Sashe 6
Nahuce Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Amma maganar soyayya irin ta uwar miji da surukar ta tsakanin ta da Rahinah Omar babu ita. Kamar yadda at the same time babu kiyayya. Watau bata kin ta haka bata son ta. A yadda ta ke son Habibullahi, kamata yayi a ce matar sa ta fari ta zame mata ‘yar gaban goshi, wadda zasu kashe su rufe tare, amma banda wannan Rahinar mai jin kan ta kamar wani dutsen yaqutu.
Washegari suka je suka kai goron tambaya da kudin aure. Aka sa ranar daurin aure Juma’ah bayan masallaci, tun ranar Alhamis Ambasada da ‘ya’yan sa maza Abbas da kanin sa wadanda suka dawo karatu daga Frankfurt, Uncle Usman da nasa samarin ‘ya’yan hudu wato su Musaddiq suka kama hanyar Adamawa.
Sun dauki hanya tun da sanyin safiya daga Abuja amma basu isa Girei ba sai dare. Kai tsaye gidan Sarkin Fulani suka sauka bayan sun je sun kama Guest Inn din da zasu kwana anan cikin garin Girei.
Kafin isowar su mutanen Nahuche sun riga su isa, kannen mahaifin Habibu ne da wasu dattijai daga family din su har da Baban Ex budurwar sa Shafa’atu wanda shine madaurin auren sa duk sun isa Girei kamar yadda aka tsara. Alh. Usman shi yayi musu masauki a inda suma suka sauka (Girei Motel).
Washegari misalin karfe uku na rana bayan an sakko masallaci duk suna zaune zauren Sarkin Fulani, manyan ‘ya’yan sa su Ilyasu, Dagacin garin Girei, makwabta da dattijai abokanan arzikin Sarkin Fulani, abokan mahaifin Rahinah na kuruciya da abokan Uncle Usman na garin Girei da duk wani mai fada a ji a garin Girei, jama’ar gari ‘yan gayyar sodi ma ba’a bar su a baya ba.
Iyayen Habibu (Baffannin sa) suka mika sadakin su mai daraja wanda ya fito ne daga aljihun su da aljihun Hajiyar sa da suka yi karo-karo suka hada ba tareda sun bi ta kan sa ba, kasancewar kowannen su a kage yake kan yayi auren kawai koma da wacece, to balle da aka ce uwar dan sa Abdallah.
Don haka kowannen su cikin farin-ciki yake yin komai, ba bata lokaci aka daura auren HABIBU MUSTAPHA NAHUCHE da DR. RAHINAH OMAR GIREI. Wani aure da ya bar tarihi cike da farin cikin kowanne bangare. Ana yi ana raha da annashuwa. Limamin masallacin Juma’a na garin Girei ya bi auren da addu’o’I na musanman, tare da rokawa ma’auratan zaman lafiya da kwanciyar hankali na har abada a tsakanin su.
Washegri Asabar kowa ya kama hanyar komawa garin da ya fito, tarewa sai Habibu ya zo da kansa inji Sarkin Fulani. Ya ce Usman ya kawo masa Rahinah nan gidan sa, daga nan Girei za’a dauke ta zuwa gidan mijin ta bayan sun yi biki irin na al’adar garin Girei. Usman ya gaya masa tana gidan Ambasada yanzu haka, amma Nene Balki da Yafendo zasu dauko ta su kawo ta, in ya so, su rankaya daga nan Girei zuwa duk inda Habibu ya zaba mata ta zauna.
Kwanaki biyu kenan da daurin auren, ba tare da Habibu ko Rahinah wani ya kara neman dan uwan sa ba ko a waya, amma suna sane da cewa an daura din. Ita tana dakin ta na gidan su Nene a kwance kawai, ba abinda ke tada ta sai sallah.
Ta kashe wayoyin ta bakidaya tana wani irin jinyar zuciyar ta, da jinyar matacciyar gangar jikin ta kamar wadda ke fama da cutar paralysis, sabida yadda ta bi ta rafke akan gado, kokwakkwaran motsi bata yi, sallahr ma bata sanin lokaci yayi har sai Nene ta leko ta shaida mata cewa an yi kiran sallah.
Tun daga ranar da aka kara daura musu aure uffan bata kara cewa ba, domin kalaman Habibu na ranar da ya zo, sun yi wa zuciyar ta lahani da barna mai yawa.
Idan ta yi tunanin wai yanzu ya kara zama mijin ta na sunnah, sai duk wani kyakkyawan tunani ya subuce mata. Ta rasa wanda za ta kama.
Bata da tsumi ba ta da dabara a halin yanzu, sai na irin zaman da za ta fuskanta nan ba da jimawa ba a gidan Nahuche, a karo na biyu!
Ita dai ta san trial din ta da Habibu bai kare ba, akwai sauran manyan kalubale da ya tanadar mata, wadanda suka fi na baya. Domin ya rama abinda ya ke ganin ta yi masa. Abinda za ta rike a matsayin makamin ta yanzu shine kadai (maintaining self-esteem) din ta, na cewa ta fi gaban duk wani wargin sa a halin yanzu, za ta nuna masa cewa wata fuskar yanzu ta fi gaban mari. In Rahinah ya sani, wannan Rahinatu ce, warki daidai kugun kowanne da namiji.
Daga ita har shi sun kasa kulla komai sai tunani, wanda ya kasa basu mafita ga tarin damuwoyin su da tarin kalubalen da suke hangowa sake zama da juna, tunda dai har yanzu basu kai ga cimma matsaya kwakkwara wadda za ta yi maganin matsalolin su da rashin fahimtar da ke tsakanin su ba.
A nasa bangaren, Habib Nahuche, ya kudurce a ran sa ko kadan ba zai dauki rabin abinda ya dauka a baya daga Rahinah da sunan rashin SO ba, tunda dai yanzun ita ta amsawa kanta ba wani ya tursasata ba, don haka babu hannun sa a ciki. Nan kusa ma bai shirya mata tarewa ba ko inda zata zauna, don kamar yadda yace din ne da gaske bashi da bukatar ta cikin rayuwar sa ta yanzu.
Da dai Uncle da Ambasada sun sani da sun bar bygone a muhallin ta, don basu gama sanin ko wacece ‘yar su Rahinah ba har gobe, shiyasa suke tsammanin da zuciya daya ta amsa, shi kam ya dade da sanin cewa ya riga ya bata baya. Ya manta da ya taba auren ta, ya dade da karbar rayuwa a yadda ya same ta, kuma yana jin dadin ta a hakan. Da Rahinah, da babu ita, ba zai kasa rayuwa ba, insha Allahu.
Me jiya ta yi bare yau? Abin nufi me rashin ta na shekaru goma ya kara musu ko ya hana musu shi da Abdallahn?
Da wannan jinyar zuciyar kowannen su ke jibge akan gadon sa, ya dakatar da kowanne ayyuka na cigaban rayuwar sa da dailyactivities din sa.
Amma ga iyayen su da masoyan su abin ba haka yake ba, aunty Badiya, a ranar don farin cikin an daura wa Habibu aure da Rahinah, sai da ta kai goshin ta kasa ta yi sujjadar shukr, ta kuma dafa abinci mai rai da motsi ta rabawa mabukata sadaqah.
Hajiya Kaltume kuwa, ko da bata maraba da Rahinah, farin cikin yau Habibullahi yayi aure da azumi ta tashi a bakin ta.
Itama ta sa an dafa abincin sadaqa an raba a Kofar Jange har gidajen makwabtan ta, ko dama duk Juma’ah tana bada sadaqar naman saniya, da ake kayarwa a rabawa mabuqata na Kofar Jange, ranar da Uncle Usman ya tabbatar mata sun dauro auren suna kan hanyar dawowa Shanu uku ta sa aka kayar don yin sadaqah.
Nene Balki da Yafendo kuwa suna can suna yi wa Rahinah kyakkyawan shiri irin na iyayen kwarai masu shirin kai ‘yar fari daki, Nene tayi ordern kayan gyaran mata ‘yan gaske tafiyayyu tun daga Nijar. Ta kuma yi Magana da Yagana ‘yar Maiduguri mai yi mata gyaran jiki kan ta zo a washegari ta fara gyara Rahinah.
Sahura mai aikin Rahinah tana Kaduna, da Anty Badiya ta yi mata waya ta ce su fara shirin tarewa har rawa sai da ta taka. Don haka duk wani masoyin su cikin farin ciki yake, ya kuma ci wa auren nan alwashi da buri sabanin ma’auratan, wadanda ke ganin tamkar Alkiyamar su ta matso.
Kowanne gani yake an katse masa rayuwa an kuma hada shi da alaqaqai, tunda kar ce ta san kar, kowanne da irin alwashin da yake ci wa zuciyar sa a kan dan uwan sa.
Shi dai Habibu alwashi ya ci ba zai bari Rahinah ta shiga tsakanin sa da dan sa ba, tunda tare ta gan su, ta sake kutsowa cikin rayuwar su don ta kara tarwatsa ta.
Ita kuwa Rahinah abu daya ne yake sassauta zuciyar ta in ta tuna yanzu zata samu kusanci da Abdallah. Za ta maida hankalin ta ne kacokam kan cike wawakeken gibin da Habibu ya samar a tsakanin su wanda ta san ba zai yiwu a lokaci guda ba, sai ta yi da gaske wajen kwatowa kan ta soyayyar dan ta, ta cike ratar da Habibu ya janyo a tsakanin su.
Wannan shi ne kadai abin da zai zaunar da ita a gidan Habibu Nahuche amma ba Habibu ba; soyayyar dan ta Abdullahi!
Uwa uba farin cikin iyayen ta da kwanciyar hankalin su wato Ambasada da Uncle Usman. Ita kan ta Aunty Badiya Rahinah tana darajja ta, bata jin Habibu ya isa ya farraqa tsakanin su.
Domin Badiya ta kaunace ta kauna ta hakika tun kafin ta san alaqar da ke tsakanin su. A lokacin da ta ke neman dangin da za su rungume ta. Don haka ko wanene Habibu ga Badiya alaqar su mai kyau tana nan bazata taba canzawa ba saboda shi.
******
*Na huce* is not free.
It's 1000 via 3094856450
Sumayyah Kabara Firstbank
Washegari suka je suka kai goron tambaya da kudin aure. Aka sa ranar daurin aure Juma’ah bayan masallaci, tun ranar Alhamis Ambasada da ‘ya’yan sa maza Abbas da kanin sa wadanda suka dawo karatu daga Frankfurt, Uncle Usman da nasa samarin ‘ya’yan hudu wato su Musaddiq suka kama hanyar Adamawa.
Sun dauki hanya tun da sanyin safiya daga Abuja amma basu isa Girei ba sai dare. Kai tsaye gidan Sarkin Fulani suka sauka bayan sun je sun kama Guest Inn din da zasu kwana anan cikin garin Girei.
Kafin isowar su mutanen Nahuche sun riga su isa, kannen mahaifin Habibu ne da wasu dattijai daga family din su har da Baban Ex budurwar sa Shafa’atu wanda shine madaurin auren sa duk sun isa Girei kamar yadda aka tsara. Alh. Usman shi yayi musu masauki a inda suma suka sauka (Girei Motel).
Washegari misalin karfe uku na rana bayan an sakko masallaci duk suna zaune zauren Sarkin Fulani, manyan ‘ya’yan sa su Ilyasu, Dagacin garin Girei, makwabta da dattijai abokanan arzikin Sarkin Fulani, abokan mahaifin Rahinah na kuruciya da abokan Uncle Usman na garin Girei da duk wani mai fada a ji a garin Girei, jama’ar gari ‘yan gayyar sodi ma ba’a bar su a baya ba.
Iyayen Habibu (Baffannin sa) suka mika sadakin su mai daraja wanda ya fito ne daga aljihun su da aljihun Hajiyar sa da suka yi karo-karo suka hada ba tareda sun bi ta kan sa ba, kasancewar kowannen su a kage yake kan yayi auren kawai koma da wacece, to balle da aka ce uwar dan sa Abdallah.
Don haka kowannen su cikin farin-ciki yake yin komai, ba bata lokaci aka daura auren HABIBU MUSTAPHA NAHUCHE da DR. RAHINAH OMAR GIREI. Wani aure da ya bar tarihi cike da farin cikin kowanne bangare. Ana yi ana raha da annashuwa. Limamin masallacin Juma’a na garin Girei ya bi auren da addu’o’I na musanman, tare da rokawa ma’auratan zaman lafiya da kwanciyar hankali na har abada a tsakanin su.
Washegri Asabar kowa ya kama hanyar komawa garin da ya fito, tarewa sai Habibu ya zo da kansa inji Sarkin Fulani. Ya ce Usman ya kawo masa Rahinah nan gidan sa, daga nan Girei za’a dauke ta zuwa gidan mijin ta bayan sun yi biki irin na al’adar garin Girei. Usman ya gaya masa tana gidan Ambasada yanzu haka, amma Nene Balki da Yafendo zasu dauko ta su kawo ta, in ya so, su rankaya daga nan Girei zuwa duk inda Habibu ya zaba mata ta zauna.
Kwanaki biyu kenan da daurin auren, ba tare da Habibu ko Rahinah wani ya kara neman dan uwan sa ba ko a waya, amma suna sane da cewa an daura din. Ita tana dakin ta na gidan su Nene a kwance kawai, ba abinda ke tada ta sai sallah.
Ta kashe wayoyin ta bakidaya tana wani irin jinyar zuciyar ta, da jinyar matacciyar gangar jikin ta kamar wadda ke fama da cutar paralysis, sabida yadda ta bi ta rafke akan gado, kokwakkwaran motsi bata yi, sallahr ma bata sanin lokaci yayi har sai Nene ta leko ta shaida mata cewa an yi kiran sallah.
Tun daga ranar da aka kara daura musu aure uffan bata kara cewa ba, domin kalaman Habibu na ranar da ya zo, sun yi wa zuciyar ta lahani da barna mai yawa.
Idan ta yi tunanin wai yanzu ya kara zama mijin ta na sunnah, sai duk wani kyakkyawan tunani ya subuce mata. Ta rasa wanda za ta kama.
Bata da tsumi ba ta da dabara a halin yanzu, sai na irin zaman da za ta fuskanta nan ba da jimawa ba a gidan Nahuche, a karo na biyu!
Ita dai ta san trial din ta da Habibu bai kare ba, akwai sauran manyan kalubale da ya tanadar mata, wadanda suka fi na baya. Domin ya rama abinda ya ke ganin ta yi masa. Abinda za ta rike a matsayin makamin ta yanzu shine kadai (maintaining self-esteem) din ta, na cewa ta fi gaban duk wani wargin sa a halin yanzu, za ta nuna masa cewa wata fuskar yanzu ta fi gaban mari. In Rahinah ya sani, wannan Rahinatu ce, warki daidai kugun kowanne da namiji.
Daga ita har shi sun kasa kulla komai sai tunani, wanda ya kasa basu mafita ga tarin damuwoyin su da tarin kalubalen da suke hangowa sake zama da juna, tunda dai har yanzu basu kai ga cimma matsaya kwakkwara wadda za ta yi maganin matsalolin su da rashin fahimtar da ke tsakanin su ba.
A nasa bangaren, Habib Nahuche, ya kudurce a ran sa ko kadan ba zai dauki rabin abinda ya dauka a baya daga Rahinah da sunan rashin SO ba, tunda dai yanzun ita ta amsawa kanta ba wani ya tursasata ba, don haka babu hannun sa a ciki. Nan kusa ma bai shirya mata tarewa ba ko inda zata zauna, don kamar yadda yace din ne da gaske bashi da bukatar ta cikin rayuwar sa ta yanzu.
Da dai Uncle da Ambasada sun sani da sun bar bygone a muhallin ta, don basu gama sanin ko wacece ‘yar su Rahinah ba har gobe, shiyasa suke tsammanin da zuciya daya ta amsa, shi kam ya dade da sanin cewa ya riga ya bata baya. Ya manta da ya taba auren ta, ya dade da karbar rayuwa a yadda ya same ta, kuma yana jin dadin ta a hakan. Da Rahinah, da babu ita, ba zai kasa rayuwa ba, insha Allahu.
Me jiya ta yi bare yau? Abin nufi me rashin ta na shekaru goma ya kara musu ko ya hana musu shi da Abdallahn?
Da wannan jinyar zuciyar kowannen su ke jibge akan gadon sa, ya dakatar da kowanne ayyuka na cigaban rayuwar sa da dailyactivities din sa.
Amma ga iyayen su da masoyan su abin ba haka yake ba, aunty Badiya, a ranar don farin cikin an daura wa Habibu aure da Rahinah, sai da ta kai goshin ta kasa ta yi sujjadar shukr, ta kuma dafa abinci mai rai da motsi ta rabawa mabukata sadaqah.
Hajiya Kaltume kuwa, ko da bata maraba da Rahinah, farin cikin yau Habibullahi yayi aure da azumi ta tashi a bakin ta.
Itama ta sa an dafa abincin sadaqa an raba a Kofar Jange har gidajen makwabtan ta, ko dama duk Juma’ah tana bada sadaqar naman saniya, da ake kayarwa a rabawa mabuqata na Kofar Jange, ranar da Uncle Usman ya tabbatar mata sun dauro auren suna kan hanyar dawowa Shanu uku ta sa aka kayar don yin sadaqah.
Nene Balki da Yafendo kuwa suna can suna yi wa Rahinah kyakkyawan shiri irin na iyayen kwarai masu shirin kai ‘yar fari daki, Nene tayi ordern kayan gyaran mata ‘yan gaske tafiyayyu tun daga Nijar. Ta kuma yi Magana da Yagana ‘yar Maiduguri mai yi mata gyaran jiki kan ta zo a washegari ta fara gyara Rahinah.
Sahura mai aikin Rahinah tana Kaduna, da Anty Badiya ta yi mata waya ta ce su fara shirin tarewa har rawa sai da ta taka. Don haka duk wani masoyin su cikin farin ciki yake, ya kuma ci wa auren nan alwashi da buri sabanin ma’auratan, wadanda ke ganin tamkar Alkiyamar su ta matso.
Kowanne gani yake an katse masa rayuwa an kuma hada shi da alaqaqai, tunda kar ce ta san kar, kowanne da irin alwashin da yake ci wa zuciyar sa a kan dan uwan sa.
Shi dai Habibu alwashi ya ci ba zai bari Rahinah ta shiga tsakanin sa da dan sa ba, tunda tare ta gan su, ta sake kutsowa cikin rayuwar su don ta kara tarwatsa ta.
Ita kuwa Rahinah abu daya ne yake sassauta zuciyar ta in ta tuna yanzu zata samu kusanci da Abdallah. Za ta maida hankalin ta ne kacokam kan cike wawakeken gibin da Habibu ya samar a tsakanin su wanda ta san ba zai yiwu a lokaci guda ba, sai ta yi da gaske wajen kwatowa kan ta soyayyar dan ta, ta cike ratar da Habibu ya janyo a tsakanin su.
Wannan shi ne kadai abin da zai zaunar da ita a gidan Habibu Nahuche amma ba Habibu ba; soyayyar dan ta Abdullahi!
Uwa uba farin cikin iyayen ta da kwanciyar hankalin su wato Ambasada da Uncle Usman. Ita kan ta Aunty Badiya Rahinah tana darajja ta, bata jin Habibu ya isa ya farraqa tsakanin su.
Domin Badiya ta kaunace ta kauna ta hakika tun kafin ta san alaqar da ke tsakanin su. A lokacin da ta ke neman dangin da za su rungume ta. Don haka ko wanene Habibu ga Badiya alaqar su mai kyau tana nan bazata taba canzawa ba saboda shi.
******
*Na huce* is not free.
It's 1000 via 3094856450
Sumayyah Kabara Firstbank