif, brain dinta ya hargitse, zuciyarta ta kasa sarrafa komi sai tunanin yadda akayi ta amince da so da kaunar wanda bata taba gani ba, to ai yanzun ta daina ikrarin haka, shin ba Ya Haseeb ne ta tsunduma cikin kogin soyayyarsa ba?
Satin data dauka tana adduoi suka cika amma ta kekasa kasa taki komawa gidan Hjy Kaltume, bata aika an dauko Abdul din ba ma, ko da tanada tabbacin Umma ta ziyarci Hajiyar amma bata ce mata komi, ita da Baffa sun sa mata ido sai wani lallabata suke, ta share kowa a gidan hatta Maryam data taho ta rasa gane kanta.
Babu Wanda bai san asibitin nan mai suna *HASEEB MEDICAL CENTRE* ba, ba don komi asibitin tayi fice ba sai domin kwarewan babban likitan(CMD). Dr Haseeb Junaid Galadanci dogo ne mai dan jiki, launin fatar jikinsa chocolate ne hakan yasa tsakar mallacin da aka yi masa suka fito sosai a gefen kumatunsa a 'yar doguwar fuskarsa wadanda suka kara fito da kyaunsa na zahiri.
Yana da zafin nama sosai, hanzarin nasa ya dace da irin aikinsa watau kwararren likitan da ya shahara yai suna bangaren daya shafi rashin lafiyar kwakwalwa, kashin baya da halittun da suka danganci wadannan ababe masu matukar muhimmanci a jikin Dan Adam
Dr H.J.G yadda ake kiransa yasan hallitar kwakwalwar bil adama tamkar yadda yasan tafin hannunsa, kazaliza don ya bude kan mutum ko baya ya mayar ya dinke ba wani abu ne mai wuya a wajensa ba, da taimakon Allah duk wata matsala da aka kawo masa akayi sa'a ya duba yai aiki ko bada magani a kanyi nasara.
Dalili kenan da sunansa ya bunkasa tun daga gida Nigeria har kasashen waje, manyan asibitocin ketare ma dashi suke takama don ba inda kafafunsa basu taka ba. Sabida yawace-yawacen da yake yi ne yasa shi jin harsuna daban-daban, yana jin harshen larabci, faransanci, jamusanci, dangane da yaren harsunan kasarmu kuwa tun Yana jami'a ya iya yaren yarbanci, fulatanci dana igbo, abin ban sha'awa duk yaren daya juya harshe Yana yi sai mutum ta rantse daman shine mother tongue dinsa.
Ganin yadda ayyuka suka yi masa yawa, zirga-zirga na neman tauyesa wajen sauke hakkin iyalinsa dana iyaye yasa ya yanke shawarar gina makekiyar asibiti Wanda ya nemi wasu kwararuj likitocin suka hadu suna gudanar da harkar asibitin gadan-gadan.
Babban abin shaawa da yawanci maganar da mutane suke fadi shine ma'aikatan asibitin nada karamci tun daga leburori zuwa nurses da doctor's dinsu balle shi kanshi uban tafiyar, ta ta shahara wajen tsabta sosai, babu wulakanci tsakaninsu da patients, sun dauki Mai kudi da talaka gudane, patient sunansa patient Kuma Abu guda suka zo nema (lafiya) don haka babu banbanci.
Ba nan ya tsaya ba da kyautatawa patients dinsa ba, da duk ya lakanci basu da halin biyansa hakkinsa ya kan taimaka yayi aikin kyauta tareda kulawa ta musamman.