Sashe 5
Nahuce Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya riga ya gama binne ta daga zuciyar sa ba don ta mutu ba! Yana jin dadin rayuwar sa a haka, ba tare da Rahinah Omar a cikin ta ba.
Ita kuwa Rahinah nata tunanin daban yake, Abba Jakada, wato Ambasada Shehu ya fi karfin ya nemi kowacce irin alfarma daga gareta. A irin kalaman da ya yi mata amfani da su, babu tursasawa, a irin lallashin da ya yi mata babu bada umarni, face tsagwaron bata hakkin ta da addini ya ce a bata.
Sannan Ambasada ya ce za’a je neman auren ta ne cikin mutunci hannun iyayen ta karkashin tushen ta da asalin ta, babban abinda ya sa ta kullaci auren Habibu na baya kenan; auren ta da ya yi ba a hannun kowa nata ba, wannan kadai ya rankwafar da zuciyar Rahinah, amma ba don matsayin da ta aje Habibu ya canza ko kankani daga zuciyar ta ba.
Ba don feelings din ta a kan sa ya canza ba, har gobe yana nan a Habibun sa, dan mutanen Nahuche da har abada bazata yafewa ba. Aure ne a je a yi ta mayarwa tunda ta yarda ta amincewa ran ta tana son ABDALLAH, baza kuma ta iya rayuwa ta nutsuwa yanzu ba tare da shi ba, daga lokacin da ta dora ido a kan sa bayan wucewar shekaru goma. Bata kuma da wata hanya ta rayuwa tare da Abdallah yanzu, bayan komawa gidan su.
“’Ya ta Rahinatu kin min alfarmar? Kin amince a mayar da auren ku ki koma zama gida daya da dan ki Abdullahi karkashin inuwar auren mahaifin sa?”
Sai ta gyada kai sama cikin hawaye, wasu na korar wasu. A fili Ambasada ya jero Hamdala, Uncle Usman kuma a zuciyar sa yake yi, don shi ya so ba’a tsaya yi wa Rahinah wannan irin lallashin ba, kawai a maida auren in ya so ta kashe Habibu don kiyayya. Ya amince Habibu ba ya kin Rahinah, tata kiyayyar ta fi yawa.
Amma a yanzu ko shi ya fi jin dadin hakan, da bai zama cewa auren tursasawa ne zai kara gudana a tsakanin su ba, a zo a koma ‘yar gidan jiya.
Duk da haka Uncle Usman na tsoron Rahinah. Ya fahimci ba wai ta amince bane 100%. Ta amince ne kan ba yadda zata yi albarkacin Ambasada, albarkacin ya fi karfin kowacce alfarma daga gareta.
Sai a lokacin ya magantu, “in ma akwai abinda kika kudurta a ran ki ki sani Allah yana kallon ki, in ma ba don Allah kika amince ba duka ya rage naki, da hannu na dai bazan dauki ‘ya ta in baiwa bakon haure ba.
Mu za mu dan fita, ku yi amfani da wannan damar ku yi maganin matsalolin ku domin insha Allahu rabbi, sati mai zuwa za’a maida auren ku. Saura kuma ya rage naku. Duk wanda ya zalinci dan uwan sa ko da da kalaman fatar baki ne shi da Allah. Ubangiji SWA ya ce “Was-sulhu khair!”.
Da fadin haka, suka mike shi da Ambasada suka bar falon. Motsin kirki wannan babu wanda ya yi tsakanin Habib da Rahinah.
Kowanne zuciyar sa ta yi nauyi da sabon al’amarin da ke shirin samun sa, wato sake zama da juna a karo na biyu.
Rahinah ji tayi bazata iya cigaba da jurewa zama a inda Habibu yake ba. Gara ta tashi ta bar wurin kafin zuciyar ta ta yi bindiga da bakin cikin da ke cin ran ta. Ta san yanzu bakin alkalami ya riga ya bushe bata da sauran abun yi, bata isa ta dawo ta ce da dattijan nan ta janye alfarmar da ta yin ba. Amma cigaba da zaman ta a falon nan zai iya sawa ta yi hakan (tace ta janye din).
Gara mata zama waje daya da bakin maciji a kan zama kusa da Habibu Nahuche. Don haka ta mike cikin azama ba tare da ta dube shi ko ta ce da shi kanzil ba ta nufi kofa.
Da zuzzurfar muryar shi ya dago idanun shi da suka canza launi ya dubi bayan ta tana ficewa. Ya daga murya yadda za ta ji shi sosai.
“Gara miki ki koma ki warware musu fake yardar taki, na gaya maki, ina kara gaya miki we don’t need you in our lives anymore daga ni har Abdallah.
Bar ganin na yi shiru, ki dauka nima na amince ne, a’ah, su biyun nan suna da wata irin kima ne a idanu na da bazan iya yi musu musu ba. Amma wallahi gara duk matan duniya da ke Rahinah! Gara a aura min kowace ce da in kara hada rayuwa ta da ke”.
Wani lalataccen murmushi ne ya subuce a siririyar fatar bakin ta. Ta juyo gaba-gadi ta fuskanci Habibu.
“Ni da nace na amince, ce maka na yi har zuciyata ne? I just want to be with my son and nothing more, sabida bana so in kara jayayya a kan sa. Ka kwana da sanin Rahinar da ka sani da, ba ita ce yanzu ba, wadda ka ke raping a duk sanda ka so,wannan sai dai ku yi wrestling, ka shirya zama da sabuwar Rahinah mai ‘yanci, mai gata, tsayayya a kan kafafun ta. Auren ka ko rashin sa, ba zai kare ni da komai ba, banda Da na da zai dawo kusa da ni”.
Habibu ya yi murmushi wanda Kalmar ta ta wrestling ce sanadin sa, wasu irinbeautiful serene smiles, ko kadan kalaman ta basu yi masa ciwo ba, (as he expects words like these from her) domin ya tsammaci kalamai kamar su, ko ma fiye da su daga bakin ta, a duk ranar da suka sake haduwa. Don ta huce haushin ta.
Yace cikin ginshira.
“Rahane kike ko wa? Ki tuna yaron nan bai san ki ba, ni ya sani matsayin uwa da uban sa, don haka zuwan ki gidan su wai saboda shi, ba abinda zai sa, ba abinda zai hana.
Zan tabbata na gaya masa Uwar sa muguwa ce, azzaluma ce akan Uban sa, wadda bata cancanci yafiya da soyayya daga gareshi ba. Bata taba waiwayar sa ba tsayin shekara goma sai don ta gan shi a akan hanya.
My boy is smart, kuma da wayon sa da hankalin sa, ba kowacce karabiti ce zata zo ta ce da shi ita ta haife shi ba ya yarda….”.
Yatsunta biyu ta sa ta toshe kunnuwan ta, sannan ta karasa ficewa da ga falon da dan banzan sauri. Har tana cin uban tuntube tare da sa hannu ta toshe bakin ta daga azababben kukan da ke son kubuce mata.
*******
*ME YE ABIN YI?*
Dakin Yafendo ta nufa tana kuka wiwi, ta soma hada komai nata da zummar komawa gidan ta. Yafendo, bata ce mata ko uffan ba domin cike take da farin cikin maida auren da Abba Jakada ya ce mata za’a yi ranar Juma’ah mai zuwa.
Nene ce ta shigo dakin ganin Rahinah ta sunkuto Jakar ta tace “Rahinah, babu inda zaki koma fa, daga nan gidan sai gidan mijin ki, za’a je a kwaso komai na gidan gobe da safe insha Allahu”.
Ta fada jikin Nene tana kuka “Nene wallahi har gobe ba ya so na, nima bana son shi, Da na kawai nake so”.
Nene abin sai ya koma bata dariya Yafendo kuwa haushi ne ya kama ta, tace “shi SON ya ci uwatar, ya ci Uba nai, mu da iyayen mu suka yi mana aure bamu taba ganin mijin ba fa sai a gidan sa? Ba gashi mun haifi wadanda suka haife ku ba babu soyayyar? Aka bar duniya ana begen juna, ku kuka dauki soyayya wata tsiya, ba kya son shi kika hada shimfida da shi har kuka haifi Da?
Ina ce karewar so kenan ka hada shimfida miji?”
Nene na ta dariya ta ce Yafendo wannan ai ba sai da so ba, kaddara ne, umarnin Ubangiji ne, amma ni in zata dau lasifika ta hau duro tana yekuwar bata son Habibu ba zan taba yarda ba, domin na sha kamata tana searching (browsing) din sa a yanar gizo, har da saving hotunan sa cikin wayar ta da kwamfutar ta, in babu so me ya kawo wannnan? Wanda ba ka so meye naka na bin kwakkwafin sa?”
Rahinah ta rasa inda zata sa kanta don bakin cikin abinda Nene ke fada, kamar ta dora hannu aka ta saka ihu, Nene ta cigaba da baiwa Yafendo labarin ranar data kama ta da hoton sa cikin kwamfuta tun suna Frankfurt.
Yafendo ta ce “ahap! Ai shi munafurci dodo ne mai shi yake ci, aure kuma an mayar an gama da iznin Allah”.
A fusace Rahinah ta bar dakin zuwa nata dakin da ke gidan, ta shige ta rufe har da key. Nene da Yafendo basu kara bi ta kan ta ba a gidan. A take Nene ta kira Aunty Badiya.
Suka gaisa, suka taya juna murna na maida auren da za’a yi, amma jikin Aunty Badiya a sanyaye yake, don a lokacin tana can tana fama da Hajiyar Nahuche wadda ta ce gara Habibu ya hakura da Rahinah, don bata hango masa kwanciyar hankali a sake zama da ita ba. Matar da zata kai ka gaban Alkali tabbas bata son ka, Aunty ta ce,
“Hajiya ki rabu da Rahinah ba halin ta bane, bacin rai ne ya kai ta ga hakan. Amma ba don bata son Habibu ba”.
Don haka da Nene ta bugo yanzu suka yi wa juna murna sai ta ke yi wa Hajiya Haj. Kaltume bayanin marikiyar Rahinan ce ta bugo, komai ya daidaita ta bangaren su sai jiran ranar daurin aure.
Kuma dama Uncle Usman ya kira su ya gaya musu sati mai zuwa za’a je Girei a maida auren don Hajiya ta sanar da iyayen sa maza da zasu je su karba masa auren daga garin Nahuche, Hajiya dai kadaran-kadahan ta amsa don Rahinah ta gama sire mata, da ta yi wannan danyen aikin, kamar wadda bata da mafadi ko mashawarci.
Don ta ita a hakura da Rahinah a nemawa Habibu wata, abu daya take tunawa ta hakura wato Abdallah. Tana matukar son ya cigaba da girma karkashin kulawar iyayen sa biyu, ya daina walagigi tasakanin Zamfara da Kaduna.
Ita kuwa Rahinah nata tunanin daban yake, Abba Jakada, wato Ambasada Shehu ya fi karfin ya nemi kowacce irin alfarma daga gareta. A irin kalaman da ya yi mata amfani da su, babu tursasawa, a irin lallashin da ya yi mata babu bada umarni, face tsagwaron bata hakkin ta da addini ya ce a bata.
Sannan Ambasada ya ce za’a je neman auren ta ne cikin mutunci hannun iyayen ta karkashin tushen ta da asalin ta, babban abinda ya sa ta kullaci auren Habibu na baya kenan; auren ta da ya yi ba a hannun kowa nata ba, wannan kadai ya rankwafar da zuciyar Rahinah, amma ba don matsayin da ta aje Habibu ya canza ko kankani daga zuciyar ta ba.
Ba don feelings din ta a kan sa ya canza ba, har gobe yana nan a Habibun sa, dan mutanen Nahuche da har abada bazata yafewa ba. Aure ne a je a yi ta mayarwa tunda ta yarda ta amincewa ran ta tana son ABDALLAH, baza kuma ta iya rayuwa ta nutsuwa yanzu ba tare da shi ba, daga lokacin da ta dora ido a kan sa bayan wucewar shekaru goma. Bata kuma da wata hanya ta rayuwa tare da Abdallah yanzu, bayan komawa gidan su.
“’Ya ta Rahinatu kin min alfarmar? Kin amince a mayar da auren ku ki koma zama gida daya da dan ki Abdullahi karkashin inuwar auren mahaifin sa?”
Sai ta gyada kai sama cikin hawaye, wasu na korar wasu. A fili Ambasada ya jero Hamdala, Uncle Usman kuma a zuciyar sa yake yi, don shi ya so ba’a tsaya yi wa Rahinah wannan irin lallashin ba, kawai a maida auren in ya so ta kashe Habibu don kiyayya. Ya amince Habibu ba ya kin Rahinah, tata kiyayyar ta fi yawa.
Amma a yanzu ko shi ya fi jin dadin hakan, da bai zama cewa auren tursasawa ne zai kara gudana a tsakanin su ba, a zo a koma ‘yar gidan jiya.
Duk da haka Uncle Usman na tsoron Rahinah. Ya fahimci ba wai ta amince bane 100%. Ta amince ne kan ba yadda zata yi albarkacin Ambasada, albarkacin ya fi karfin kowacce alfarma daga gareta.
Sai a lokacin ya magantu, “in ma akwai abinda kika kudurta a ran ki ki sani Allah yana kallon ki, in ma ba don Allah kika amince ba duka ya rage naki, da hannu na dai bazan dauki ‘ya ta in baiwa bakon haure ba.
Mu za mu dan fita, ku yi amfani da wannan damar ku yi maganin matsalolin ku domin insha Allahu rabbi, sati mai zuwa za’a maida auren ku. Saura kuma ya rage naku. Duk wanda ya zalinci dan uwan sa ko da da kalaman fatar baki ne shi da Allah. Ubangiji SWA ya ce “Was-sulhu khair!”.
Da fadin haka, suka mike shi da Ambasada suka bar falon. Motsin kirki wannan babu wanda ya yi tsakanin Habib da Rahinah.
Kowanne zuciyar sa ta yi nauyi da sabon al’amarin da ke shirin samun sa, wato sake zama da juna a karo na biyu.
Rahinah ji tayi bazata iya cigaba da jurewa zama a inda Habibu yake ba. Gara ta tashi ta bar wurin kafin zuciyar ta ta yi bindiga da bakin cikin da ke cin ran ta. Ta san yanzu bakin alkalami ya riga ya bushe bata da sauran abun yi, bata isa ta dawo ta ce da dattijan nan ta janye alfarmar da ta yin ba. Amma cigaba da zaman ta a falon nan zai iya sawa ta yi hakan (tace ta janye din).
Gara mata zama waje daya da bakin maciji a kan zama kusa da Habibu Nahuche. Don haka ta mike cikin azama ba tare da ta dube shi ko ta ce da shi kanzil ba ta nufi kofa.
Da zuzzurfar muryar shi ya dago idanun shi da suka canza launi ya dubi bayan ta tana ficewa. Ya daga murya yadda za ta ji shi sosai.
“Gara miki ki koma ki warware musu fake yardar taki, na gaya maki, ina kara gaya miki we don’t need you in our lives anymore daga ni har Abdallah.
Bar ganin na yi shiru, ki dauka nima na amince ne, a’ah, su biyun nan suna da wata irin kima ne a idanu na da bazan iya yi musu musu ba. Amma wallahi gara duk matan duniya da ke Rahinah! Gara a aura min kowace ce da in kara hada rayuwa ta da ke”.
Wani lalataccen murmushi ne ya subuce a siririyar fatar bakin ta. Ta juyo gaba-gadi ta fuskanci Habibu.
“Ni da nace na amince, ce maka na yi har zuciyata ne? I just want to be with my son and nothing more, sabida bana so in kara jayayya a kan sa. Ka kwana da sanin Rahinar da ka sani da, ba ita ce yanzu ba, wadda ka ke raping a duk sanda ka so,wannan sai dai ku yi wrestling, ka shirya zama da sabuwar Rahinah mai ‘yanci, mai gata, tsayayya a kan kafafun ta. Auren ka ko rashin sa, ba zai kare ni da komai ba, banda Da na da zai dawo kusa da ni”.
Habibu ya yi murmushi wanda Kalmar ta ta wrestling ce sanadin sa, wasu irinbeautiful serene smiles, ko kadan kalaman ta basu yi masa ciwo ba, (as he expects words like these from her) domin ya tsammaci kalamai kamar su, ko ma fiye da su daga bakin ta, a duk ranar da suka sake haduwa. Don ta huce haushin ta.
Yace cikin ginshira.
“Rahane kike ko wa? Ki tuna yaron nan bai san ki ba, ni ya sani matsayin uwa da uban sa, don haka zuwan ki gidan su wai saboda shi, ba abinda zai sa, ba abinda zai hana.
Zan tabbata na gaya masa Uwar sa muguwa ce, azzaluma ce akan Uban sa, wadda bata cancanci yafiya da soyayya daga gareshi ba. Bata taba waiwayar sa ba tsayin shekara goma sai don ta gan shi a akan hanya.
My boy is smart, kuma da wayon sa da hankalin sa, ba kowacce karabiti ce zata zo ta ce da shi ita ta haife shi ba ya yarda….”.
Yatsunta biyu ta sa ta toshe kunnuwan ta, sannan ta karasa ficewa da ga falon da dan banzan sauri. Har tana cin uban tuntube tare da sa hannu ta toshe bakin ta daga azababben kukan da ke son kubuce mata.
*******
*ME YE ABIN YI?*
Dakin Yafendo ta nufa tana kuka wiwi, ta soma hada komai nata da zummar komawa gidan ta. Yafendo, bata ce mata ko uffan ba domin cike take da farin cikin maida auren da Abba Jakada ya ce mata za’a yi ranar Juma’ah mai zuwa.
Nene ce ta shigo dakin ganin Rahinah ta sunkuto Jakar ta tace “Rahinah, babu inda zaki koma fa, daga nan gidan sai gidan mijin ki, za’a je a kwaso komai na gidan gobe da safe insha Allahu”.
Ta fada jikin Nene tana kuka “Nene wallahi har gobe ba ya so na, nima bana son shi, Da na kawai nake so”.
Nene abin sai ya koma bata dariya Yafendo kuwa haushi ne ya kama ta, tace “shi SON ya ci uwatar, ya ci Uba nai, mu da iyayen mu suka yi mana aure bamu taba ganin mijin ba fa sai a gidan sa? Ba gashi mun haifi wadanda suka haife ku ba babu soyayyar? Aka bar duniya ana begen juna, ku kuka dauki soyayya wata tsiya, ba kya son shi kika hada shimfida da shi har kuka haifi Da?
Ina ce karewar so kenan ka hada shimfida miji?”
Nene na ta dariya ta ce Yafendo wannan ai ba sai da so ba, kaddara ne, umarnin Ubangiji ne, amma ni in zata dau lasifika ta hau duro tana yekuwar bata son Habibu ba zan taba yarda ba, domin na sha kamata tana searching (browsing) din sa a yanar gizo, har da saving hotunan sa cikin wayar ta da kwamfutar ta, in babu so me ya kawo wannnan? Wanda ba ka so meye naka na bin kwakkwafin sa?”
Rahinah ta rasa inda zata sa kanta don bakin cikin abinda Nene ke fada, kamar ta dora hannu aka ta saka ihu, Nene ta cigaba da baiwa Yafendo labarin ranar data kama ta da hoton sa cikin kwamfuta tun suna Frankfurt.
Yafendo ta ce “ahap! Ai shi munafurci dodo ne mai shi yake ci, aure kuma an mayar an gama da iznin Allah”.
A fusace Rahinah ta bar dakin zuwa nata dakin da ke gidan, ta shige ta rufe har da key. Nene da Yafendo basu kara bi ta kan ta ba a gidan. A take Nene ta kira Aunty Badiya.
Suka gaisa, suka taya juna murna na maida auren da za’a yi, amma jikin Aunty Badiya a sanyaye yake, don a lokacin tana can tana fama da Hajiyar Nahuche wadda ta ce gara Habibu ya hakura da Rahinah, don bata hango masa kwanciyar hankali a sake zama da ita ba. Matar da zata kai ka gaban Alkali tabbas bata son ka, Aunty ta ce,
“Hajiya ki rabu da Rahinah ba halin ta bane, bacin rai ne ya kai ta ga hakan. Amma ba don bata son Habibu ba”.
Don haka da Nene ta bugo yanzu suka yi wa juna murna sai ta ke yi wa Hajiya Haj. Kaltume bayanin marikiyar Rahinan ce ta bugo, komai ya daidaita ta bangaren su sai jiran ranar daurin aure.
Kuma dama Uncle Usman ya kira su ya gaya musu sati mai zuwa za’a je Girei a maida auren don Hajiya ta sanar da iyayen sa maza da zasu je su karba masa auren daga garin Nahuche, Hajiya dai kadaran-kadahan ta amsa don Rahinah ta gama sire mata, da ta yi wannan danyen aikin, kamar wadda bata da mafadi ko mashawarci.
Don ta ita a hakura da Rahinah a nemawa Habibu wata, abu daya take tunawa ta hakura wato Abdallah. Tana matukar son ya cigaba da girma karkashin kulawar iyayen sa biyu, ya daina walagigi tasakanin Zamfara da Kaduna.