Sashe 5
Majanuni Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yace."Shahida Irin wad'annan mutanan da kike gani basu da gaskiya shiyasa Allah yake mayar dasu haka watakila akwai wani mugun abun da ya tafka wanda yasa Allah ya nuna masa kuskuransa saboda haka idan za ki yi tausayi da imani ki tausayawa 'kananun yara ko kuma marayu ko nakasassu irinki amma ba irin wad'annan mutanan ba."
Direba yace."Gaskiya ne Alhaji nima na jima ina mamakin mutumin nan da yake ina yawan shigowa unguwar nan ina ganinsa sai nayi ta mamakin yanda akayi rayuwarsa ta lalace haka koda yake duk mutumin da bashi da gaskiya yakan 'kare rayuwarsa a firgice ba tare da ya san ina ya dosa ba."
Hawaye ta share tana jin zafin magangansu tace."Abbah ku dai kuyi masa Addua dashi da masu lalura irin tashi watakila kuma babu d'aya daga cikin abunda kuke zargi mybe jarabtace daga Ubangiji."
Murmushi yayi ya dauko tafkekiyar wayarsa yana dubawa yace." Shahida irin halinku daya da mahaifiyarki Allah ya gafarta mata."
Ta amsa da ameen tana goge fuskarta.
Suna zaune a tsakar gida ita da Saliha suna gyaran kayan miya suka shiga gidan.
Koda ta amsa sallamarsu sai kawai ta mayar da kanta kasa ta cigaba da abinda takeyi tai bala'in shan kunu!
Da yake ya iya Siyasa sai ya cire takalmansa cikin ladabi da 'yar dariya a tare dashi yace."Baba sannu da aiki."
Ciki-ciki ta amsa ita kuwa Saliha ko kallonsa ba tayi ba ballanatanta ta gaisheshi hakan ya 'bata mata rai sosai sai itama ta kudiri aniya a zuciyarta kan cewa duk sanda babanta yazo gidan ta daina gaishe shi.
Da fara'a a tare dashi yace."Ai dawowata kenan na samu yarinyar nan a gidan shine take sheda min abunda ya faru har kika kore ta daga gidanki haba Baba ai hannunka baya ru'bewa ka yanke ka yar."
Hannu ta d'aga masa da fadin." Dakata! Jamilu kazo ne kayi min dadin baki ko kuma kud'ina kazo ka biya ni bana son neman gidin zama ko kuma dama can hakkin rike yarinyar nan a hannuna yake?"
Maganar ta 'bata masa rai amma sai ya basar yace."Haba Baba ki kwantar da hankalinki muyi magana ta fahinta mana ake rasa mutum ma ballanatana kudi."
Tsaki! taja tana cizge alayyahun dake gabanta ta ce." Mutuwa dole ce amma da gangan yarinyar nan tayi min wasarere! da kudi har 'barawo ya sace saboda haka ka tashi ka bani guri bana bukatar tsari da dadin baki mutukar ba biya na kudi za kayi ba."
Ya girgiza kai har ila yau da murmushi a fuskarsa yace."Wai shin ma nawa ne kudin naki.?"
Ta kalleshi she'ke'ke! kafin tace."Kaji fa! kamar gaske har wani tambaya kake kamar wanda zai iya biya."
Dariya yasa baka ta'ba ganin 'bacin ransa saboda ya iya siyasa yace."Ko ba zan iya biya ba ai yana da kyau na sani."
Ta'be baki tayi da fadin." Babu amfanin na fad'a maka tunda ba iya biya za kayi ba."
Ya gyad'a kanshi yana kallonta minti biyu ya giciye yana gyara babbar rigarsa ta zuba masa ido tana kallonsa ya zaro yan dubu-dubu sabbi kar dasu har wasu na zubewa a kasan gurin.
Cike da mamaki take kallonsa yana irgawa cas ya cake mata dubu hamsin a gabanta ya gyara zaman babbar rigarsa da fadin." Gashinan duk da na san ban isa na biya kudin hidimar da akayi min ba ayi hakuri da ni da hali na na san anyi min kokari."
Kunya ce ta rufe ta sai ta sunkuyar da kanta ba tare da tace komai ba har ya gama maganarsa ya fita daga gidan.
Ganin haka yasa Shahida shiga daki ta kwanta kan gado abu biyu suka dame ta irin rayuwar k'as'kancin da take a tsakanin 'bangare biyu da kuma al'amarin *Baban- baba* daya tsaya mata a cikin rai.
Hawaye masu zafi suka dinga karakaina a saman fuskarta hakika maraici bala'i ne tabbas da uwarta tana raye a duniya ta san ba za tayi irin wannan rayuwar ba, Baba Asabe itace ta haifi mamanta itace kuma ta haifi Kawu Musa mahaifin Saliha kenan amma ba tasan me yasa take fifita Saliha a kanta ba, Gashi dai duk ita ta haifi iyayensu amma tafi son Saliha a kanta duk abinda Saliha za tayi daidai ne a gurinta amma ita abu kad'an idan tayi sai ya zama laifi.
Ta shigo dakin ta sameta tana kuka, sai jikinta ya kara sanyi murya ta d'aga da karfi ta ce."Kukan me kuma kike bayan ubanki yazo ya fanshe ki ashe dama yana da kudi mugunta ce take sa baya zuwa ya bani wani abu duba da irin dawainiyar da nake dake ko tausayin tsufa na ba ya ji."
Ta mi'ke zaune cikin 'bacin rai da masifa irin ta kurame! tace."Wai shin Baba ni d'in bare ce a gurinki? ko kuwa bake kika haifi uwata ba?"
Ta rike baki tana kallonta da fadin." Ni kike wa tsawa yau kuma tambotsan naki a kaina zaki sauke shi?"
Tace"Ni tambayarki nake ina so ki bani amsa?
Tace."Ni ce na haifi Uwarki na kuma Haifi Musa su biyu kacal Allah ya ba ni sai me kike so kiji.?
Tace."To me yasa kike 'bakin ciki don kin kula dani kin ciyar dani kin tufarta dani don kinyi min d'awainiya shine kike gorantawa ubana ai sai yana dashi zai zo ya baki."
Cike da dumbun mamaki tace."Shahida yau ubanki kike fifitawa a kaina.?
Tace."Kada kiyi min mummunar fahinta Baba ina so na nuna miki Kuskuran da kike aikatawa kada ki d'auka bana fahimtar komai duk abinda kike ina lure dake kin fi k'aunar Saliha a kaina meye dalili? ko don ita ubanta yana baki kudi ni kuwa uwata ta mutu bata raye babu abunda take tsinana miki shine kike gallaza min saboda kawai tsautsayi ya ratsa an sace kud'inki shine har zaki tattara min kayana ki watsa waje wai kin kore ni Haba Baba ke baki ji kunya ba."
Baba Asabe bakinta ya mutu kallonta kawai take ta cigaba da cewa." Tunda kika dasa sayar da man gyada a gidan nan ni nake zuwa na saro miki kuma bant'ba zubar miki da kudi ba sai wannan karon amma saboda rashin tawakkali kika fita duniya kina zage-zage kowa yana kallonki ai wannan abun kunya ne."
Baba Asabe ta fashe da kuka tasa gefen zaninta ta fyace hanci ta ce."Lallai Shahida wuyanki ya isa yanka ni kikewa rashin kunya ko kuma dai Jamilu da Talatu sunyi miki hud'uba akaina."
Tace."Ni ina ruwana da Talatu itama ai ba k'aunata take ba kuma Abbanmu ba zai zuga ni nayi miki rashin kunya ba."
Ta goge fuska da fadin." To babu laifi tunda a karan kanki ki kaga dacewar hakan na gode." Tana 'kare maganarta sai ta kama hanyar fita tana goge fuskarta.
Komawa tayi ta kwanta tana jin wasai a cikin ranta dama abubuwan da ake mata a gidan yana damunta yau dai ta amayar da abunda yake cikinta ta samu sa'ida.
Ta shigo d'akin ta tsaya a kanta cike da tsageranci ta d'aga murya da fadin." Shahida ke marakunyar ina ce da zaki dinga farfad'awa Baba magana kamar wata sa'arki."
Dama a ciki take da ita sai ta zabura! ta mike tsaye jikinta har tsuma! yake cikin yanayin maganarta tace."Mara kunyar gidanku ce! nace mara kunyar gidanku ce idan kina da mataki ki dauka."
Saliha ta tsorata domin ta san halinta idan tana cikin bacin rai! bata lank'wasuwa kuma idan fada ya ratsa a tsakaninsu da wuya take kai labari domin lilis! take mata.
Sai taja baya, bata daddara ba tace."To mara kunya Da kika mike tsaye kina wani zabura! duka na za kiyi ne kin san dai ni ba sa'arki bace."
Tace."Ki fita ki bani guri bana bukatar ganinki ni duk wanda ba zai ja girmanshi ba to zan hau kai na taka kuma ke baki cancanci na baki girma ba saboda kema baki da ladabi."
Tace."Don Ubanki ni ce mara dalabi.'' Tace."Ubanki dai domin uba bai fi uba ba ehe.!
Saliha ranta ya 'baci kawai sai ta fitar da hannu ta kai mata duka, ai kafin kice me! ta cukumeta ta matseta jikin bango! tana dukanta ta ko'ina."
Saliha ta dinga ihu! tana kakari tare da kiran sunan Baba wai tazo ta ceceta.
Ita kuwa Shahida dukanta kawai take sai kace wata mai iskokai.
Hankali a tashe ta shigo dakin tana fadin." Sai da nace ki kyaleta saboda kinfi kowa sanin halinta idan tana irin wannan halin babu maganar wanda ta ke ji kuma 'karfi ku ba daya bane kin girmeta amma ta fiki 'karfi duka take miki."
Saliha na ihu! take fadin." Ki janyeta ni ba surutu za ki yi ba ta matse min wuya zata kashe ni."
Cikin rarrashi da kwantar da kai tace." Yarinyar kirki yi hakuri ki saketa ai ta daku kada kiji mata ciwo kinga k'arfinku ba daya bane kiyi hakuri ta daina yi miki katsalandan a cikin al'amuranki."
Banza tayi mata ta cigaba da dukanta tana mintsininta!
Baba ta cigaba da banbanki tana kwantar da kai da 'yar murya tace."Shahida kinga bani da lafiya kada wannan 'bacin ran yasa ciwona ya tashi yau da 'kyar zan iya bacci sakamakon wannan al'amari banji dadin maganganun da ki ka fad'a min ba."
Ta fashe da kuka tana cigaba da maganar daso ta tabbatar mata da cewa abun yana ci mata towo a kwarya.
Ganin yanda take kuka ne yasa ta saketa ta koma gefe tana mayar da numfashi, Saliha data samu kanta sai ta wawuri! wani gwangwani da Baba ke ajiye-ajiye a ciki ta kai mata duka dashi da fadin." Shegiya mayya 'yar mai dattin hula." Da yake 'kasa-'kasa tayi maganar yasa ba taji ba, Baba ta buga mata tsawa tare da nuna mata hanyar fita, tana numfarfashin wahala ta fita d'aga dakin.
Baba ta rufa mata baya ba tare da ta sake wata magana ba.
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/K7QH4idftZS5fSw7m2Rueb Ku yi join domin samun damar karanta littafi na d'aya.
Direba yace."Gaskiya ne Alhaji nima na jima ina mamakin mutumin nan da yake ina yawan shigowa unguwar nan ina ganinsa sai nayi ta mamakin yanda akayi rayuwarsa ta lalace haka koda yake duk mutumin da bashi da gaskiya yakan 'kare rayuwarsa a firgice ba tare da ya san ina ya dosa ba."
Hawaye ta share tana jin zafin magangansu tace."Abbah ku dai kuyi masa Addua dashi da masu lalura irin tashi watakila kuma babu d'aya daga cikin abunda kuke zargi mybe jarabtace daga Ubangiji."
Murmushi yayi ya dauko tafkekiyar wayarsa yana dubawa yace." Shahida irin halinku daya da mahaifiyarki Allah ya gafarta mata."
Ta amsa da ameen tana goge fuskarta.
Suna zaune a tsakar gida ita da Saliha suna gyaran kayan miya suka shiga gidan.
Koda ta amsa sallamarsu sai kawai ta mayar da kanta kasa ta cigaba da abinda takeyi tai bala'in shan kunu!
Da yake ya iya Siyasa sai ya cire takalmansa cikin ladabi da 'yar dariya a tare dashi yace."Baba sannu da aiki."
Ciki-ciki ta amsa ita kuwa Saliha ko kallonsa ba tayi ba ballanatanta ta gaisheshi hakan ya 'bata mata rai sosai sai itama ta kudiri aniya a zuciyarta kan cewa duk sanda babanta yazo gidan ta daina gaishe shi.
Da fara'a a tare dashi yace."Ai dawowata kenan na samu yarinyar nan a gidan shine take sheda min abunda ya faru har kika kore ta daga gidanki haba Baba ai hannunka baya ru'bewa ka yanke ka yar."
Hannu ta d'aga masa da fadin." Dakata! Jamilu kazo ne kayi min dadin baki ko kuma kud'ina kazo ka biya ni bana son neman gidin zama ko kuma dama can hakkin rike yarinyar nan a hannuna yake?"
Maganar ta 'bata masa rai amma sai ya basar yace."Haba Baba ki kwantar da hankalinki muyi magana ta fahinta mana ake rasa mutum ma ballanatana kudi."
Tsaki! taja tana cizge alayyahun dake gabanta ta ce." Mutuwa dole ce amma da gangan yarinyar nan tayi min wasarere! da kudi har 'barawo ya sace saboda haka ka tashi ka bani guri bana bukatar tsari da dadin baki mutukar ba biya na kudi za kayi ba."
Ya girgiza kai har ila yau da murmushi a fuskarsa yace."Wai shin ma nawa ne kudin naki.?"
Ta kalleshi she'ke'ke! kafin tace."Kaji fa! kamar gaske har wani tambaya kake kamar wanda zai iya biya."
Dariya yasa baka ta'ba ganin 'bacin ransa saboda ya iya siyasa yace."Ko ba zan iya biya ba ai yana da kyau na sani."
Ta'be baki tayi da fadin." Babu amfanin na fad'a maka tunda ba iya biya za kayi ba."
Ya gyad'a kanshi yana kallonta minti biyu ya giciye yana gyara babbar rigarsa ta zuba masa ido tana kallonsa ya zaro yan dubu-dubu sabbi kar dasu har wasu na zubewa a kasan gurin.
Cike da mamaki take kallonsa yana irgawa cas ya cake mata dubu hamsin a gabanta ya gyara zaman babbar rigarsa da fadin." Gashinan duk da na san ban isa na biya kudin hidimar da akayi min ba ayi hakuri da ni da hali na na san anyi min kokari."
Kunya ce ta rufe ta sai ta sunkuyar da kanta ba tare da tace komai ba har ya gama maganarsa ya fita daga gidan.
Ganin haka yasa Shahida shiga daki ta kwanta kan gado abu biyu suka dame ta irin rayuwar k'as'kancin da take a tsakanin 'bangare biyu da kuma al'amarin *Baban- baba* daya tsaya mata a cikin rai.
Hawaye masu zafi suka dinga karakaina a saman fuskarta hakika maraici bala'i ne tabbas da uwarta tana raye a duniya ta san ba za tayi irin wannan rayuwar ba, Baba Asabe itace ta haifi mamanta itace kuma ta haifi Kawu Musa mahaifin Saliha kenan amma ba tasan me yasa take fifita Saliha a kanta ba, Gashi dai duk ita ta haifi iyayensu amma tafi son Saliha a kanta duk abinda Saliha za tayi daidai ne a gurinta amma ita abu kad'an idan tayi sai ya zama laifi.
Ta shigo dakin ta sameta tana kuka, sai jikinta ya kara sanyi murya ta d'aga da karfi ta ce."Kukan me kuma kike bayan ubanki yazo ya fanshe ki ashe dama yana da kudi mugunta ce take sa baya zuwa ya bani wani abu duba da irin dawainiyar da nake dake ko tausayin tsufa na ba ya ji."
Ta mi'ke zaune cikin 'bacin rai da masifa irin ta kurame! tace."Wai shin Baba ni d'in bare ce a gurinki? ko kuwa bake kika haifi uwata ba?"
Ta rike baki tana kallonta da fadin." Ni kike wa tsawa yau kuma tambotsan naki a kaina zaki sauke shi?"
Tace"Ni tambayarki nake ina so ki bani amsa?
Tace."Ni ce na haifi Uwarki na kuma Haifi Musa su biyu kacal Allah ya ba ni sai me kike so kiji.?
Tace."To me yasa kike 'bakin ciki don kin kula dani kin ciyar dani kin tufarta dani don kinyi min d'awainiya shine kike gorantawa ubana ai sai yana dashi zai zo ya baki."
Cike da dumbun mamaki tace."Shahida yau ubanki kike fifitawa a kaina.?
Tace."Kada kiyi min mummunar fahinta Baba ina so na nuna miki Kuskuran da kike aikatawa kada ki d'auka bana fahimtar komai duk abinda kike ina lure dake kin fi k'aunar Saliha a kaina meye dalili? ko don ita ubanta yana baki kudi ni kuwa uwata ta mutu bata raye babu abunda take tsinana miki shine kike gallaza min saboda kawai tsautsayi ya ratsa an sace kud'inki shine har zaki tattara min kayana ki watsa waje wai kin kore ni Haba Baba ke baki ji kunya ba."
Baba Asabe bakinta ya mutu kallonta kawai take ta cigaba da cewa." Tunda kika dasa sayar da man gyada a gidan nan ni nake zuwa na saro miki kuma bant'ba zubar miki da kudi ba sai wannan karon amma saboda rashin tawakkali kika fita duniya kina zage-zage kowa yana kallonki ai wannan abun kunya ne."
Baba Asabe ta fashe da kuka tasa gefen zaninta ta fyace hanci ta ce."Lallai Shahida wuyanki ya isa yanka ni kikewa rashin kunya ko kuma dai Jamilu da Talatu sunyi miki hud'uba akaina."
Tace."Ni ina ruwana da Talatu itama ai ba k'aunata take ba kuma Abbanmu ba zai zuga ni nayi miki rashin kunya ba."
Ta goge fuska da fadin." To babu laifi tunda a karan kanki ki kaga dacewar hakan na gode." Tana 'kare maganarta sai ta kama hanyar fita tana goge fuskarta.
Komawa tayi ta kwanta tana jin wasai a cikin ranta dama abubuwan da ake mata a gidan yana damunta yau dai ta amayar da abunda yake cikinta ta samu sa'ida.
Ta shigo d'akin ta tsaya a kanta cike da tsageranci ta d'aga murya da fadin." Shahida ke marakunyar ina ce da zaki dinga farfad'awa Baba magana kamar wata sa'arki."
Dama a ciki take da ita sai ta zabura! ta mike tsaye jikinta har tsuma! yake cikin yanayin maganarta tace."Mara kunyar gidanku ce! nace mara kunyar gidanku ce idan kina da mataki ki dauka."
Saliha ta tsorata domin ta san halinta idan tana cikin bacin rai! bata lank'wasuwa kuma idan fada ya ratsa a tsakaninsu da wuya take kai labari domin lilis! take mata.
Sai taja baya, bata daddara ba tace."To mara kunya Da kika mike tsaye kina wani zabura! duka na za kiyi ne kin san dai ni ba sa'arki bace."
Tace."Ki fita ki bani guri bana bukatar ganinki ni duk wanda ba zai ja girmanshi ba to zan hau kai na taka kuma ke baki cancanci na baki girma ba saboda kema baki da ladabi."
Tace."Don Ubanki ni ce mara dalabi.'' Tace."Ubanki dai domin uba bai fi uba ba ehe.!
Saliha ranta ya 'baci kawai sai ta fitar da hannu ta kai mata duka, ai kafin kice me! ta cukumeta ta matseta jikin bango! tana dukanta ta ko'ina."
Saliha ta dinga ihu! tana kakari tare da kiran sunan Baba wai tazo ta ceceta.
Ita kuwa Shahida dukanta kawai take sai kace wata mai iskokai.
Hankali a tashe ta shigo dakin tana fadin." Sai da nace ki kyaleta saboda kinfi kowa sanin halinta idan tana irin wannan halin babu maganar wanda ta ke ji kuma 'karfi ku ba daya bane kin girmeta amma ta fiki 'karfi duka take miki."
Saliha na ihu! take fadin." Ki janyeta ni ba surutu za ki yi ba ta matse min wuya zata kashe ni."
Cikin rarrashi da kwantar da kai tace." Yarinyar kirki yi hakuri ki saketa ai ta daku kada kiji mata ciwo kinga k'arfinku ba daya bane kiyi hakuri ta daina yi miki katsalandan a cikin al'amuranki."
Banza tayi mata ta cigaba da dukanta tana mintsininta!
Baba ta cigaba da banbanki tana kwantar da kai da 'yar murya tace."Shahida kinga bani da lafiya kada wannan 'bacin ran yasa ciwona ya tashi yau da 'kyar zan iya bacci sakamakon wannan al'amari banji dadin maganganun da ki ka fad'a min ba."
Ta fashe da kuka tana cigaba da maganar daso ta tabbatar mata da cewa abun yana ci mata towo a kwarya.
Ganin yanda take kuka ne yasa ta saketa ta koma gefe tana mayar da numfashi, Saliha data samu kanta sai ta wawuri! wani gwangwani da Baba ke ajiye-ajiye a ciki ta kai mata duka dashi da fadin." Shegiya mayya 'yar mai dattin hula." Da yake 'kasa-'kasa tayi maganar yasa ba taji ba, Baba ta buga mata tsawa tare da nuna mata hanyar fita, tana numfarfashin wahala ta fita d'aga dakin.
Baba ta rufa mata baya ba tare da ta sake wata magana ba.
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/K7QH4idftZS5fSw7m2Rueb Ku yi join domin samun damar karanta littafi na d'aya.