Sashe 10
Majanuni Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duka muka zuba mata ido da kallon mamaki a fuskokinmu, kawai sai ta zube kasan kafet tana kuka! tare da rungume yarinyar a jikinta!
Hajiya ta je ta kama yarinyar tana duddubata, sai ta kalleni bakinta na rawa, nima yarinyar kawai na zubawa ido ganin fuskarta irin tawa sak! sai dai bata da haske sosai! gabana ya dinga fad'uwa ina kiran sunan Allah a zuciyata cikin raina naji cewa wannan yarinyar 'yata ce domin kama take da Sadiya 'kanwata.
Hajiya ta ce"Fatima wannan kukan da ki ke bashi da wani amfani, kiyi mana bayanin matsayin wannan yarinyar."
Ta share hawaye murya a dashe ta ce" 'Yarsa ce" gabad'aya muka zuba mata ido.
Ta cigaba da cewa" Bayan naje likita yayi min allurar zubar da ciki, ashe tagwaye ne (twins) kuma d'aya ne ya fita. shima likitan be gane ba, saboda Allah ya 'boye al'amarinsa, sai bayan na je saudia domin fara gudanar da harkokina, kawai ciki ya bayyana, koda na je asibiti domin a zubar, likitan ya tabbatar min da cewa ba zai fita ba, domin kuwa ya riga ya girma, idan kuma na tsananta to zan iya rasa rayuwata, wannan dalilin yasa na hak'ura har na haifeta, amma na shiga damuwa sosai, saboda ina fargaba kada na kawo maka yarinyar kace ba kai ne ubanta ba, sai dai nayi farin ciki sosai da Allah yasa yarinyar tayi kama da kai, don Allah Hajiya ku yafe min."
Hajiya ta dinga kuka tana fadin" Fatima kinga ikon Allah ko? yanzu kin tabbatar da cewa, ba a yiwa Allah wayo tunda ya saukar da ishara a kanki, ya kamata kiyi hankali kuma"
Ta ce"Wallahi Hajiya nayi nadama sosai, na san kuma abinda na aikata ba dai-dai bane don Allah ki bashi hakuri ya mayar dani d'akina"
Na kalleta zuciyata cike da b'akin ciki abinda ta aikata Na ce"Har abada aure ya haramta a tsakaninmu, idan kin manta to bari na tuna miki, saki d'aya sau uku nayi miki, ba kuma a lokaci guda ba, ballanatana ki kawo min wani k'auli da ba'adi! saki uku ya halarta a kanki, ni dake har abada mun gama zaman aure, wannan yarinya kuma na 'karba Allah yayi mata albarka"
Sosai take kuka tana bani hakuri wai idan aka tambayi malamai za su iya gyara lamarin, kallon mahaukaciya kawai nake mata, ina ji Hajiya na tambayarta sunan yarinyar ta ce" Sunan mahaifiyarsa nasa mata wato Aisha, amma sai nake kiranta da Shukura"
Ta ce"Aikuwa kin kyauta da ki ka sanya mata sunan Aisha, Allah yasa ta gaji halinta.
Tashi nayi na basu guri domin zamana a gurin ina kallon fuskarta yana tuna min da munanan abubuwan da suka faru a baya.
Wannan shine mafarin dawowar Shukura hannuna, domin hana ta tafiya nayi da ita, Hajiya ta cigaba da rainonta, ita kuma tunda ta tabbatar da cewa ba zan mayar da ita ba, sai ta fara biye-biyen malamai, daga 'karshe dai ta je tayi auran kisan wuta wanda ko wata uku ba tayi ba ta fito, ta zo ta matsanta min cewa lallai sai na mayar da ita gidana, sai da nayi mata jan ido sosai! ta saurara min, na nuna mata cewa ko babu mata a duniya sai ita wallahi ba zan 'kara zaman aure da ita ba.
"Wannan shine tarihin rayuwata da Fatima matata ta farko, kuma Uwar Shukura, kasancewar asubah ta gabato zan tsaya miki a nan kafin na cigaba da baki labarin abinda ya wuce..
[1/12, 11:25 PM] Binta Umar Abbale: 78&79
Hannunsa ri'ke da fulas mai d'an girma ya shigo dakin, ido na tsira masa har ya 'karaso gurin da nake zaune, cikin taushin murya ya ce" Tashi ga abincin na samo miki gurin Hajiya." Shuru nayi ban ce komai ba, kuma bani da niyyar tashi.
Ya ajiye fulas din kan dirowa, ya hayo gadon yana k'okarin janyo ni, Na cire hannunsa da fad'in" Don Allah ka daina ta'ba ni."
A sakarce ya kalle ni, kafin ya girgiza kansa, yanayinsa ya nuna kamar ya fara gajiya da abinda nake masa, ni kuwa duk abinda nake yi, baya damuna, domin har yanzu ban yi na'am dashi a cikin zuciyata ba, amma kuma ina mamakin yanda yake min rawar jiki, kuma ina kallon tsagwaron sona a cikin 'kwayoyin idanuwansa.
Kansa ya sunkyar k'asa yayi shuru tare da tsirawa k'asa ido! wannan ya sake tabbatar min da cewa; ransa a 'bace yake da abubuwan da nake masa.
Jiki a sanyaye na sauko daga gadon, na shiga band'akin dake cikin dakin, na wanko hannuna na fito, na same shi a yanda yake, kusa da kafafunsa na zauna tare da janyo abincin na bud'e, abinci ne mai rai da lafiya, sai 'kamshi yake, lokaci 'kank'ani yunwar da nake ji ta dawo sabuwa, hannu nasa da bissimillah a bakina na fara cin abincin.
Tashi yayi ya fita, minti uku ya shigo da ruwa da lemo ya ajiye a gabana, kunya duk ta rufe ni ganin irin hidimar da yake min, ni kaina na san abinda nake masa bana kyautawa. a hankali na ce" Sannu" bai amsa ba, kawai ya nemi gefen gado ya zauna tare da kunna wayarsa yana dubawa.
Har na kammala cin abincin, hankalinsa yana kan wayarsa, na je na wanke hannuna, na zaune can 'karshen gado.
A nutse ya kalle ni tare da fad'in" Kin 'koshi?" shuru nayi ina kallonsa don ban ji abinda ya fad'a ba.
Murya ya bud'e kafin ya sake maimaita maganarsa. kai na d'aga masa alamar "Eh na ko'shi.
Ya ce" Kin shirya saurarata yanzu?"
Cikin jin nauyi na ce"Eh" sai ya ajiye wayar hannunsa a kusa dashi, wannan karon beyi yun'kurin rungume ni ba, sai dai ya mayar da hankalinsa kaina sosai kafin ya cigaba da bani labarin rayuwarsa.
"Zinaru, 'kanwar maigida na ce, ina nufin mutumin da nake aiki a 'kar'kashinsa, ni dai da bakina da nasa ban ta'ba fad'a masa cewar bani da aure ba, sai kawai ya same ni da wata magana wacce na kasa yin jayyaya dashi.
"Saddiku na yaba da hankali da nutsuwarka, wananan dalilin yasa nake neman wata alfarma a gurinka, ina fatan zan samu.
Na ce" Alhaji wace irin alfarma ce wannan?" domin ni a gani na mai nake dashi da har zai nemi alfarma a guri na.
Ya ce" 'Kanwata nake so ka aura" gabana ne ya fad'i! na kalle shi tare da fad'in" Alhaji ai ina da aure"
Murmushi yayi kafin ya ce" Allah ta'alah hud'u ya ce mu aura mutukar muna da iko! to ballanatana kuma na san da cewa; baka da aure, na samu labari a bakin abokinka Faruk, wannan dalilin yasa na nemi wannan alfarmar a gurinka.
Wato Faruk ne ya fad'a masa cewa; bani da aure, amma gaskiya ban ji dad'in abinda yayi min ba domin kwata-kwata babu maganar aure a tare dani, amma tunda al'amarin ya kasance haka, dole nayi hakuri, domin ba zan iya jayayya da wanda ya rufa min asiri ba.
Na ce" Alhaji Na gode da wannan kyauta da kayi min, tabbas hakane, bani da aure a yanzu, amma shekarun baya na auri 'yar uwata har da rabo a tsakaninmu."
Ya ce" Ma sha Allah. ai duk Faruk ya fad'a min komai. amma idan kana ganin da akwai matsala sai na janye.
Na ce" Haba Alhaji ai kafi 'karfin komai a guri na wallahi, zan auri 'kanwarka kamar yanda ka bu'kata"
Ya ce" Na gode sosai Saddiku da wannan rufin asirin da kayi min, sai dai kuma hanzari ba gudu ba"
Shuru yayi fuskarsa da alamun damuwa.
Na ce" Alhaji da akwai matsala kenan?"
Ya gyad'a kansa da fad'in" 'Kwarai kuwa Saddiku ba zan munafurce ka ba, yarinyar nan ta d'an yi yawo gaskiyar magana kenan, bana tsammanin za a samu budurci a tare da ita, bayan haka kuma tana da aljanu, wanda muke tunanin sune suke sanyata aikata munanan ayyuka"
Gabad'aya jikina ya mutu! cikin zuciyata nake tasbihi ga Ubangiji duba da irin kaddarar da take wanzuwa a tattare dani, ba zan ta'ba bijirewa umarnin Alhaji Harazimi ba, domin yayi min abinda ba zan manta ba.
Na ce" Alhaji kada ka damu. auran Zinaru a gare ni, kamar jahadi ne, mutukar tayi istibura'i zan aureta na kuma zauna da ita da zuciya d'aya, maganar aljanu kuma, ba su fi k'arfin Allah ba, insha Allahu zanyi iyakar bakin kokarina akan hakan.
Nan da nan, ya saki fuskarsa cikin jin dadin lafazi na, ya ce" Na gode sosai Saddiku Allah ya saka maka da alheri, hakika ka rufa min asiri a lokacin da nake bukatar hakan, a duniya bani da matsalar komai, sai ta Zinaru, 'kanwata ce, mu biyu iyayenmu suka haifa, asali mutumin Nijar ne, cikin zinder aka haife ni, neman kudi ya kawo ni Najeria, har nayi aure na tara iyali na, bayan rasuwar iyayenmu, Zinaru ta dawo hannuna, wallahi tunda ta zama cikakkiyar budurwa ta gagare ni, babu irin dukan da ban yi mata ba, amma k'arshe sai ta tattara kayanta ta gudu, sai tayi wata uku hud'u sannan zata dawo gida, wannan dalilin yasa na daina dukanta, sai na tsananta da addu'a tare da sanya matakan tsaro a gidana, amma duk da hakan, sai ta fita yawo, maza na d'aukarta a mota su tafi uwa duniya, wannan shine dalilin da yasa na yanke shawarar yi mata aure, ko Allah zai sanya ta shiryu.
Cikin damuwa na ce" Ranka ya dad'e ka kwantar da hankalinka, duk abinda yayi farko, yana da 'karshe! ni nayi maka al'kawarin ri'ke yarinyar nan amana, zanyi iyakar bakin 'kok'ari na insha Allahu.
Sosai ya dinga yi min godiya har sai da ya bani tausayi.
Wallahi Shahida idan kin ga Zinaru, sai ki dauka ita tayi kanta saboda tsananin kyau! domin ta ko'ina tayi, cikakkiyar mace kyakykyawa, tana da duk abinda namiji yake bukata, dama na fad'a miki asalinsu, 'yan nijar ne, buzaye ne gashinta har baya gata da kyau! sai dai rashin kyawun hali.
Amma kin san wani abu, wallahi kwata-kwata ni ba ta kwanta min a raina ba, kawai dai na aureta ne saboda d'an uwanta, dama can a tsari na bana son auran kyakykyawar mace, saboda wasu dalilai nawa.
Hajiya ta je ta kama yarinyar tana duddubata, sai ta kalleni bakinta na rawa, nima yarinyar kawai na zubawa ido ganin fuskarta irin tawa sak! sai dai bata da haske sosai! gabana ya dinga fad'uwa ina kiran sunan Allah a zuciyata cikin raina naji cewa wannan yarinyar 'yata ce domin kama take da Sadiya 'kanwata.
Hajiya ta ce"Fatima wannan kukan da ki ke bashi da wani amfani, kiyi mana bayanin matsayin wannan yarinyar."
Ta share hawaye murya a dashe ta ce" 'Yarsa ce" gabad'aya muka zuba mata ido.
Ta cigaba da cewa" Bayan naje likita yayi min allurar zubar da ciki, ashe tagwaye ne (twins) kuma d'aya ne ya fita. shima likitan be gane ba, saboda Allah ya 'boye al'amarinsa, sai bayan na je saudia domin fara gudanar da harkokina, kawai ciki ya bayyana, koda na je asibiti domin a zubar, likitan ya tabbatar min da cewa ba zai fita ba, domin kuwa ya riga ya girma, idan kuma na tsananta to zan iya rasa rayuwata, wannan dalilin yasa na hak'ura har na haifeta, amma na shiga damuwa sosai, saboda ina fargaba kada na kawo maka yarinyar kace ba kai ne ubanta ba, sai dai nayi farin ciki sosai da Allah yasa yarinyar tayi kama da kai, don Allah Hajiya ku yafe min."
Hajiya ta dinga kuka tana fadin" Fatima kinga ikon Allah ko? yanzu kin tabbatar da cewa, ba a yiwa Allah wayo tunda ya saukar da ishara a kanki, ya kamata kiyi hankali kuma"
Ta ce"Wallahi Hajiya nayi nadama sosai, na san kuma abinda na aikata ba dai-dai bane don Allah ki bashi hakuri ya mayar dani d'akina"
Na kalleta zuciyata cike da b'akin ciki abinda ta aikata Na ce"Har abada aure ya haramta a tsakaninmu, idan kin manta to bari na tuna miki, saki d'aya sau uku nayi miki, ba kuma a lokaci guda ba, ballanatana ki kawo min wani k'auli da ba'adi! saki uku ya halarta a kanki, ni dake har abada mun gama zaman aure, wannan yarinya kuma na 'karba Allah yayi mata albarka"
Sosai take kuka tana bani hakuri wai idan aka tambayi malamai za su iya gyara lamarin, kallon mahaukaciya kawai nake mata, ina ji Hajiya na tambayarta sunan yarinyar ta ce" Sunan mahaifiyarsa nasa mata wato Aisha, amma sai nake kiranta da Shukura"
Ta ce"Aikuwa kin kyauta da ki ka sanya mata sunan Aisha, Allah yasa ta gaji halinta.
Tashi nayi na basu guri domin zamana a gurin ina kallon fuskarta yana tuna min da munanan abubuwan da suka faru a baya.
Wannan shine mafarin dawowar Shukura hannuna, domin hana ta tafiya nayi da ita, Hajiya ta cigaba da rainonta, ita kuma tunda ta tabbatar da cewa ba zan mayar da ita ba, sai ta fara biye-biyen malamai, daga 'karshe dai ta je tayi auran kisan wuta wanda ko wata uku ba tayi ba ta fito, ta zo ta matsanta min cewa lallai sai na mayar da ita gidana, sai da nayi mata jan ido sosai! ta saurara min, na nuna mata cewa ko babu mata a duniya sai ita wallahi ba zan 'kara zaman aure da ita ba.
"Wannan shine tarihin rayuwata da Fatima matata ta farko, kuma Uwar Shukura, kasancewar asubah ta gabato zan tsaya miki a nan kafin na cigaba da baki labarin abinda ya wuce..
[1/12, 11:25 PM] Binta Umar Abbale: 78&79
Hannunsa ri'ke da fulas mai d'an girma ya shigo dakin, ido na tsira masa har ya 'karaso gurin da nake zaune, cikin taushin murya ya ce" Tashi ga abincin na samo miki gurin Hajiya." Shuru nayi ban ce komai ba, kuma bani da niyyar tashi.
Ya ajiye fulas din kan dirowa, ya hayo gadon yana k'okarin janyo ni, Na cire hannunsa da fad'in" Don Allah ka daina ta'ba ni."
A sakarce ya kalle ni, kafin ya girgiza kansa, yanayinsa ya nuna kamar ya fara gajiya da abinda nake masa, ni kuwa duk abinda nake yi, baya damuna, domin har yanzu ban yi na'am dashi a cikin zuciyata ba, amma kuma ina mamakin yanda yake min rawar jiki, kuma ina kallon tsagwaron sona a cikin 'kwayoyin idanuwansa.
Kansa ya sunkyar k'asa yayi shuru tare da tsirawa k'asa ido! wannan ya sake tabbatar min da cewa; ransa a 'bace yake da abubuwan da nake masa.
Jiki a sanyaye na sauko daga gadon, na shiga band'akin dake cikin dakin, na wanko hannuna na fito, na same shi a yanda yake, kusa da kafafunsa na zauna tare da janyo abincin na bud'e, abinci ne mai rai da lafiya, sai 'kamshi yake, lokaci 'kank'ani yunwar da nake ji ta dawo sabuwa, hannu nasa da bissimillah a bakina na fara cin abincin.
Tashi yayi ya fita, minti uku ya shigo da ruwa da lemo ya ajiye a gabana, kunya duk ta rufe ni ganin irin hidimar da yake min, ni kaina na san abinda nake masa bana kyautawa. a hankali na ce" Sannu" bai amsa ba, kawai ya nemi gefen gado ya zauna tare da kunna wayarsa yana dubawa.
Har na kammala cin abincin, hankalinsa yana kan wayarsa, na je na wanke hannuna, na zaune can 'karshen gado.
A nutse ya kalle ni tare da fad'in" Kin 'koshi?" shuru nayi ina kallonsa don ban ji abinda ya fad'a ba.
Murya ya bud'e kafin ya sake maimaita maganarsa. kai na d'aga masa alamar "Eh na ko'shi.
Ya ce" Kin shirya saurarata yanzu?"
Cikin jin nauyi na ce"Eh" sai ya ajiye wayar hannunsa a kusa dashi, wannan karon beyi yun'kurin rungume ni ba, sai dai ya mayar da hankalinsa kaina sosai kafin ya cigaba da bani labarin rayuwarsa.
"Zinaru, 'kanwar maigida na ce, ina nufin mutumin da nake aiki a 'kar'kashinsa, ni dai da bakina da nasa ban ta'ba fad'a masa cewar bani da aure ba, sai kawai ya same ni da wata magana wacce na kasa yin jayyaya dashi.
"Saddiku na yaba da hankali da nutsuwarka, wananan dalilin yasa nake neman wata alfarma a gurinka, ina fatan zan samu.
Na ce" Alhaji wace irin alfarma ce wannan?" domin ni a gani na mai nake dashi da har zai nemi alfarma a guri na.
Ya ce" 'Kanwata nake so ka aura" gabana ne ya fad'i! na kalle shi tare da fad'in" Alhaji ai ina da aure"
Murmushi yayi kafin ya ce" Allah ta'alah hud'u ya ce mu aura mutukar muna da iko! to ballanatana kuma na san da cewa; baka da aure, na samu labari a bakin abokinka Faruk, wannan dalilin yasa na nemi wannan alfarmar a gurinka.
Wato Faruk ne ya fad'a masa cewa; bani da aure, amma gaskiya ban ji dad'in abinda yayi min ba domin kwata-kwata babu maganar aure a tare dani, amma tunda al'amarin ya kasance haka, dole nayi hakuri, domin ba zan iya jayayya da wanda ya rufa min asiri ba.
Na ce" Alhaji Na gode da wannan kyauta da kayi min, tabbas hakane, bani da aure a yanzu, amma shekarun baya na auri 'yar uwata har da rabo a tsakaninmu."
Ya ce" Ma sha Allah. ai duk Faruk ya fad'a min komai. amma idan kana ganin da akwai matsala sai na janye.
Na ce" Haba Alhaji ai kafi 'karfin komai a guri na wallahi, zan auri 'kanwarka kamar yanda ka bu'kata"
Ya ce" Na gode sosai Saddiku da wannan rufin asirin da kayi min, sai dai kuma hanzari ba gudu ba"
Shuru yayi fuskarsa da alamun damuwa.
Na ce" Alhaji da akwai matsala kenan?"
Ya gyad'a kansa da fad'in" 'Kwarai kuwa Saddiku ba zan munafurce ka ba, yarinyar nan ta d'an yi yawo gaskiyar magana kenan, bana tsammanin za a samu budurci a tare da ita, bayan haka kuma tana da aljanu, wanda muke tunanin sune suke sanyata aikata munanan ayyuka"
Gabad'aya jikina ya mutu! cikin zuciyata nake tasbihi ga Ubangiji duba da irin kaddarar da take wanzuwa a tattare dani, ba zan ta'ba bijirewa umarnin Alhaji Harazimi ba, domin yayi min abinda ba zan manta ba.
Na ce" Alhaji kada ka damu. auran Zinaru a gare ni, kamar jahadi ne, mutukar tayi istibura'i zan aureta na kuma zauna da ita da zuciya d'aya, maganar aljanu kuma, ba su fi k'arfin Allah ba, insha Allahu zanyi iyakar bakin kokarina akan hakan.
Nan da nan, ya saki fuskarsa cikin jin dadin lafazi na, ya ce" Na gode sosai Saddiku Allah ya saka maka da alheri, hakika ka rufa min asiri a lokacin da nake bukatar hakan, a duniya bani da matsalar komai, sai ta Zinaru, 'kanwata ce, mu biyu iyayenmu suka haifa, asali mutumin Nijar ne, cikin zinder aka haife ni, neman kudi ya kawo ni Najeria, har nayi aure na tara iyali na, bayan rasuwar iyayenmu, Zinaru ta dawo hannuna, wallahi tunda ta zama cikakkiyar budurwa ta gagare ni, babu irin dukan da ban yi mata ba, amma k'arshe sai ta tattara kayanta ta gudu, sai tayi wata uku hud'u sannan zata dawo gida, wannan dalilin yasa na daina dukanta, sai na tsananta da addu'a tare da sanya matakan tsaro a gidana, amma duk da hakan, sai ta fita yawo, maza na d'aukarta a mota su tafi uwa duniya, wannan shine dalilin da yasa na yanke shawarar yi mata aure, ko Allah zai sanya ta shiryu.
Cikin damuwa na ce" Ranka ya dad'e ka kwantar da hankalinka, duk abinda yayi farko, yana da 'karshe! ni nayi maka al'kawarin ri'ke yarinyar nan amana, zanyi iyakar bakin 'kok'ari na insha Allahu.
Sosai ya dinga yi min godiya har sai da ya bani tausayi.
Wallahi Shahida idan kin ga Zinaru, sai ki dauka ita tayi kanta saboda tsananin kyau! domin ta ko'ina tayi, cikakkiyar mace kyakykyawa, tana da duk abinda namiji yake bukata, dama na fad'a miki asalinsu, 'yan nijar ne, buzaye ne gashinta har baya gata da kyau! sai dai rashin kyawun hali.
Amma kin san wani abu, wallahi kwata-kwata ni ba ta kwanta min a raina ba, kawai dai na aureta ne saboda d'an uwanta, dama can a tsari na bana son auran kyakykyawar mace, saboda wasu dalilai nawa.