Sashe 9
Majanuni Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wannan karon ba'kin cikin da Mariya ta had'iya yafi wanda ta had'iya a lokacin da ya auri Hafsatu, Talatu fitinanniya ce ta ajin karshe gabad'aya ta kanainaiye shi ta hanashi gane fari da baki ita kadai yake gani a gabansa, iskanci iri - iri suke a gidan, Sai ya kasance Mariya ta zama 'yar kallo domin tunda Talatu ta shigo gidan shikkenan ta kar'be girki da mijin gabadaya tsayin wata shida itake juya gidan sai abinda take so za'ayi.
Sai dai abinda Talatu bata sani ba shine duk ranar da ta tafi Unguwa shi kuma a lokacin yake samun damar shiga dakin Mariya yayi abinda yake bukata domin duk gigin da yake akanta ba wani cikakkiyar gamsuwa yake samu da ita ba, Yafi samun gamsuwar da yake bukata da Mariya.
Cikin ikon Allah ciki ya samu kuma bai bayyana kanshi ba sai da yayi wata biyar, ita Mariyar ta san da zaman cikin a jikinta. kawai tayi masa shuru ne saboda tana gudun ta fada masa ya zubar dashi tunda tana ganin irin k'wayoyin da yake dubgawa matayensa.
Aikuwa bala'i ne ya tashi a lokacin da Talatu ta farga da cikin tana kuka tana fadin." Ashe dama yaudararta yake yana kusantar Mariya gashinan har yayi mata ciki amma ita saboda mugunta duk sanda ta samu ciki sai ya bata magani cikin ya zube to dan haka wallahi ba zata yarda ba sai an zubar da cikin Mariya.
Budar bakinsa sai yace."Ta kwantar da hankalinta shi wannan ciki ba nasa bane domin shi rabon da ya hada shimfida da Mariya har ya manta.
Mariya tana share hawaye ta fito daga dakinta tana kallonsu a tsaye a tsakar gidan sai rarrashinta yake, Tace."Jamilu kaji tsoron Allah kaji tsoron ranar haduwar ka dashi, kai ka san wannan cikin na jikina kai ne ubansa amma ka ke shegenta shi.
Ya nuna ta da yatsa da fadin." Rufe min baki munafurka Allah ta'ala har yaushe na kwanta dake da zanyi miki ciki ban yarda ba tun wuri kije ki nemi uban danki."
Wani irin hawaye masu tsananin zafi suka shiga zuba a saman fuskata, ta dinga kokarin magana amma tsabar bacin rai ya hanata furta komai, a daddafe ta shiga dakinta, tasa hijabi ta fito.
Ya kalleta ya watsar da fadin." Duk in da zaki tafi kije domin kuwa ba zan yarda da wannan cikin ba.
Talatu zuciyarta tayi wasai dama babban burinta Mariya ta fita ta bar mata gidan ita kad'ai.
Tsakanin Baba Asabe da Hujaj! rigima aka tafka ba kad'an ba! domin kuwa Baba Asabe cewa ita ba zata yarda da wannan 'kazafin ba sai ta maka! shi a kotu a maimako ya risina ya bata hakuri domin su samu daidaito a tsakaninsu, sai ya k'ara fusata yace idan kotun k'oli zata kai k'ararsa taje ta kai babu abunda ya dame shi.
Baba Asabe kai tsaye kotun musulunci ta nufa ta d'auki lauya ya tsaya mata suka fara bugawa, da yake ita gaskiya duk inda take sai ta nuna kanta a take asirin Hujaj! ya tonu domin kuwa duk wanda zai bud'i baki a gurin ba zai fadi alkairinsa ba sai sharrinsa.
Alk'ali ya tabbatar da shedu daga bakunan jama'a a take ya yanke hukunci kan cewa dole Hujaj! ya amince da wannan ciki domin addinin musulunci ne ya amince da hakan, koda bashi yayi cikin ba tunda har ya kasance a gidanshi a ka sameshi dole ya dauki d'an da za'a haifa a matsayin d'ansa, bayan haka kuma dole ya cigaba da kula da matarsa da cikin da take dauke dashi, Ci da sha da kula da lafiyarsu duk yana rataye a wuyansa.
Mai sharia ya gama yanke hukunci ya buga katako alamun hukuncin ya tabbata, ya mi'ke. kotu ta tashi kowa na fadin albarkacin bakinsa.
Bayan kwana uku ya samu takarda da biro ba tare da tunani da tsinkaye ba ya rubuta saki har uku da kansa yaje ya har gidan ya bada takadar ya futo abunsa.
Baba Asabe ba ta iya karatun hausa ba, ita Mariyar ita ta karanta takardar a take a lokacin ta fadi a gurin, hankalin Baba Asabe ya tashi a wahalce aka kaita asibiti taimakon gaggawa akayi a kanta domin kuwa jininta ya kai k'ololowa gurin hawa.
Haka Baba Asabe ta dinga kai kawo ita kad'ai dan ma dai tana da kudi a ajiye shiyasa ta samu saukin wasu al'amuran.
A takaice sai da Mariya tayi sati uku a kwance a asibiti ta samu sauki likita ya dora ta akan magani tare da sharad'ai masu tsauri domin kuwa. hawan jini ga mace mai ciki babban matsala ne.
Baba Asabe ta sake yun'kurin shigar da kara kotu domin tun sanda alkali ya yanke hukunci Hujaj! bai ta'ba zuwa ya kawo naira biyar a cikin abunda alkali ya yanke masa ba.
Kawu Musa d'anta shine ya hanata yace ta bar maganar kawai su barshi da Allah domun duk yanda take tunanin Hujaj! ya wuce haka shaid'anin mutum ne, Sharia dashi bata da amfani.
Baba Asabe ta hakura ta bar maganar suka kyaleshi da mugun halinsa, Bangaran Mariya kuwa sai addua domin ita kadai ta san irin kuncin da take ciki bata ta'ba tsammanin Jamilu zai tozartata irin hakaba.
Allah al-musauwiru wanda bashi da tamka, ya fara saukar da ishara akan Hujaj! kasuwancinsa ya tsaya duk abinda ya ta'ba sai ya lalace ta kai ta kawo idan ya fita kasuwa haka zai wuni babu wanda zai zo gurinsa da niyyar sayan kayansa, Idan zai tafi gida sai ya ci bashi domin kuwa idan yaje gida babu kudi a jikinsa zasu kwana suna tafka rigima da Talatu.
Wani abokinsa ya jashi gurin wani malami domin yayi masa duba acikin al'amuransa yaga abunda yake kai kawo.
Kai tsaye malamin yace."Matarsa da ya rabu da ita itace mahad'in arzikinsa saboda haka idan yana so arzikinsa ya dawo tilas yaje ya dawo da ita gidansa.
Jin wannan magana sai hankalinsa ya tashi ya dinga share zufa yana tunanin yanda za'ayi ya cigaba da zaman aure da Mariya bayan yayi mata saki uku.
A hanyarsu ta dawowa gida Alhaji Shu'aibu ya kalleshi da fadin." Ya hujaj! naga duk ka tashi hankalinka wannan al'amarin fa duk mai sauki ne."
Ya kalleshi cikin damuwa yace."Alhaji Sha'aibu ya kake kiran wannan al'amari me sauki saki uku fa nayi mata ta yaya zan aureta dole sai ta auri wani sannan zata hallata a gareni."
Alhaji Sha'aibu yayi murmushi da fadin." Yanzu dai mu bari ta haihu akwai shawarar da zan baka."
Yace." Alhaji zama cikin kuncin talaucin nan ya isheni wallahi."
Yace."To ya za kayi kaine kayi ganganci ai irin wannan ba'a yanke hukunci kai tsaye sai mahukunta sun duba maka abunda ya dace da rayuwarka gashinan ka saketa ba tare da ka san itace abokiyar arzikinka ba."
Hujaj! ya girgiza kai da fadin." Wallahi sharrin zuciya ne amma nan gaba dole na kiyaye a yanzu dai burina ta dawo hannuna ko arzikina ya dawo."
Yace."Ka kwantar da hankalinka komai zai zo da sauki insha Allah.
*****
Alhaji Sha'aibu shi ya cigaba da kwantar masa da hankali, amma duk da haka kullum cikin lissafin wattanin cikin yake sai da ta haihu sannan hankalinsa ya kwanta.
Alhaji Sha'aibu shi ya bashi bashin kudi wanda yayi wa 'yar da aka haifa siyayya, sannan kuma shine ya jagorance shi zuwan gidan, kunyar duniya ta isheshi sai sunkuyar da kai yake, Alhaji Sha'aibun ne mai k'ok'arin magana
Baba ta kalleshi da fadin." Da dai banyi niyyar yi maka magana ba amma ta kama dole sai nayi inaso ka bude idonka sosai ka kalli wannan 'yar dake hannunka."
Yayi ta maza ya daga kai ya kalleta da fadin." Ai tunda na kalli yarinyar nan na tabbatar da cewa ni ne ubanta saboda haka don Allah Baba ayi hakuri kada ayi tone-tone duk abubuwan da suka faru a baya tsautsayi ne amma na san ban kyauta ba.
Ta girgiza kai da fadin." To naji maganarka wane suna kake ganin za'a sanyawa yarinyar ."? Da murmushi a fuskarsa yace."Sunan mahaifiyata nake da niyyar sanya mata Maryama kenan."
Tace."Shikkenan Allah ya raya ta yasa cikon addinin musulunci ce." gabadaya suka amsa da ameeen ya Allah."
Da zasu tafi ya ajiye mata dubu biyar da fadin duk hidimar da ta tashi tayi da kudin kafin ranar suna."
Ba tace komai ba har suka fita daga gidan, Ta girgiza kai da fadin." Kullum yana fama da malin-malin(babbar riga) sai kace limami amma shaid'ancisa yafi karfinsa.
Itama Mariya dake uwar dakin maganar da take kenan, idan yana magana kamar mutumin kirki amma mugun halinsa yafi dubu! gabad'aya yanzu bata kaunar ta bude ido ta ganshi ta tsaneshi don dai kawai kaddarar aure ta ratsa a tsakaninta dashi babu yanda za tayi tunda ya kasance uban 'yarta dole tayi hakuri ta manta da abubuwan da suka faru a baya.
Ashe rigima ce take jiransa a can gidansa.
Ya shiga gidan cikin nishadi da walwala domin kuwa gani yake kamar Mariya ta dawo gidansa ta gama tunda Alhaji Sha'aibu ya fada masa shawarar da ya yanke kan cewa shi din ya amince zai yi *(Auran kisan wuta)* da ita zai saketa idan tayi wata daya ko biyu a gidansa, To tunda ya fada masa wannan magana yake farin ciki tabbas ya san Alhaji Sha'aibu ba zai cutar dashi ba.
A tsaye ya sameta a tsakiyar tsakar gidan sai kace wacce aka dasa! tsoro ta bashi da sauri ya kira sunan Allah kafin ya fuskanci itace yaja mummunan tsaki da fadin." Talatu ke wace irin jahila ce zaki tsaya tsakiyar tsakar gida sai kace aljana ko wani siddabarun kike min a gida."?
Ta fusata! dama a wuya take ta hayayya'ko! masa tana kumfar baki tace." Rufe min baki algungumi! munafiki duk halin da kake ciki na sani tsohuwar matarka daka saki ta haihu har kana siyayya kana kai wa jaririyar data haifa bayan da bakinka ka furta cewa ba kaine ubanta ba."
Ya daga mata hannu da fadin." Kinga saurara min! idan kuma kin 'kiya zanyi maganinki ni ba shashashan namiji bane da zaki titsiye da maganganun banza ni ne nan Uban yarinyar da Mariya ta haifa kuma a yau nayi mata hud'uba da sunan mahaifiyata Maryama saboda haka ki hadiyi zuciya ki mutu."
Sai dai abinda Talatu bata sani ba shine duk ranar da ta tafi Unguwa shi kuma a lokacin yake samun damar shiga dakin Mariya yayi abinda yake bukata domin duk gigin da yake akanta ba wani cikakkiyar gamsuwa yake samu da ita ba, Yafi samun gamsuwar da yake bukata da Mariya.
Cikin ikon Allah ciki ya samu kuma bai bayyana kanshi ba sai da yayi wata biyar, ita Mariyar ta san da zaman cikin a jikinta. kawai tayi masa shuru ne saboda tana gudun ta fada masa ya zubar dashi tunda tana ganin irin k'wayoyin da yake dubgawa matayensa.
Aikuwa bala'i ne ya tashi a lokacin da Talatu ta farga da cikin tana kuka tana fadin." Ashe dama yaudararta yake yana kusantar Mariya gashinan har yayi mata ciki amma ita saboda mugunta duk sanda ta samu ciki sai ya bata magani cikin ya zube to dan haka wallahi ba zata yarda ba sai an zubar da cikin Mariya.
Budar bakinsa sai yace."Ta kwantar da hankalinta shi wannan ciki ba nasa bane domin shi rabon da ya hada shimfida da Mariya har ya manta.
Mariya tana share hawaye ta fito daga dakinta tana kallonsu a tsaye a tsakar gidan sai rarrashinta yake, Tace."Jamilu kaji tsoron Allah kaji tsoron ranar haduwar ka dashi, kai ka san wannan cikin na jikina kai ne ubansa amma ka ke shegenta shi.
Ya nuna ta da yatsa da fadin." Rufe min baki munafurka Allah ta'ala har yaushe na kwanta dake da zanyi miki ciki ban yarda ba tun wuri kije ki nemi uban danki."
Wani irin hawaye masu tsananin zafi suka shiga zuba a saman fuskata, ta dinga kokarin magana amma tsabar bacin rai ya hanata furta komai, a daddafe ta shiga dakinta, tasa hijabi ta fito.
Ya kalleta ya watsar da fadin." Duk in da zaki tafi kije domin kuwa ba zan yarda da wannan cikin ba.
Talatu zuciyarta tayi wasai dama babban burinta Mariya ta fita ta bar mata gidan ita kad'ai.
Tsakanin Baba Asabe da Hujaj! rigima aka tafka ba kad'an ba! domin kuwa Baba Asabe cewa ita ba zata yarda da wannan 'kazafin ba sai ta maka! shi a kotu a maimako ya risina ya bata hakuri domin su samu daidaito a tsakaninsu, sai ya k'ara fusata yace idan kotun k'oli zata kai k'ararsa taje ta kai babu abunda ya dame shi.
Baba Asabe kai tsaye kotun musulunci ta nufa ta d'auki lauya ya tsaya mata suka fara bugawa, da yake ita gaskiya duk inda take sai ta nuna kanta a take asirin Hujaj! ya tonu domin kuwa duk wanda zai bud'i baki a gurin ba zai fadi alkairinsa ba sai sharrinsa.
Alk'ali ya tabbatar da shedu daga bakunan jama'a a take ya yanke hukunci kan cewa dole Hujaj! ya amince da wannan ciki domin addinin musulunci ne ya amince da hakan, koda bashi yayi cikin ba tunda har ya kasance a gidanshi a ka sameshi dole ya dauki d'an da za'a haifa a matsayin d'ansa, bayan haka kuma dole ya cigaba da kula da matarsa da cikin da take dauke dashi, Ci da sha da kula da lafiyarsu duk yana rataye a wuyansa.
Mai sharia ya gama yanke hukunci ya buga katako alamun hukuncin ya tabbata, ya mi'ke. kotu ta tashi kowa na fadin albarkacin bakinsa.
Bayan kwana uku ya samu takarda da biro ba tare da tunani da tsinkaye ba ya rubuta saki har uku da kansa yaje ya har gidan ya bada takadar ya futo abunsa.
Baba Asabe ba ta iya karatun hausa ba, ita Mariyar ita ta karanta takardar a take a lokacin ta fadi a gurin, hankalin Baba Asabe ya tashi a wahalce aka kaita asibiti taimakon gaggawa akayi a kanta domin kuwa jininta ya kai k'ololowa gurin hawa.
Haka Baba Asabe ta dinga kai kawo ita kad'ai dan ma dai tana da kudi a ajiye shiyasa ta samu saukin wasu al'amuran.
A takaice sai da Mariya tayi sati uku a kwance a asibiti ta samu sauki likita ya dora ta akan magani tare da sharad'ai masu tsauri domin kuwa. hawan jini ga mace mai ciki babban matsala ne.
Baba Asabe ta sake yun'kurin shigar da kara kotu domin tun sanda alkali ya yanke hukunci Hujaj! bai ta'ba zuwa ya kawo naira biyar a cikin abunda alkali ya yanke masa ba.
Kawu Musa d'anta shine ya hanata yace ta bar maganar kawai su barshi da Allah domun duk yanda take tunanin Hujaj! ya wuce haka shaid'anin mutum ne, Sharia dashi bata da amfani.
Baba Asabe ta hakura ta bar maganar suka kyaleshi da mugun halinsa, Bangaran Mariya kuwa sai addua domin ita kadai ta san irin kuncin da take ciki bata ta'ba tsammanin Jamilu zai tozartata irin hakaba.
Allah al-musauwiru wanda bashi da tamka, ya fara saukar da ishara akan Hujaj! kasuwancinsa ya tsaya duk abinda ya ta'ba sai ya lalace ta kai ta kawo idan ya fita kasuwa haka zai wuni babu wanda zai zo gurinsa da niyyar sayan kayansa, Idan zai tafi gida sai ya ci bashi domin kuwa idan yaje gida babu kudi a jikinsa zasu kwana suna tafka rigima da Talatu.
Wani abokinsa ya jashi gurin wani malami domin yayi masa duba acikin al'amuransa yaga abunda yake kai kawo.
Kai tsaye malamin yace."Matarsa da ya rabu da ita itace mahad'in arzikinsa saboda haka idan yana so arzikinsa ya dawo tilas yaje ya dawo da ita gidansa.
Jin wannan magana sai hankalinsa ya tashi ya dinga share zufa yana tunanin yanda za'ayi ya cigaba da zaman aure da Mariya bayan yayi mata saki uku.
A hanyarsu ta dawowa gida Alhaji Shu'aibu ya kalleshi da fadin." Ya hujaj! naga duk ka tashi hankalinka wannan al'amarin fa duk mai sauki ne."
Ya kalleshi cikin damuwa yace."Alhaji Sha'aibu ya kake kiran wannan al'amari me sauki saki uku fa nayi mata ta yaya zan aureta dole sai ta auri wani sannan zata hallata a gareni."
Alhaji Sha'aibu yayi murmushi da fadin." Yanzu dai mu bari ta haihu akwai shawarar da zan baka."
Yace." Alhaji zama cikin kuncin talaucin nan ya isheni wallahi."
Yace."To ya za kayi kaine kayi ganganci ai irin wannan ba'a yanke hukunci kai tsaye sai mahukunta sun duba maka abunda ya dace da rayuwarka gashinan ka saketa ba tare da ka san itace abokiyar arzikinka ba."
Hujaj! ya girgiza kai da fadin." Wallahi sharrin zuciya ne amma nan gaba dole na kiyaye a yanzu dai burina ta dawo hannuna ko arzikina ya dawo."
Yace."Ka kwantar da hankalinka komai zai zo da sauki insha Allah.
*****
Alhaji Sha'aibu shi ya cigaba da kwantar masa da hankali, amma duk da haka kullum cikin lissafin wattanin cikin yake sai da ta haihu sannan hankalinsa ya kwanta.
Alhaji Sha'aibu shi ya bashi bashin kudi wanda yayi wa 'yar da aka haifa siyayya, sannan kuma shine ya jagorance shi zuwan gidan, kunyar duniya ta isheshi sai sunkuyar da kai yake, Alhaji Sha'aibun ne mai k'ok'arin magana
Baba ta kalleshi da fadin." Da dai banyi niyyar yi maka magana ba amma ta kama dole sai nayi inaso ka bude idonka sosai ka kalli wannan 'yar dake hannunka."
Yayi ta maza ya daga kai ya kalleta da fadin." Ai tunda na kalli yarinyar nan na tabbatar da cewa ni ne ubanta saboda haka don Allah Baba ayi hakuri kada ayi tone-tone duk abubuwan da suka faru a baya tsautsayi ne amma na san ban kyauta ba.
Ta girgiza kai da fadin." To naji maganarka wane suna kake ganin za'a sanyawa yarinyar ."? Da murmushi a fuskarsa yace."Sunan mahaifiyata nake da niyyar sanya mata Maryama kenan."
Tace."Shikkenan Allah ya raya ta yasa cikon addinin musulunci ce." gabadaya suka amsa da ameeen ya Allah."
Da zasu tafi ya ajiye mata dubu biyar da fadin duk hidimar da ta tashi tayi da kudin kafin ranar suna."
Ba tace komai ba har suka fita daga gidan, Ta girgiza kai da fadin." Kullum yana fama da malin-malin(babbar riga) sai kace limami amma shaid'ancisa yafi karfinsa.
Itama Mariya dake uwar dakin maganar da take kenan, idan yana magana kamar mutumin kirki amma mugun halinsa yafi dubu! gabad'aya yanzu bata kaunar ta bude ido ta ganshi ta tsaneshi don dai kawai kaddarar aure ta ratsa a tsakaninta dashi babu yanda za tayi tunda ya kasance uban 'yarta dole tayi hakuri ta manta da abubuwan da suka faru a baya.
Ashe rigima ce take jiransa a can gidansa.
Ya shiga gidan cikin nishadi da walwala domin kuwa gani yake kamar Mariya ta dawo gidansa ta gama tunda Alhaji Sha'aibu ya fada masa shawarar da ya yanke kan cewa shi din ya amince zai yi *(Auran kisan wuta)* da ita zai saketa idan tayi wata daya ko biyu a gidansa, To tunda ya fada masa wannan magana yake farin ciki tabbas ya san Alhaji Sha'aibu ba zai cutar dashi ba.
A tsaye ya sameta a tsakiyar tsakar gidan sai kace wacce aka dasa! tsoro ta bashi da sauri ya kira sunan Allah kafin ya fuskanci itace yaja mummunan tsaki da fadin." Talatu ke wace irin jahila ce zaki tsaya tsakiyar tsakar gida sai kace aljana ko wani siddabarun kike min a gida."?
Ta fusata! dama a wuya take ta hayayya'ko! masa tana kumfar baki tace." Rufe min baki algungumi! munafiki duk halin da kake ciki na sani tsohuwar matarka daka saki ta haihu har kana siyayya kana kai wa jaririyar data haifa bayan da bakinka ka furta cewa ba kaine ubanta ba."
Ya daga mata hannu da fadin." Kinga saurara min! idan kuma kin 'kiya zanyi maganinki ni ba shashashan namiji bane da zaki titsiye da maganganun banza ni ne nan Uban yarinyar da Mariya ta haifa kuma a yau nayi mata hud'uba da sunan mahaifiyata Maryama saboda haka ki hadiyi zuciya ki mutu."