← Book details Mafarin Lamari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 10

Sashe 9

Mafarin Lamari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Haka Yaseera taci gaba da amfani da k'wayar maye tana afkawa Samir, tana kuma samun damar yana biya mata buk'ata yadda takeso, batare da yana cikin hayyacin sa ba takashe wayoyinsa, yaran sa ita ke kaisu School ta d'auko su, ko kuma ta tura mai aiki ta taho da su Napep, abokan aikin sa har gida sukazo nemansa, tace musu yatafi k'auyensu kuma babu network, kowa mamakin hakan yakeyi saboda rashin fad'arsa a gurin aiki abashi izini, gashi Samir yana bin doka, tafe dai tafe dai har aka kwashe sati guda ciff Yaseera ta mayar da Samir d'an maye bashi da aiki saidai ta bulbula masa k'waya cikin lemo yasha daga nan sai bacci, sosai Yaseera take sashi a gaba tana masa dariya gami da cewa"kaima kaji yadda mukeji shege, har kana cewa ka tsani halaiyata gashi a sannu nasaka ciki, kullum cikin maye."
Samir baya iya budar baki yace mata uffan, saboda k'wayar tayi masa k'arfi gashi kullum take bashi guda ya shanye, wanda ita kwatarsa take sha.

************

Gefe guda Kabir yafara samun kan Aysher, dan yanzu idan yaje gidan tana fitowa idan ya aika suyi zance, har labarin yaranta tabashi, dan bai nuna mata yasan mijinta ba, ballantana yaran da suka haifa.

A hakan dai harya samu yashawo kan Aysher ta amince ya kawo sadakin sa, bisa taimakon malamin sa dayayi masa aiki akan haka, kafin akawo sadakin Aysher tayita kiran wayar Samir tasanar masa amman wayar sa akashe, dan haka bata wani damu ba dan yanzu zuciyarta soyayyar kabir ne cike a cikinta.

Muje zuwa

MAMAN HANAN
ZAUREN LITTATTAFAN HAUSA.
[12/31/2017, 21:35] Zeeett Zamaniwrite Group Novels: 💐💐💐💐💐

*MAFARIN LAMARIN*

DAGA TASKAR
*ZAMANI WRITER'S ASSOCIATION (Z.W.A)*
________
______________
```WE ARE HERE TO EDUCATE, MOTIVATE,AND ENTERTAIN OUR READER'S.```

_________
______________

©Zeetty
📚zaku iya samun littattafan mu a face book 👇🏻
Fb.me/
ZAMANIWRITERSASSOCIATION

📩zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏻
[email protected]

*MY BEAUTY QUEEN HAKIKA INA ALFAHARI DAKE, ALLAH BAR ZUMUNCI.*

PAGE 30-31
Samir yana cikin wannan hali, kwatsam Mama (mahaifiyar sa) ta sauka a gidan saboda jin shirun yayi yawa kuma gashi bata samunshi a waya, bata kuma da number Yaseera. Sanda mama tazo gidan bata samu Yaseera ba ta tafi gurin Johnson suyi sallama zai koma America, kuma tana sauri tabar k'ofar d'akin a bud'e, sallama Mama ta dingayi taji shiru ba'a amsa mata ba gashi yaran duk sun tafi Makaranta, Baba mai aiki ta tafi tahowa dasu, cikin sa'a Mama ta danna kanta d'akin Samir na da wanda yazama na Yaseera a yanzu, sallama tadingayi taji shiru, hango Samir tayi kwance akan gado yanata shek'a bacci, da sauri Mama tak'arasa tana bubbuga sa tare da tambayarsa ko lafiya? Sam Samir baisan tanayi ba, jijjigashi Mama takeyi shiru gashi dai a zahiri yana numfashi amman babu abinda yake iya motsawa a jikin sa. Ihu mai k'arfi Mama ta saki, kafin tafice daga d'akin da sauri wajen kwates d'in ta nufa gidan dake kusa da na Samir taje tafara bubbuga k'ofar da k'arfi, kana kallonta kasan cewar a rikice take, Emanuel yak'araso ya bud'e k'ofar cikin gur6atacciyar hausar shi yafara tambaya"Mama lafiya kuwa (dayake yasanta d'an zaman da tayi a gidan Samir din)."

Kuka Mama tafarayi tana nuna masa k'ofar gidan Samir gami da cewa"Samir gashi can bashi da lafiya baisan inda kansa yake ba, mara bansa da gawa numfashi." Duk da cewar Emanuel bai fahimci abinda take nufi duka ba, amman yad'an gane wasu dan haka yace"Jesus, what is wrong with him?, kwana biyu baya zuwa office, i call him but his phone is switch off, na tambayi Madam tace min he is travel, ashe yadawo babu lafiya, muje Mama barin fito da mota, just now am back, na zo d'aukar wasu taddune daga office."

Ita dai Mama dayake ba fahimtar abinda yake cewa takeyi ba, dan gaba d'aya a rikice take, ko ina a jikinta rawa yakeyi, da sauri ta koma gidan Samir d'in ta shiga d'akin, tayi yunk'urin d'aukar sa amman inaa, bazata iya ba dan haka ta jira har Emanuel ya shigo yana fad'in"excuse!" Mama da sauri tafito ta nuna masa d'akin da Samir yake kwance, kasan cewar Emanuel k'atoton inyamuri maji k'arfi dan haka ya cicci6i Samir yasashi a mota.

*********
Suna isa asibitin dake cikin kwates din, kai tsaye aka wuce da Samir A & E (Accident and emergency) likitoci suka taru akansa dan gano abinda yake damunsa, jikinsu yayi sanyi matuk'a, sanda suka gano musabbabin matsalar tashi, dan haka Dr. Hussain yafito yana sharce gumin dake fuskar sa, ya k'araso ya samu su Emanuel wanda yakasa komawa Office, bayan yakira ya shaida musu abinda ke faruwa. Dr. Hussain yace"kubiyoni zuwa office, pls inason ganin wani na kusa dashi."

Da sauri Mama da Ema suka k'arasa office d'in kowa zuciyarsa cike da son jin abinda yake damun Samir.

Dubansu Likita yayi kafin ya sauke idonsa akan Mama ya k'ura mata ido, kafin yace"daga gani kece Mahaifiyar wannan mara lafiyan, shin zan iya fad'ar matsalarsa a gaban wannan ko kuma yabamu guri?".

"Zaka iya likita, da badan shiba, bansan yazanyi na kawoshi asibiti ba kafad'a kawai ba matsala." Cewar Mama.

Likita yace"wato Mama a zahirin gaskiya binciken da mukayi mungano cewar Samir yasha magungunar maye masu matuk'ar k'arfi, wanda sune sanadiyyar jefashi cikin wannan halin da yake ciki, wanda bamu da tabbas d'in cewar k'wakwalwarsa tanada cikakken lafiya a yanzu, har sai ya farfad'o k'wayar ta sakeshi, wanda zaikai nan da wasu kwanaki, sai kuyita addu'a kar ya samu ta6in hankali, wanda warkewarsa zaiyi wahala sai wani ikon Allah."
Kuka Mama tafara gami da salati tana fad'in"wallahi likita d'ana ba mashayi bane sai dai idan wannan matar tashi ce ta sashi a wannan muguwar hanyar, dan tun farko abinda yasa ya guji aurenta kenan, 'yar maye ce sosai, ya Allah kabama Samir lafiya." Sosai Mama take kuka abin tausayi.

Emanuel wanda bai gama fahimtar bayanin likita gaba d'aya ba, dan da hausa aka yima Mama bayani, sai da yasake tambayar likita cikin harshen turanci yayi masa bayani sosai, nan shima ya shiga cikin tashin hankali tare da fatan Allah yabashi lafiya. A asibitin Ema yabar Mama ya koma office tare da alk'awarin zai fad'awa Yaseera dan suzo asibitin kar hankalinsu yatashi.

A6angaren Yaseera kuwa, tariga su Baba dawowa gida dan haka ta shigo falon da 'yar guntuwar wak'ar ta, bata damu da ganin gidan a bud'e ba, kasancewar basu da wani matsalar 6arayi a kwates d'in, kai tsaye d'akin ta, ta nufa inda Samir yake a kwance wayam tagani sanda takai kallonta kan gadon ta, taga babu mijinta kwance a gurin. A rud'e ta fice daga falon, sukayi kici6is da Anatu (matar Emanuel) zata shigo gidanta, da sauri Ana ta tareta da cewa"thank God! Kadawo, Ema yanata kiran wayana, yana tambayana ko kadawo?, nazo three times kenan."

"Ke Anatu kin cikamin kunne, fad'amin meye yakawoki gurina dan inada matsalar da tafi zuwanki yanzu." Yaseera yafad'a cikin muryar fad'a.

"Sorry Madam, Ema yace mijinka ba lafiya, yana cikin Hospital d'in asibitin nan so yace ya fad'a maka, kar hankalinka ya tashi." Ana tana gama fad'in haka tabar k'ofar falon Yaseera.

A lokacin kuma Baba tadawo daga d'auko su Aslam daga school.

Kai Yaseera ta dafe tare da fad'in"Oh my God! Waye yazo ya ga D-lovely cikin wannan halin har yakaishi asibiti? Kodai Emanuel ne?". Dan haka a fili Yaseera tace"sai naci kutmar uban Emanuel, zai fad'amin dalilinsa na shigomin gida bama nan."

Baba kuwa tanaji Yaseera ta ambaci hakan ta fara fad'in"sai hak'uri Uwar d'akina, labarin dana samu a kwates d'innan shine, shida Anatu yara hud'u suka haifa yanzu haka, kuma har yanzu ba suyi aure ba, wai sai nan da shekara guda mai zuwa, dan haka kinga irin wad'an nan k'abilun balallai bane susan darajar aure, yara 4 fa Uwar d'akina, zaman zina sukeyi wanda Allah ya tsinewa mai...."

"Ke rufemin baki, tambayarki nayi? Duk kin cikani da surutu to dan uban babanki banason ji ba kisan tashin hankalin da nake ciki ba, ki wuce ki cire musu uniform mu tafi asibiti D-lovely ba lafiya."

Cikin sauri Baba ta ja hannun su Aslam zuwa d'akinsu dan canja musu kaya, bataji haushin zagin da Yaseera tayi mata ba dan kuwa tasaba da hakan, ballan tana yau ya hadun mata da ciwon miji.

A hanyarsu ta zuwa asibiti Yaseera takira wayar Mahaifinta cikin Kuka take sanar masa Samir bashi da lafiya, yana asibiti wasu ne suka kawoshi gida yau da asuba cikin yanayi na maye.............

Muje zuwa

MAMAN HANAN
ZAUREN LITTATTAFAN HAUSA
[12/31/2017, 21:37] Zeeett Zamaniwrite Group Novels: 💐💐💐💐💐

*MAFARIN LAMARIN*

DAGA TASKAR
*ZAMANI WRITER'S ASSOCIATION (Z.W.A)*
________
______________
```WE ARE HERE TO EDUCATE, MOTIVATE,AND ENTERTAIN OUR READER'S.```

_________
______________

©Zeetty
📚zaku iya samun littattafan mu a face book 👇🏻
Fb.me/
ZAMANIWRITERSASSOCIATION

📩zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏻
[email protected]

PAGE 32-33
Kuka sosai Yaseera taci gaba dayi a cikin motar, tana driving tana face hanci, Baba mai aiki fad'i takeyi sai hak'uri Uwar d'akina Allah yasakama uban gida na.

Cikin wannan halin suka k'atasa asibitin, idan kaga Yaseera saika rantse da Allah bata da wani masaniyya game da halin da Samir ya tsinci kansa a ciki, da tambaya suka k'arasa d'akin da aka kwantar da Samir din.

Da gudu Yaseera tak'arasa gadon da yake kwance kamar gawa, ta kwanta akan kirjinsa tana kuka sosai mai had'e sheshshek'a tare da fad'in"Allah yasaka maka D-lovely, duk mugun daya aikata maka hakan Allah ya baiyanashi, bazamu ta6a yafe masa ba."

Cikin wannan halin Mahaifinta yazo ya risketa, tare da wasu ma'aikatan NNPC gumi ne ya fara tsatstsafowa daga fuskar Alh. Auwal Mataimaki yasa hankici yana sharewa, kallo d'aya yayima Samir yaji tausayin shi yakamasa, tabbas an zalunceshi, shi ba mai shaye-shaye ba an mayar da shi d'an maye k'arfi da yaji, dan sunje ofishin likita yayi musu bayanin duk abinda yake faruwa akan Samir d'in.
Chapter 9 · 0% Book details