Sashe 2
Mafarin Lamari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Aslam da baisan wainar da ake toya ba, bayan baya gida amman jikin sa yabashi cewar Abban sane yayima Momy irin abin da yake mata kullum a gaban su (Duka).
Aslam yanada wayau kasan cewar shi yaro d'an shekara shida yana primary Two a School, haka Islamiyya yana Aji 2 duk aji d'aya yake tafiya da boko da Arabiyya.
Binsu yayi da kallo cikin Zuciyar sa yana mai k'ara tsanar Abban nasa.
Da taimakon Maryam Aysher tayi wanka tare da gasa jikinta, bayan tafito Maryam ta bata maganin ciwon jiki tasha anan bacci ya d'auki Aysher, bacci mai cike da alamun wahala.
Da wurwuri yadawo gida hanun sa d'auke da wani farin takarda, fuskar sa tana d'auke da alamun farin ciki.
Da sallama yashigo gidan ya tarar da Maryam a kitchen tana d'ora musu abincin dare, fuskar ta a tur6une ta gaisheshi, ya amsa da fara'a sosai yak'ara da cewa"Maryam kece a gidan namu, ya su Umma da Baba?"
"Suna nan lafiya" tabashi tare da shan toka (lols 'yan skt)
"Ina Momy'n Aslam?".
" Tana d'aki a kwance batajin dad'i."
Sai yanzu Samir ya tuna da abinda yayi mata da safe kafin ya fita, cikin mutuwar jiki ya shige d'akin da take kwance.
A zaune yasameta tayi tagumi, yashigo da sallama ta amsa tana murmushin yak'e kafin tace"sannu da dawowa Abban Aslam, ya k'ok'ari?."
"Alhamdulillah Sulty na, yau Allah ya kar6i addu'ar mu, ga takaddata ta d'aukar aiki a NNPC."
Hannu Aysher ta d'aga sama tare da fad'in"Alhamdulillah, Allah nagode maka Allah maji rokon bawansa, nayi maka murna Abban Aslam Ubangiji yasa kafara a sa'a."
Kai ya gyad'a yana fad'in"Ameen ameen Sulty na, kifagar ceni dan Allah."
Shiiiiii Aysher tayi masa alamun yayi shiru kafin tace"karka fara Maryam tana gidan nan, kabari sai ta tafi."
_Cikin zuciyar sa mamakin sanyin halin Aysher yakeyi da hak'urin ta, yana godiya da Allah baisa ya datse igiyar auren su dayayi niyyar yi yau ba._
"Bakomai Sulty barin je na dubo miki magani, ina ne yake maki ciwo yanzu."
"Bako ina dan nasha magani, kasan cewar na tanadeshi tuntuni, saboda irin haka."
Kallon matar tashi yay, yana tausaya mata abubuwan dayayi mata, kafin ya girgiza kai yafice dan barin d'akin.
Aysher kuwa mamaki ne ya rufeta yaushe rabon da Abban Aslam yakirata da wannan sunan *SULTY* tun farkon samun cikin Aslam.
```Kukasance tare dani, dan jin farkon tarihin wad'an nan ma'aurata.```
MAMAN HANAN
ZAUTEN LITTATTAFAN HAUSA
[12/23/2017, 18:37] Zeeett Zamaniwrite Group Novels: 💐💐💐💐💐
*MAFARIN LAMARIN*
DAGA TASKAR
*ZAMANI WRITER'S ASSOCIATION (Z.W.A)*
©Zeetty
PAGE 6-7
Cikin lokaci k'ank'ani al'amura suka canjama Samir da Aysher, kai tsaye aka bashi gida a NNPC dake cikin Quaters na Kaduna, komai da komai ansa a gidan bazasu shiga da komai ba sai kayan sakawan su, dan haka Aysher tayima 'yan uwanta sallama da danginta, suka d'auki hanyar kaduna, bisa rakiyar k'awanta da wasu daga cikin dangin Mahaifiyar ta.
Kwanan sh d'aya 'yan rakiya suka juyo dan komawa gida, Aslam da Afra ansamo musu makaranta anan cikin NNPC Quaters d'in. Wani kana kallonsu Aysher da Samir a wannan lokacin dole subaka sha'awa, dan tabbas hutu yazo musu sosai, gaba d'aya sun canja, musamman Aysher tak'ara wani fresh da haske, gata daman tubarkallah akwai kyau.
Satin su biyu da dawowa Al'amura duk sun canja, wani kulawa da soyayya Samir yake yima matar shi, wanda baita6a yimata ba a farkon.
Tausayin matar sa sosai yakeyi idan yatuna da abubuwan daya aikata mata abaya, lallai talauci baiyiba, dole anemi tsari dashi, kullum tunanin samir kenan a gida ko Office idan yakad'aice.
Fara aikin sa bada dad'ewaba aka k'ara masa matsayi a gurin aiki, wannan abu bak'aramin dad'i yayima Aysher da Mijinta ba.
Washergari har gurin aiki Aysher tarakashi bayan sunkai su Aslam School, tare suka bud'e sabon Office d'in Abban Aslam. Suka shiga da bismillah addu'a Aysher tayima mijin ta sosai kafin su shafa.
Samir rungumo Aysher yayi yana hawaye "Sulty na, kiyafemin na zalunceki dayawa, na biyewa sharrin shaid'an da zugin abokai, dan Allah kigafarceni (yak'arasa fad'a tare da k'ok'arin durk'usa mata)."
Saurin dagoshi Aysher tayi tana share mishi hawaye kafin tace"Abban Aslam na yafe maka, amman dan Allah nima kayimin alk'awarin idan natashi neman wani abu a gurinka bazaka hanani ba."
Dasauri Samir yace"Namiki Alk'awari Sulty na, banga abinda nake dashi a duk duniyar nan, dazaki nema nakasa yimiki ba, anjima za'a kawomiki sabuwar motar ki, saboda yanzu hanun ki ya fad'a, zakidinga taimakamin dakai su Aslam makaranta da d'auko su."
Kai kawai Aysher ta gyad'a masa.
Soyayya Samir yake nunama Sulty Aysher sosai.
*BAYAN SATI BITU*
Komai yawuce a gurin wad'an nan ma'auratan.
Ranar Monday da misalin k'arfe 2:00pm, akayima Samir waya daga School d'insu Aslam cewa yazo yad'auki yaranshi dan andad'e da tashi a School kuma gashi ankira wayar Madam akashe.
Arikice Samir yabar Office kai tsaye School d'in ya isa, yad'auki yaranshi ransa a 6ace, yana mamikin inda Sulty ta tafi batazo tad'auki yaransu a School ba, wayar ta kuma a kashe, Afra sai surutu take masa amman yak'i kulata, yana tunanin halin da zaije ya riski matar sa a ciki idan sun k'arasa gida.
Yana Parking yafito yabud'ema yaran baijira fito warsuba yasakai cikin gidan da sauri, yayi amfani da da key d'in gurinshi ya bud'e gidan, kiranta yafarayi yaji shiru, kai tsaye d'akin ta ya nufa dammmm kirjinsa yabuga sakamakon ganin Akwatinan Aysher a zube a kan gado, babu babban cikin sa, a hankali ya k'arasa kan gadon, ya k'arasa kan gadon cikin sanyin jiki, takadda yagani akan gadon a hankali yasa hannu yad'auka ya fara warwarewa, rubutun Aysher yagani kamar haka:-
_ASSALAMU ALAIKUM_
_Abban Aslam kayi hak'uri da hukuncin dana yanke a tsanin zamana dakai, zanyi hakan ne bawai dan bana sonka ba, a'a sai nace duk duniya bayan iyayenka nafi kowa sonka._
_Karka manta da alk'awarin dakayi min nacewa duk abinda na nema a gurinka zaka yimin, bakomai nake soba Abban Aslam dan Allah kataimaka ka sauwak'emin, murabu dakai rabuwa na har abada, bawai dan bana sonka ba saidon lokacin da nakejira yazo kenan naci gaba da hak'urin zamadakai, dan inaso na k'aryata duniya cewar ni mai farar k'afa ce, nashanye duk abubuwan da kakemin, har zuwa yanzu da Allah ya axurta ka, nayanke rabuwa dakai._
_Kataimaka kayimin abinda nakeso cikin ruwan sanyi, wallahi wallahi nagama zama dakai har abada, sai naji daga gareka._
_Ma'assalam._
*Matarka a baya, Aysher Muhammad Rogo.*
Muje zuwa.......
MAMAN HANAN
ZAUREN LITTATTAFAN HAUSA.
[12/28/2017, 10:29] Zeeett Zamaniwrite Group Novels: [11/19, 5:59 PM] Zeetty: 💐💐💐💐💐
*MAFARIN LAMARIN*
DAGA TASKAR
*ZAMANI WRITER'S ASSOCIATION (Z.W.A)*
©Zeetty
```Ayimin afuwa wajen rubuta PAGE nayi kuskure 5-6 zan saka, but nasa 6-7 so yanzu zan gyara.```
PAGE 7-8
Samir yana gama karanta wannan wasik'ar ya sunkuyar da kansa k'asa yanajin zubar wasu hawaye masu zafi daga idanuwan sa, hak'ik'a abokan sa sun kaishi sun baro, yakasa yadda da k'addara, lallai imanin sa bai zamo cikakke ba, daga kansa yayi yana tunanin irin abubuwan daya aikatama Sulty Aysher a baya, lallai da wuya ta iya yafe masa.............
~ASALIN LABARIN~
_Aysher Muhammad rogo itace yarinya ta 4 a gurin iyayen ta Dr.Muhammad Rogo da Fatima, Isah ne babba sai Usman,Auwal sai Aysher, Hadiza da Auta Maryam._
_Iyayen Aysher 'yan boko ne musamman Mahaifin ta wanda likitan hak'ori ne, Aysher sun had'u da Samir ne tun tana aji biyar a makarantar sakandire, abokine ga Babban yayanta Isah, tare suka gama karatu a B.U.K, kuma margayi malam Bashir amini ne sosai a gurin Dr.Muhammad mahaifi ga Aysher._
_Malam Bashir malamin makaranta ne kafin mutuwar sa, mutum ne nagari mai halin dattako._
_Sosai Dr.Muhammad yakar6i maganar auren Aysher da Samir, dan yasan halin mahaifin sa, kuma yana ganin hankalin Samir d'in ganin yadda suke tafiyar da al'amuransu da d'ansa Isah._
_Dakanshi ya samo musu aiki tare da Isah a ma'aikatar kar6an haraji ta garin kano, Aysher tana gama karatun Sakandire aka sha bikinta da Angon ta Samir._
_Farkon zaman auren su abin sai son barka ga duk wanda yaje gidan, wani irin soyayya suke yima junan su, wanda basa iya 6oyewa a gaban kowaye, mafi akasari ba'ason zuwa gidan musamman ranar Week end dan Samir dakan sa yayi gargad'i da hakan, a cewar sa, wannan ranar, ranar sa ne shi kad'ai, salon bai canja ba a lokacin da Aysher ta samu ciki, kulawa yake nuna mata sosai tare da tsantsar soyyayya ga abinda zata haifo masa._
_Lamarin yafaro ne bayan Haihuwar Aslam, lokacin yanada shekaru uku, a wannan lokacin sabuwar gwabnati ta hau kujerar mulkin kano, dan haka aka sallami ma'aikata dayawa, cikin su harda Samir. Hankalin Dr.Muhammad yayi bala'in tashi dajin wannan labarin._
_Shikansa Samir dafarko yad'auki al'amarin dacewa kaddara ne, amman daga baya yasamu wasu shaid'anun abokai suka zugeshi da cewa had'in baki ne daga gurin surukin nasa idan ba hakaba, meyasa ba'a kori Isah ba?, wannan kawai anyine dan a tozarta Samir d'in._
[11/19, 6:57 PM] Zeetty: _Dan anga yafara tara Iyali, tun Samir bai d'auki maganar da mahimmanci ba, har yad'auka, dan haka lokaci guda yafara canjama Sulty shi, abu kad'an idan tayi saiya rufeta da masifa da bala'i, wata rana har dukan ta yakeyi agaban Aslam, tun yaron baya fahimta har yafara ganewa, a haka Maryam k'anwarta tazo takawo mata ziyara wata rana ta risketa jiki duk shatin bulala kamar wata Jaka, hankalin Maryam yatashi dan haka takira yayan su Isah a waya tana sanar masa, hankalin sa a tashe ya k'araso gidan ganin irin dukan dake jikin k'anwarsa wani tausayin ta ya kamashi._
_Bayan ankaita asibiti binciken likita nafarko daya fara ganowa shine, Aysher tana d'auke da hawan jini, Dr.Muhammad ransa ya6aci dajin haka, yakuma tausayama 'yar sa, dan yasan may be tana fuskantar matsala a gidan mijin ta, dan su kansu yagama canja musu baya zuwa gidan, idan suka had'u da Isah saidai Isah yayi mishi magana._
Aslam yanada wayau kasan cewar shi yaro d'an shekara shida yana primary Two a School, haka Islamiyya yana Aji 2 duk aji d'aya yake tafiya da boko da Arabiyya.
Binsu yayi da kallo cikin Zuciyar sa yana mai k'ara tsanar Abban nasa.
Da taimakon Maryam Aysher tayi wanka tare da gasa jikinta, bayan tafito Maryam ta bata maganin ciwon jiki tasha anan bacci ya d'auki Aysher, bacci mai cike da alamun wahala.
Da wurwuri yadawo gida hanun sa d'auke da wani farin takarda, fuskar sa tana d'auke da alamun farin ciki.
Da sallama yashigo gidan ya tarar da Maryam a kitchen tana d'ora musu abincin dare, fuskar ta a tur6une ta gaisheshi, ya amsa da fara'a sosai yak'ara da cewa"Maryam kece a gidan namu, ya su Umma da Baba?"
"Suna nan lafiya" tabashi tare da shan toka (lols 'yan skt)
"Ina Momy'n Aslam?".
" Tana d'aki a kwance batajin dad'i."
Sai yanzu Samir ya tuna da abinda yayi mata da safe kafin ya fita, cikin mutuwar jiki ya shige d'akin da take kwance.
A zaune yasameta tayi tagumi, yashigo da sallama ta amsa tana murmushin yak'e kafin tace"sannu da dawowa Abban Aslam, ya k'ok'ari?."
"Alhamdulillah Sulty na, yau Allah ya kar6i addu'ar mu, ga takaddata ta d'aukar aiki a NNPC."
Hannu Aysher ta d'aga sama tare da fad'in"Alhamdulillah, Allah nagode maka Allah maji rokon bawansa, nayi maka murna Abban Aslam Ubangiji yasa kafara a sa'a."
Kai ya gyad'a yana fad'in"Ameen ameen Sulty na, kifagar ceni dan Allah."
Shiiiiii Aysher tayi masa alamun yayi shiru kafin tace"karka fara Maryam tana gidan nan, kabari sai ta tafi."
_Cikin zuciyar sa mamakin sanyin halin Aysher yakeyi da hak'urin ta, yana godiya da Allah baisa ya datse igiyar auren su dayayi niyyar yi yau ba._
"Bakomai Sulty barin je na dubo miki magani, ina ne yake maki ciwo yanzu."
"Bako ina dan nasha magani, kasan cewar na tanadeshi tuntuni, saboda irin haka."
Kallon matar tashi yay, yana tausaya mata abubuwan dayayi mata, kafin ya girgiza kai yafice dan barin d'akin.
Aysher kuwa mamaki ne ya rufeta yaushe rabon da Abban Aslam yakirata da wannan sunan *SULTY* tun farkon samun cikin Aslam.
```Kukasance tare dani, dan jin farkon tarihin wad'an nan ma'aurata.```
MAMAN HANAN
ZAUTEN LITTATTAFAN HAUSA
[12/23/2017, 18:37] Zeeett Zamaniwrite Group Novels: 💐💐💐💐💐
*MAFARIN LAMARIN*
DAGA TASKAR
*ZAMANI WRITER'S ASSOCIATION (Z.W.A)*
©Zeetty
PAGE 6-7
Cikin lokaci k'ank'ani al'amura suka canjama Samir da Aysher, kai tsaye aka bashi gida a NNPC dake cikin Quaters na Kaduna, komai da komai ansa a gidan bazasu shiga da komai ba sai kayan sakawan su, dan haka Aysher tayima 'yan uwanta sallama da danginta, suka d'auki hanyar kaduna, bisa rakiyar k'awanta da wasu daga cikin dangin Mahaifiyar ta.
Kwanan sh d'aya 'yan rakiya suka juyo dan komawa gida, Aslam da Afra ansamo musu makaranta anan cikin NNPC Quaters d'in. Wani kana kallonsu Aysher da Samir a wannan lokacin dole subaka sha'awa, dan tabbas hutu yazo musu sosai, gaba d'aya sun canja, musamman Aysher tak'ara wani fresh da haske, gata daman tubarkallah akwai kyau.
Satin su biyu da dawowa Al'amura duk sun canja, wani kulawa da soyayya Samir yake yima matar shi, wanda baita6a yimata ba a farkon.
Tausayin matar sa sosai yakeyi idan yatuna da abubuwan daya aikata mata abaya, lallai talauci baiyiba, dole anemi tsari dashi, kullum tunanin samir kenan a gida ko Office idan yakad'aice.
Fara aikin sa bada dad'ewaba aka k'ara masa matsayi a gurin aiki, wannan abu bak'aramin dad'i yayima Aysher da Mijinta ba.
Washergari har gurin aiki Aysher tarakashi bayan sunkai su Aslam School, tare suka bud'e sabon Office d'in Abban Aslam. Suka shiga da bismillah addu'a Aysher tayima mijin ta sosai kafin su shafa.
Samir rungumo Aysher yayi yana hawaye "Sulty na, kiyafemin na zalunceki dayawa, na biyewa sharrin shaid'an da zugin abokai, dan Allah kigafarceni (yak'arasa fad'a tare da k'ok'arin durk'usa mata)."
Saurin dagoshi Aysher tayi tana share mishi hawaye kafin tace"Abban Aslam na yafe maka, amman dan Allah nima kayimin alk'awarin idan natashi neman wani abu a gurinka bazaka hanani ba."
Dasauri Samir yace"Namiki Alk'awari Sulty na, banga abinda nake dashi a duk duniyar nan, dazaki nema nakasa yimiki ba, anjima za'a kawomiki sabuwar motar ki, saboda yanzu hanun ki ya fad'a, zakidinga taimakamin dakai su Aslam makaranta da d'auko su."
Kai kawai Aysher ta gyad'a masa.
Soyayya Samir yake nunama Sulty Aysher sosai.
*BAYAN SATI BITU*
Komai yawuce a gurin wad'an nan ma'auratan.
Ranar Monday da misalin k'arfe 2:00pm, akayima Samir waya daga School d'insu Aslam cewa yazo yad'auki yaranshi dan andad'e da tashi a School kuma gashi ankira wayar Madam akashe.
Arikice Samir yabar Office kai tsaye School d'in ya isa, yad'auki yaranshi ransa a 6ace, yana mamikin inda Sulty ta tafi batazo tad'auki yaransu a School ba, wayar ta kuma a kashe, Afra sai surutu take masa amman yak'i kulata, yana tunanin halin da zaije ya riski matar sa a ciki idan sun k'arasa gida.
Yana Parking yafito yabud'ema yaran baijira fito warsuba yasakai cikin gidan da sauri, yayi amfani da da key d'in gurinshi ya bud'e gidan, kiranta yafarayi yaji shiru, kai tsaye d'akin ta ya nufa dammmm kirjinsa yabuga sakamakon ganin Akwatinan Aysher a zube a kan gado, babu babban cikin sa, a hankali ya k'arasa kan gadon, ya k'arasa kan gadon cikin sanyin jiki, takadda yagani akan gadon a hankali yasa hannu yad'auka ya fara warwarewa, rubutun Aysher yagani kamar haka:-
_ASSALAMU ALAIKUM_
_Abban Aslam kayi hak'uri da hukuncin dana yanke a tsanin zamana dakai, zanyi hakan ne bawai dan bana sonka ba, a'a sai nace duk duniya bayan iyayenka nafi kowa sonka._
_Karka manta da alk'awarin dakayi min nacewa duk abinda na nema a gurinka zaka yimin, bakomai nake soba Abban Aslam dan Allah kataimaka ka sauwak'emin, murabu dakai rabuwa na har abada, bawai dan bana sonka ba saidon lokacin da nakejira yazo kenan naci gaba da hak'urin zamadakai, dan inaso na k'aryata duniya cewar ni mai farar k'afa ce, nashanye duk abubuwan da kakemin, har zuwa yanzu da Allah ya axurta ka, nayanke rabuwa dakai._
_Kataimaka kayimin abinda nakeso cikin ruwan sanyi, wallahi wallahi nagama zama dakai har abada, sai naji daga gareka._
_Ma'assalam._
*Matarka a baya, Aysher Muhammad Rogo.*
Muje zuwa.......
MAMAN HANAN
ZAUREN LITTATTAFAN HAUSA.
[12/28/2017, 10:29] Zeeett Zamaniwrite Group Novels: [11/19, 5:59 PM] Zeetty: 💐💐💐💐💐
*MAFARIN LAMARIN*
DAGA TASKAR
*ZAMANI WRITER'S ASSOCIATION (Z.W.A)*
©Zeetty
```Ayimin afuwa wajen rubuta PAGE nayi kuskure 5-6 zan saka, but nasa 6-7 so yanzu zan gyara.```
PAGE 7-8
Samir yana gama karanta wannan wasik'ar ya sunkuyar da kansa k'asa yanajin zubar wasu hawaye masu zafi daga idanuwan sa, hak'ik'a abokan sa sun kaishi sun baro, yakasa yadda da k'addara, lallai imanin sa bai zamo cikakke ba, daga kansa yayi yana tunanin irin abubuwan daya aikatama Sulty Aysher a baya, lallai da wuya ta iya yafe masa.............
~ASALIN LABARIN~
_Aysher Muhammad rogo itace yarinya ta 4 a gurin iyayen ta Dr.Muhammad Rogo da Fatima, Isah ne babba sai Usman,Auwal sai Aysher, Hadiza da Auta Maryam._
_Iyayen Aysher 'yan boko ne musamman Mahaifin ta wanda likitan hak'ori ne, Aysher sun had'u da Samir ne tun tana aji biyar a makarantar sakandire, abokine ga Babban yayanta Isah, tare suka gama karatu a B.U.K, kuma margayi malam Bashir amini ne sosai a gurin Dr.Muhammad mahaifi ga Aysher._
_Malam Bashir malamin makaranta ne kafin mutuwar sa, mutum ne nagari mai halin dattako._
_Sosai Dr.Muhammad yakar6i maganar auren Aysher da Samir, dan yasan halin mahaifin sa, kuma yana ganin hankalin Samir d'in ganin yadda suke tafiyar da al'amuransu da d'ansa Isah._
_Dakanshi ya samo musu aiki tare da Isah a ma'aikatar kar6an haraji ta garin kano, Aysher tana gama karatun Sakandire aka sha bikinta da Angon ta Samir._
_Farkon zaman auren su abin sai son barka ga duk wanda yaje gidan, wani irin soyayya suke yima junan su, wanda basa iya 6oyewa a gaban kowaye, mafi akasari ba'ason zuwa gidan musamman ranar Week end dan Samir dakan sa yayi gargad'i da hakan, a cewar sa, wannan ranar, ranar sa ne shi kad'ai, salon bai canja ba a lokacin da Aysher ta samu ciki, kulawa yake nuna mata sosai tare da tsantsar soyyayya ga abinda zata haifo masa._
_Lamarin yafaro ne bayan Haihuwar Aslam, lokacin yanada shekaru uku, a wannan lokacin sabuwar gwabnati ta hau kujerar mulkin kano, dan haka aka sallami ma'aikata dayawa, cikin su harda Samir. Hankalin Dr.Muhammad yayi bala'in tashi dajin wannan labarin._
_Shikansa Samir dafarko yad'auki al'amarin dacewa kaddara ne, amman daga baya yasamu wasu shaid'anun abokai suka zugeshi da cewa had'in baki ne daga gurin surukin nasa idan ba hakaba, meyasa ba'a kori Isah ba?, wannan kawai anyine dan a tozarta Samir d'in._
[11/19, 6:57 PM] Zeetty: _Dan anga yafara tara Iyali, tun Samir bai d'auki maganar da mahimmanci ba, har yad'auka, dan haka lokaci guda yafara canjama Sulty shi, abu kad'an idan tayi saiya rufeta da masifa da bala'i, wata rana har dukan ta yakeyi agaban Aslam, tun yaron baya fahimta har yafara ganewa, a haka Maryam k'anwarta tazo takawo mata ziyara wata rana ta risketa jiki duk shatin bulala kamar wata Jaka, hankalin Maryam yatashi dan haka takira yayan su Isah a waya tana sanar masa, hankalin sa a tashe ya k'araso gidan ganin irin dukan dake jikin k'anwarsa wani tausayin ta ya kamashi._
_Bayan ankaita asibiti binciken likita nafarko daya fara ganowa shine, Aysher tana d'auke da hawan jini, Dr.Muhammad ransa ya6aci dajin haka, yakuma tausayama 'yar sa, dan yasan may be tana fuskantar matsala a gidan mijin ta, dan su kansu yagama canja musu baya zuwa gidan, idan suka had'u da Isah saidai Isah yayi mishi magana._