Sashe 1
Nahuce Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
[8/10, 4:36 PM] +234 816 049 3429: SUMAYYAH ABDULKADIR TAKORI 07030137870
*HABIBU NAHUCHE*
Ya bai wa kan sa hutu ne domin ya gama fahimtar a hargitse yake, ci gaba da ayyukan sa a wannan halin da ya ke ciki ba abin da zai haifar sai tarin nakasu da koma baya cikin harkokin kasuwancin sa. Domin hatta lissafi kowa da ke tare da shi ya san ya daina yin sa daidai.
Ya dauka komai nata ya tafi, tafiyar da babu dawowa, ya dauka ya riga ya binne ta a zuciyar sa ba don ta mutu ba, sai don ta gama taka rawar ta a rayuwar sa, ya dauka komai nata ya zama bygone? Tunda bai hana shi progressing ba. Amma ashe likimo ta yi wa zuciyar sa mai kama da kwanton Bauna!
Daga lokacin da idanun sa suka shiga cikin those innocent fulani eyes din na Rahinah Omar, komai ya dawo masa sabo fil. Wai kunama ta harbi gyambo.
In ma ya ce har da kari ba zai yi karya ba. Yanzu ya gan ta ne a matsayin cikakkiyar mace (matured young lady in her late twenties fiye da yadda ta ke a baya. Yanzu ne ta ke amsa sunan mace sosai, ta ke amsa sunan (Dr. Rahinah Omar Girei Otorhinolaryngologist) ba 'yar yarinya budurwa mai tsananin kyau da ya sani a Jamus, mai amsa sunan Rahinah Omar ba.
Wannan kyan na yanzu hade yake da sanin ciwon kai, matured mind, contentment of life.
A halin yanzu ka ganta tsammani za ka yi balarabiyar kasar Oman ce sabida yadda fatar jikinta ke glittering.
Dr. Irshad bai iya boye hakan a ran sa, a duk lokacin da ya ga Rahinah ko wani aiki ya kawo ta ofishin sa sai ya fada kasa-kasa cewa, ‘Looking Ravishing'.
A duk sanda ya fadi hakan ita kuma za ta yi kicin-kicin da fuska, don duk namijin da ya yabe ta haushi yake ba ta.
Habibu Nahuche has never praised her beauty, watakila bai ma san ya ake gaya wa mace abin da zai dadada mata rai ba. Yet shi kadai yake burge ta, shi kadai ta ke so ta ji ya yabi wani abu nata. Unfortunately bai taba ba, sunan ta “muguwa-azzaluma” a bakin sa.
Watakila wadannan muggan kalaman nasa da suka haukata ta a kwanakin nan, su za su cigaba da birkitata suna farautar farin cikin ta da nutsuwar ta har zuwa ranar da ta daina numfashi.
*******
Duk da bai san wace irin alaka ce tsakanin ta da su Uncle Usman ba, ya fahimci alaka ce ta kusa ba ta nesa ba.
Maimakon ya samu hutu kamar yadda yake bukata cikin ’Nahuche Hotel’ na garin Ikko, tun bayan da ya sada Abdallah da ‘Boarding School’ don ma kada Rahinah ta samu access din sake ganin sa, sai kadaicin ya bankado wa zuciyar sa tsohon kundi da tsohon miki na rayuwar KWANAKI BAKWAI a birnin Cologne din JAMUS.
Rayuwar da har yau bai kara maimaitawa ba, bai kara samun kwatankwacin ta a gardi ba, bai kara attemptingdin ta da kowacce ’ya mace ba tsayin shekaru goma, wato rayuwar auratayyah! For she left no space in him. Ta mamaye ko’ina na zuciyar sa.
Ya rike kan sa ta duk hanyar da addini yayi umarni, ta hanyar maida kan sa busy kullum, da neman kudi da azumin tadawwu’i don kada ya tuna ta. Don kada ya nemi mata. Ya sani ba irin mummunan zargin da duniya bata yi masa akan rashin aure.
Idan ya ce yana sufferinginternally a cikin wannan dan tsakanin, ya yi kadan ya bayyana irin halin da ya samu kan sa. Ganin ta ya tuna masa cewa shima NAMIJI ne mai lafiyar bukatar aure, don a baya ya dauka ya dade da komawa mace. Sabida kowacce macen kallon mata-maza yake mata sai ko yau da ya ga RahinahOmar ganin idanun sa, ya kuma ji muryar ta jin kunnen sa…
******
*ASHE RAHINAH BAKI SAN GATSE BA?*
Mr. Atiku wato PA din sa na Abuja ne ya kira shi, da bai same shi ba, sai ya kira PA din Lagos. Rasak. Cikin tashin hankali yake gaya masa ya hada shi da Oga, itisurgent. Shi kuma yace masa Oga fa ba ya amsa waya currently, yana hutu a Hotel, ajiyar zuciya PA din Abuja ya yi, yace.
"Sai ka gaya masa hutu bai gan shi ba, an turo masa da SAMMACI daga Federal High Court, Abuja, kuma zance har ya bullawa media.
He has to be in Abuja today or tomorrow a kashe zancen nan kafin 'Daily Trust’ su shigar da jaridar da zasu fitar jibi zuwa yanar gizon su, ko su fara sayar da ita a kan takarda.
Ban san wa ya kai musu zancen ba kuma ban san wa ya yi karar sa ba. Amma hakika a kan yaron sa ne, Abdallah. Har suna questioninglegitimacy din sa dalilin hakan. Ana neman sa nan da kwana uku a kotu!”.
Jeremy da ke kula da abincin sa shi ya shigo masa da jaridar yau da ya sayo tare da lunch din sa. PA dinsa ne ya ce ya kai masa jaridar tare da abincin rana, tunda sun yi-sun yi da shi akan ya daga waya don su gaya masa yayi wani abu kafin ’Daily Trust’ su saki labarin, amma ko damar ganin sa bai basu ba balle ya san abinda ke faruwa.
Headline na jaridar Sabuwar Najeriya (NEW NIGERIA) dauke ya ke da kanun labaru kamar haka…..
"NAHUCHE’S EX-WIFE DRAGS HIM TO COURT, ACCUSES HIM OF INJUSTICE ON THEIR CHILD’S CUSTODY….DR. RAHINAH OMAR OF NIZAMIYE APPEALS THE COURT FOR JUSTICE...
Yayin da Headline na 'Daily Trust’ ya ce.
"IS ABDALLAH NAHUCHE A LEGITIMATE CHILD???”
A cikin kanun labaran kuma an yi bayanin zuwan sa Germany karatu, tare da dawowa da yayi tare da karamin yaron, ba tareda kowa nasa ya shaida auren sa ba.
“No one knows how, and where Habibu Nahuche got his beautiful son Abdallah in GERMANY…..not even his Mother….”.
Ba da niyyar cin abinci ya fito falon ba, ya fito ne domin ya dauki wayar sa da ya bari akan diningtable din. Babban abinda ya fizgi hankalin sa kan jaridar da ke ajiye shine hoton Abdallah a fuskar jarida, sai na shi dana Rahinah, a kagauce ya bi headlines din. Wadanda suka sa wani irin gumi tsatstsafo masa.
“Ita kenan bata san gatse ba?! Ashe Rahinah bata da hankali da hangen nesa har yanzu tana nan yadda take da kafiya da taurin kan ta? Nauyin shekaru ba su kara mata komai ba daga sanin da ya yi mata a baya, basu canza ta ba haka basu ishe ta yin hankali ba?
Har yanzu tana nan a sha yanzu magani yanzun ta! (not giving things a second thought)”.
Ya tambayi kan sa cikin tasowar wani matsanancin bacin rai, da bai taba ji a rayuwar sa ba, ba don yana shayin kotu zata kwace masa Abdallah ta bata ba, sai tunanin wannan tereren da ta ja musu, da Dan sa da ya ji ana kokarin sheganta masa!”
A take ya yi waya yayi booking jirgi mai zuwa Abuja, da zummar zai je yau ya fuskanci Dr. Rahinah Omar da duk abinda take taqama da shi a duniya, sai ta gwammace bata yi karar nan ba…sai ta gwammace bata san shi ba, sai ta gwammace wata alaqa bata taba hada su ba. Yau za ta san ko waye "REAL Habibu Nahuche” domin zai fiddo mata truecolour din sa.
Abdallah kuma sai dai ta daukaka kara zuwa SupremeCourt, (Federal High Court) ta yi tsararo ta kwatar mata shi, kai duk duniya bai ga kotun data isa kwatar Abdallah ba a kasar nan da wajen ta daga hannun sa……
(Babban bacin ran Habibu Nahuche ba karar sa da Rahinah tayi gaban Alkali bane, kamar shegan ta masa Abdallah da ta janyo ake kokarin yi a kafafen yada labarai babu gaira babu dalili, sai don neman magana da neman suna irin na ’yan jarida).
******
*ABUJA*
Kafin ka ce meye wannan labarin ya bazu kamar wutar daji a media, musamman cikin birnin tarayyah, kowace jarida tun daga ta cikin gida wato LEADERSHIP har Daily Tribune da Sahara Reporters ta maida shi headline din ta na wannnan satin. FACEBOOK, TWITTER, WHATSAPP groups kuwa sun maida shi ’topic of discussion’ hotunan Habibu da Rahinah da kyakkyawan dan su Abdullahi ya baibaye wayoyin al’ummah. Kowa yana fadin albarkacin bakin sa mai dadi da marar dadi.
Duk wanda ya kwana da sanin Habibu Nahuche (Lucky), Hotelier, ya ji labarin tsohuwar matar sa ta maka shi a kotu kan ya bata dan ta, dan da ba’a da tabbacin na halaal ne don a kasar Germany suka haife shi ba da sanin kowa nasu ba.
Washegari Aunty da Uncle suka bi bayan su zuwa wajen Hajiya, Aunty ta tabbatar wa Uncle babu inda Habibu zai je da Abdallah sai Zamfara, don ba zai iya yawon jihohin Najeriya da yake yi da yaron ba, don ba ya so jama'a suna tanka wa a kan tsananin kamannin da ke tsakanin sa da yaron.
A cewar sa don kada baki ya kama shi. Yana guje masa kambun baka. Don haka Aunty ba ta raba dayan biyun tabbas Zamfara suka nufa.
Ilai kuwa Hajiya Kaltume sai ganin Aunty da maigidanta ta yi sun yi sallama suna shigowa.
Suka zazzauna suna gaggaisawa da Hajiya cikin tsananin girmamawa. Hajiya ta ce,
"Ni laifin me kuka yi wa Baban Abdallah ne?”
Dariya Aunty da Daddy suka yi a tare, Aunty ta ce,
"Babu laifin fa da muka yi masa. Laifin mu daya kasancewar mu iyayen mahaifiyar Abdallah".
Hajiya ta dan zamo jikin ta daga cikin kujerar ta, ta tattara hankalin ta kan babbar diyar ta, cikin rashin fahimta ta ce.
"Wace mahaifiyar Abdallahn?"
Aunty ba ta bata lokaci ba, ta ce, "Dr. Rahinah, mahaifiyar sa wadda ta haife shi, matar Habibu a Jamus, wadda ta guje shi.
Diya ta ke ta halali ga Baban su Musaddiq shi da mahaifin ta mai rasuwa ciki daya suka fito".
Hajiyar Nahuche ba ta san sanda ta ce, "Allahu Akbar!" ba, "Allah da iko Yake, to ya aka yi da can ba mu sani ba?"
*HABIBU NAHUCHE*
Ya bai wa kan sa hutu ne domin ya gama fahimtar a hargitse yake, ci gaba da ayyukan sa a wannan halin da ya ke ciki ba abin da zai haifar sai tarin nakasu da koma baya cikin harkokin kasuwancin sa. Domin hatta lissafi kowa da ke tare da shi ya san ya daina yin sa daidai.
Ya dauka komai nata ya tafi, tafiyar da babu dawowa, ya dauka ya riga ya binne ta a zuciyar sa ba don ta mutu ba, sai don ta gama taka rawar ta a rayuwar sa, ya dauka komai nata ya zama bygone? Tunda bai hana shi progressing ba. Amma ashe likimo ta yi wa zuciyar sa mai kama da kwanton Bauna!
Daga lokacin da idanun sa suka shiga cikin those innocent fulani eyes din na Rahinah Omar, komai ya dawo masa sabo fil. Wai kunama ta harbi gyambo.
In ma ya ce har da kari ba zai yi karya ba. Yanzu ya gan ta ne a matsayin cikakkiyar mace (matured young lady in her late twenties fiye da yadda ta ke a baya. Yanzu ne ta ke amsa sunan mace sosai, ta ke amsa sunan (Dr. Rahinah Omar Girei Otorhinolaryngologist) ba 'yar yarinya budurwa mai tsananin kyau da ya sani a Jamus, mai amsa sunan Rahinah Omar ba.
Wannan kyan na yanzu hade yake da sanin ciwon kai, matured mind, contentment of life.
A halin yanzu ka ganta tsammani za ka yi balarabiyar kasar Oman ce sabida yadda fatar jikinta ke glittering.
Dr. Irshad bai iya boye hakan a ran sa, a duk lokacin da ya ga Rahinah ko wani aiki ya kawo ta ofishin sa sai ya fada kasa-kasa cewa, ‘Looking Ravishing'.
A duk sanda ya fadi hakan ita kuma za ta yi kicin-kicin da fuska, don duk namijin da ya yabe ta haushi yake ba ta.
Habibu Nahuche has never praised her beauty, watakila bai ma san ya ake gaya wa mace abin da zai dadada mata rai ba. Yet shi kadai yake burge ta, shi kadai ta ke so ta ji ya yabi wani abu nata. Unfortunately bai taba ba, sunan ta “muguwa-azzaluma” a bakin sa.
Watakila wadannan muggan kalaman nasa da suka haukata ta a kwanakin nan, su za su cigaba da birkitata suna farautar farin cikin ta da nutsuwar ta har zuwa ranar da ta daina numfashi.
*******
Duk da bai san wace irin alaka ce tsakanin ta da su Uncle Usman ba, ya fahimci alaka ce ta kusa ba ta nesa ba.
Maimakon ya samu hutu kamar yadda yake bukata cikin ’Nahuche Hotel’ na garin Ikko, tun bayan da ya sada Abdallah da ‘Boarding School’ don ma kada Rahinah ta samu access din sake ganin sa, sai kadaicin ya bankado wa zuciyar sa tsohon kundi da tsohon miki na rayuwar KWANAKI BAKWAI a birnin Cologne din JAMUS.
Rayuwar da har yau bai kara maimaitawa ba, bai kara samun kwatankwacin ta a gardi ba, bai kara attemptingdin ta da kowacce ’ya mace ba tsayin shekaru goma, wato rayuwar auratayyah! For she left no space in him. Ta mamaye ko’ina na zuciyar sa.
Ya rike kan sa ta duk hanyar da addini yayi umarni, ta hanyar maida kan sa busy kullum, da neman kudi da azumin tadawwu’i don kada ya tuna ta. Don kada ya nemi mata. Ya sani ba irin mummunan zargin da duniya bata yi masa akan rashin aure.
Idan ya ce yana sufferinginternally a cikin wannan dan tsakanin, ya yi kadan ya bayyana irin halin da ya samu kan sa. Ganin ta ya tuna masa cewa shima NAMIJI ne mai lafiyar bukatar aure, don a baya ya dauka ya dade da komawa mace. Sabida kowacce macen kallon mata-maza yake mata sai ko yau da ya ga RahinahOmar ganin idanun sa, ya kuma ji muryar ta jin kunnen sa…
******
*ASHE RAHINAH BAKI SAN GATSE BA?*
Mr. Atiku wato PA din sa na Abuja ne ya kira shi, da bai same shi ba, sai ya kira PA din Lagos. Rasak. Cikin tashin hankali yake gaya masa ya hada shi da Oga, itisurgent. Shi kuma yace masa Oga fa ba ya amsa waya currently, yana hutu a Hotel, ajiyar zuciya PA din Abuja ya yi, yace.
"Sai ka gaya masa hutu bai gan shi ba, an turo masa da SAMMACI daga Federal High Court, Abuja, kuma zance har ya bullawa media.
He has to be in Abuja today or tomorrow a kashe zancen nan kafin 'Daily Trust’ su shigar da jaridar da zasu fitar jibi zuwa yanar gizon su, ko su fara sayar da ita a kan takarda.
Ban san wa ya kai musu zancen ba kuma ban san wa ya yi karar sa ba. Amma hakika a kan yaron sa ne, Abdallah. Har suna questioninglegitimacy din sa dalilin hakan. Ana neman sa nan da kwana uku a kotu!”.
Jeremy da ke kula da abincin sa shi ya shigo masa da jaridar yau da ya sayo tare da lunch din sa. PA dinsa ne ya ce ya kai masa jaridar tare da abincin rana, tunda sun yi-sun yi da shi akan ya daga waya don su gaya masa yayi wani abu kafin ’Daily Trust’ su saki labarin, amma ko damar ganin sa bai basu ba balle ya san abinda ke faruwa.
Headline na jaridar Sabuwar Najeriya (NEW NIGERIA) dauke ya ke da kanun labaru kamar haka…..
"NAHUCHE’S EX-WIFE DRAGS HIM TO COURT, ACCUSES HIM OF INJUSTICE ON THEIR CHILD’S CUSTODY….DR. RAHINAH OMAR OF NIZAMIYE APPEALS THE COURT FOR JUSTICE...
Yayin da Headline na 'Daily Trust’ ya ce.
"IS ABDALLAH NAHUCHE A LEGITIMATE CHILD???”
A cikin kanun labaran kuma an yi bayanin zuwan sa Germany karatu, tare da dawowa da yayi tare da karamin yaron, ba tareda kowa nasa ya shaida auren sa ba.
“No one knows how, and where Habibu Nahuche got his beautiful son Abdallah in GERMANY…..not even his Mother….”.
Ba da niyyar cin abinci ya fito falon ba, ya fito ne domin ya dauki wayar sa da ya bari akan diningtable din. Babban abinda ya fizgi hankalin sa kan jaridar da ke ajiye shine hoton Abdallah a fuskar jarida, sai na shi dana Rahinah, a kagauce ya bi headlines din. Wadanda suka sa wani irin gumi tsatstsafo masa.
“Ita kenan bata san gatse ba?! Ashe Rahinah bata da hankali da hangen nesa har yanzu tana nan yadda take da kafiya da taurin kan ta? Nauyin shekaru ba su kara mata komai ba daga sanin da ya yi mata a baya, basu canza ta ba haka basu ishe ta yin hankali ba?
Har yanzu tana nan a sha yanzu magani yanzun ta! (not giving things a second thought)”.
Ya tambayi kan sa cikin tasowar wani matsanancin bacin rai, da bai taba ji a rayuwar sa ba, ba don yana shayin kotu zata kwace masa Abdallah ta bata ba, sai tunanin wannan tereren da ta ja musu, da Dan sa da ya ji ana kokarin sheganta masa!”
A take ya yi waya yayi booking jirgi mai zuwa Abuja, da zummar zai je yau ya fuskanci Dr. Rahinah Omar da duk abinda take taqama da shi a duniya, sai ta gwammace bata yi karar nan ba…sai ta gwammace bata san shi ba, sai ta gwammace wata alaqa bata taba hada su ba. Yau za ta san ko waye "REAL Habibu Nahuche” domin zai fiddo mata truecolour din sa.
Abdallah kuma sai dai ta daukaka kara zuwa SupremeCourt, (Federal High Court) ta yi tsararo ta kwatar mata shi, kai duk duniya bai ga kotun data isa kwatar Abdallah ba a kasar nan da wajen ta daga hannun sa……
(Babban bacin ran Habibu Nahuche ba karar sa da Rahinah tayi gaban Alkali bane, kamar shegan ta masa Abdallah da ta janyo ake kokarin yi a kafafen yada labarai babu gaira babu dalili, sai don neman magana da neman suna irin na ’yan jarida).
******
*ABUJA*
Kafin ka ce meye wannan labarin ya bazu kamar wutar daji a media, musamman cikin birnin tarayyah, kowace jarida tun daga ta cikin gida wato LEADERSHIP har Daily Tribune da Sahara Reporters ta maida shi headline din ta na wannnan satin. FACEBOOK, TWITTER, WHATSAPP groups kuwa sun maida shi ’topic of discussion’ hotunan Habibu da Rahinah da kyakkyawan dan su Abdullahi ya baibaye wayoyin al’ummah. Kowa yana fadin albarkacin bakin sa mai dadi da marar dadi.
Duk wanda ya kwana da sanin Habibu Nahuche (Lucky), Hotelier, ya ji labarin tsohuwar matar sa ta maka shi a kotu kan ya bata dan ta, dan da ba’a da tabbacin na halaal ne don a kasar Germany suka haife shi ba da sanin kowa nasu ba.
Washegari Aunty da Uncle suka bi bayan su zuwa wajen Hajiya, Aunty ta tabbatar wa Uncle babu inda Habibu zai je da Abdallah sai Zamfara, don ba zai iya yawon jihohin Najeriya da yake yi da yaron ba, don ba ya so jama'a suna tanka wa a kan tsananin kamannin da ke tsakanin sa da yaron.
A cewar sa don kada baki ya kama shi. Yana guje masa kambun baka. Don haka Aunty ba ta raba dayan biyun tabbas Zamfara suka nufa.
Ilai kuwa Hajiya Kaltume sai ganin Aunty da maigidanta ta yi sun yi sallama suna shigowa.
Suka zazzauna suna gaggaisawa da Hajiya cikin tsananin girmamawa. Hajiya ta ce,
"Ni laifin me kuka yi wa Baban Abdallah ne?”
Dariya Aunty da Daddy suka yi a tare, Aunty ta ce,
"Babu laifin fa da muka yi masa. Laifin mu daya kasancewar mu iyayen mahaifiyar Abdallah".
Hajiya ta dan zamo jikin ta daga cikin kujerar ta, ta tattara hankalin ta kan babbar diyar ta, cikin rashin fahimta ta ce.
"Wace mahaifiyar Abdallahn?"
Aunty ba ta bata lokaci ba, ta ce, "Dr. Rahinah, mahaifiyar sa wadda ta haife shi, matar Habibu a Jamus, wadda ta guje shi.
Diya ta ke ta halali ga Baban su Musaddiq shi da mahaifin ta mai rasuwa ciki daya suka fito".
Hajiyar Nahuche ba ta san sanda ta ce, "Allahu Akbar!" ba, "Allah da iko Yake, to ya aka yi da can ba mu sani ba?"