Sashe 1
Mafarin Lamari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
[12/23/2017, 18:37]
__
*MAFARIN LAMARIN*
DAGA TASKAR
*ZAMANI WRITER'S ASSOCIATION (Z.W.A)*
©Zeetty
_GARGA'DI_
_Wannan labarin nawa da abin da ya k'unsa, duk mallakar marubuciyar ce. Saboda haka sai a guji juya, ko sarrafa wannan labarin batare da izini ba. In kunne yaji........_
_TUNATAR WA_
_Wannan labarin kagaggen labari ne, don fad'akarwa da Nisha d'antar da masu karatu. Saboda haka sai a guji yin zargi ko zaton cewa anyi wannan labari ne domin a musgunawa wani ko wasu, haka sunaye da garuruwan dake cikin wanna labari, an sane kawai don k'ayata labarin._
_GAREKU MARUBUTA_
_Ina kira a gareku, da mu gyara rubutun mu, musan abinda zamu dinga sakawa dan gyara rayuwar k'annemu da 'ya'yanmu, kar mu 6ata musu tarbiya da sakawa yara buri, abinda bazai yiwu ba a wannan zamanin mudaina rubutawa, mutuna online novels mafi akasari 'yan mata yanzu sun raja'a a kansa, dan Allah muhankalta._
```NOTE```:- *Masu karatu kuyi hak'uri bazaku samu cigaban Labarin littafin Hanyar libiya ba, saboda wani dalili mai karfi, ku gafarceni, dalilin haka nema yasa nafara sabon novel.*
*LITTATAFAN MARUBUCIYAR*
*HANGEN DALA*
*DAGA ALLAH NE*
*HANYAR LIBIYA*
*'DABI'A*
*ZUBAR HAWAYE*
*NAMIJIN DUNIYA*
```BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM.```
PAGE 1-2
Shigowa gida yayi ko sallama babu, yafara ball da wani baho daya gani a gefen tsakar gidan, cikin bala'i yafara magana"aikin banza aikin wofi, ni za'a kawoma iskanci a cikin gidan nan?, toh zan yimiki wulak'anci, Aysher ina kike, yooo gani d'an iska ko? Ina magana kina ciki kin maidani shashasha, kai uban giji kayi mana arziki ina ganin wulak'anci a gurin matar nan, bazaki fito ba saina shigo har d'akin na nakad'a miki duka, a gaban 'ya'yan naki kaza uwar son 'ya'ya.?"
Da sauri har tana cin tuntu6e ta fito, tana cewa"kayi hak'uri Abban Aslam, wallahi Afra ce take so tayi bacci, shine nake lalla6ata dan nasamu tayi bacci na k'arasa aiki na."
Doguwar tsaki ya saki, kafin yafara magana cikin kumfar baki"Kinji tsiyar ba, daga anyi miki magana sai kice 'ya'ya sai bala'in son 'ya'ya, wuce kibani guri nidai Allah kawomin ranar da zan rabu da wannan bala'in, saboda banda kud'i kin mayar dani d'an iska, shashasha ko?"
"Kayi hak'uri Abban Aslam ba haka bane, ka gafarceni idan na 6ata maka rai." Ta k'arasa fad'a tare da juyawa dan komawa d'akin ta.
Fusgota yayi kafin ya wanketa da mari, yafara magana cikin hargagi"Ehhh mana wato gani d'an iska ina magana kin tafi kin barni wato nagayawa iska ko.?"
Hanunta dafe da kuncin ta tafara magana tana hawaye tace"Kayi Hakuri Abban Aslam, kace natafi, na juya domin tafiyar, amman yanzu kace nayi maka badai-dai ba, kadaure ka sanar dani laifin dana aikata gareka kake hukunta ni, ta wannan hanyar dan Allah, auren so mukayi ni dakai, bawanda akayima dole amman kwata-kwata baifi zaman shekara d'aya mukayi cikin kwanciyar hankali ba.?"
"Hmmm tuhumata kikeyi,? Nace tuhumata kikeyi, tunda na aureki wane cigaba nasamu sam babu wani cigaba kullum sai komawa baya nakeyi, duk abokaina sun fini kud'i da arziki, nikam tabbas na auro mai farar k'afa, zama nin nan ina ake auren so? Sai dai auren kud'i, to bari kiji dakyau, ina nan nasa ayimin binciken matar aure, auren jari zanyi, 'yar alasawa, muga tsiya, shashasha kawai."
Yana gama fad'in haka yasa kai yafice dan barin gidan.
Komawa tayi da baya ta shige d'aki, zama tayi ta rafka tagumi, shin me natsarema Abban Aslam lokaci guda ya canja min?, talaucin nan bani na d'ora mana ba, lallai nice ma mai farar k'afar?, ikon Allah.
Bayan ta gama komai ta gyara gidan tsaff ta d'auko turaren tsinke mai rangwamen kud'i ta kunna, kud'in da Yayanta Nasiru ya bata shekaran jiya da taje gida dashi ta sake amfani yau dan yimusu cefane, Macaroni ta dafa da dankalin turawa, ta siyo d'ayen kifinta ta soya ta watsa a ciki.
Bayan ta gama komai ta share gidan, ga goge ko ina tsaf, tashiga wanka ta fito ta kimtsa, cikin kwalliyarta mai sauk'i, hak'ik'a AYSHER tanada kyau, koda ace batayi kwalliya ba, dubeta yanzu kamar bata ta6a haihuwar yara har guda biyu ba.
Tana zaune a falo ya shigo yana cika yana batsewa, salama yayi ciki-ciki, Aysher ta amsa tare da fad'in"Sannu da dawowa Abban Aslam."
"Yauwa sannu" ya fad'a a dake.
Tace"Me zaka farayi wanka ko cin abinci.?"
"Bazanyi wankan ba, nace bazanyi wankan ba ko dole ne, zoki mak'ureni nayi dole uwata."
"Yi hakuri barin kawo maka abinci."
(Tak'arasa fad'a tare da mik'ewa dan zuwa kawo mashi abinci)
Try ta d'auko mai d'auke da food flask da plate da cokali, ta k'araso gaban sa ta ajiye tare da bud'ewa ta zuba masa, ruwa ta d'auko a roba ta ajiye masa a gaban sa, duk yana binta da kallo saida ta gama tace"Bismillah"
Yace"Kina wani yimin abu isa-isa idan tak'amarki yau ban baki kud'in cefane ba kiyimin list, in sha Allahu zan biyaki idan nayi kud'i."
"Kayi hak'uri duk maganar baikai haka ba."
"'Daukar abincin yayi yafara ci kamar dole, daga k'arshe dai zagewa yayi, yaci yayi kat, kafin ya mik'e a 3 seater, yana satan kallon matar sa, tayi masa kyau take wani sha'awata ya lullu6eshi."
"Zan shiga ciki Abban Aslam saida safe, saika shigo."
Yace"Aikin kenan, toh banyadda ba kijira nagama kallo, har lokacin tashina yayi mushiga tare, inada buk'ata, kinsan ai dole zan buk'ace ki wannan kwalliya haka dan tsabar jarabarki ta motsa shiyasa kika yimin ita, kijira zan biyaki hakkinki, kar Allah yakamani kodan saboda haka narasa ganin dai-dai, barin gama mushige dan nasan ko kinshiga ciki ba bacci zaki iya ba, mayya kawai."
Maganar tasa tayima Aysher ciwo, amman ba yadda zatayi, komawa tayi ta zauna tana kissima abubuwa dayawa a ranta, wato yanada buk'atar ta amman shine zai juya maganar kanta, Allah kayimin agaji........
MAMAN HANAN
ZAUREN LITTATTAFAN HAUSA.
[12/23/2017, 18:37] Zeeett Zamaniwrite Group Novels: 💐💐💐💐💐
*MAFARIN LAMARIN*
DAGA TASKAR
*ZAMANI WRITER'S ASSOCIATION (Z.W.A)*
©Zeetty
PAGE 3-4
Washe gari da wani masifar yatashi, ko karyawan safe bai tsaya yayi a gidan ba.
Ita dai Aysher baiwar Allah fara gyaran gidan tayi tsaff tayima yaranta wanka ta shirya Aslam yatafi School.
Tagumi tayi tana tunanin halin mijinta da zaman su na da, da kuma na yanzu, tashare hawayen dake zubowa daga fuskar ta, hannu ta d'aga tana rokon Allah ya kawo mata mafita, amman cikin ranta ta kuduri wani abu a cikin sa.
12:00pm yashigo gidan da sallama kafin ya d'ora daga inda ya tsaya fad'i yake"Ke matsiyaciya fito, za'ayita ta k'are nagaji da wannan bak'in talaucin naki, daman tunda naga kinnace saini abin yabani mamaki, ashe kinsan kalarki wato mai farar k'afa ne ke, Mamana da kanta yau tace na hak'ura da wannan auren da kullum babu cigaba sai ci baya."
Cikin K'walla Aysher ta fara magana"Kayi hakuri Abba Aslam, karka rabu dani a wannan yanayin, koma zaka sakeni ina rok'onka Alfarma kabarni nayi zaman 'ya'yana dan Allah."
"Mtswwww kinji tsiyar taki ba?, ana magana sai ki fara cewa yaran ki, toh ke kika haifarmin su, kinsan dai ke kad'ai bazakiyi cikin su ki haife ba, sai da taimakona, yara kuma 'ya'yana ne dan haka zan sakeki yau basai gobe ba, ko Allah zai azurtani na huta da wannan bak'in talaucin da kika jefani tunda na aure ki, gurin aiki nawa ina kai takadduna amman haryau ba wanda suka kirani."
"Kayi hakuri Abban Aslam idan har kayi hakuri ni kaina akwai lokacin da zan rabu dakai, lokacin nakejira yazo, zan rabu dakai rabuwa ta har abada."
"Zancen banza zancen wofi, sai sanda kika gama tatseni na rasa wanda zan kama sannan kikeso na rabu dake ko?, muna fuka dabadan nasan halin yan gidan ku ba kuma yayan ki abokina ne, dasai nace ko mayya na aura."
Kafin Aysher ta bud'i baki tace wani abu taji duka ta ko ina a gaban k'aramar yarinyar ta, Aysher tana kuka Afra tana kuka, baikula suba saida yayi mata ligis kafin ya tsalleke k'afarsa yabar gidan ko kallon 'yar tashi baiyi ba, ballantana ya waiwayo yaga halin da matar tashi take ciki.
A hankali Aysher ta rarrafa taje kusa da 'yarta ta rungumo tana lallashinta, itama yarinyar tasa hannu akan mahaifiyar ta alamar tana lallashinta, abin gwanin ban tausayi.
Aysher tana yashe a tsakar gidan takasa motsawa nan da can, saboda jikin ta gaba d'aya yagama tsami ciwo yake mata, 1:00pm k'anwar ta Maryam tashigo gidan Hannun ta d'auke da Aslam wanda yataso daga school suka had'u a hanya.
Dasauri Maryam ta saki hannun Aslam ta zura da gudu, dan ganin halin da yayarta take ciki, ta k'arasa tare da kamo hanun 'yar uwar nata tana girgiza mata kai tana cewa"Aunty kardai ace haryanzu bakiyi girman daina duk ba a gurin YAYA SAMIR?, toh wallahi anyi na farko, anyi na k'arshe, yau saina fad'ama Umma da Baba dan wallahi bazaiyiwu ki zamo jaka a gurin sa ba, bayan duk hallaccin da kikayi masa a baya, aiban manta da d'an kunne da sarkarki da Gold da kika siyar kika bashi kud'in akan yaja jari ba, yace ya had'u da 'yan damfara bayan shine cikakken madanfari saboda tayaya zaka bada kud'i kace ayi maka kud'i, saboda son banza, toh yau za'ayita ta k'are dole ya rabu dake Aunty Aysher." Cikin fad'a da 6abin rai Maryam take fad'in haka kasan cewarta masifaffiya ce ta k'arshe.
Cikin sanyin ta Aysher ta d'ago kanta tace"Kiyi hakuri Maryam karki fad'a a gida, wannan abun yazamo sirri tsakanina dake, karki manta sau nawa Baba da Yaya suke zuwa sunayi masa fad'a akan dukan nan amman haryau ya kasa bari, idan kika fad'a agida raba auren za'ayi dan haka Yaya yace, nikuma banshirya rabuwa dashi ba yanzu, dan haka dan Allah kirufamin asiri, akwai lokacin da zaizo dole na rabu dashi, kid'auka wannan abin da Abban Aslam yakemin a matsayin tawa kaddaran da zan tarar a gidan aure na, taimaka ki juyemin ruwa nayi wanka, na shirya ko zanji sauk'in ciwo jikin nan Maryam."
_"Aunty Aysher bazata ta6a canja wannan sanyin halin nata ba, shiyasa take cutuwa dayawa."_
Cikin Zuciyar maryam take fad'in haka, sannu Aunty Allah kawo miki mafita, (tafad'a tare da kamo hanun yayar ta dan Zuwa band'aki). Ameen Maryam (tabata amsa)
__
*MAFARIN LAMARIN*
DAGA TASKAR
*ZAMANI WRITER'S ASSOCIATION (Z.W.A)*
©Zeetty
_GARGA'DI_
_Wannan labarin nawa da abin da ya k'unsa, duk mallakar marubuciyar ce. Saboda haka sai a guji juya, ko sarrafa wannan labarin batare da izini ba. In kunne yaji........_
_TUNATAR WA_
_Wannan labarin kagaggen labari ne, don fad'akarwa da Nisha d'antar da masu karatu. Saboda haka sai a guji yin zargi ko zaton cewa anyi wannan labari ne domin a musgunawa wani ko wasu, haka sunaye da garuruwan dake cikin wanna labari, an sane kawai don k'ayata labarin._
_GAREKU MARUBUTA_
_Ina kira a gareku, da mu gyara rubutun mu, musan abinda zamu dinga sakawa dan gyara rayuwar k'annemu da 'ya'yanmu, kar mu 6ata musu tarbiya da sakawa yara buri, abinda bazai yiwu ba a wannan zamanin mudaina rubutawa, mutuna online novels mafi akasari 'yan mata yanzu sun raja'a a kansa, dan Allah muhankalta._
```NOTE```:- *Masu karatu kuyi hak'uri bazaku samu cigaban Labarin littafin Hanyar libiya ba, saboda wani dalili mai karfi, ku gafarceni, dalilin haka nema yasa nafara sabon novel.*
*LITTATAFAN MARUBUCIYAR*
*HANGEN DALA*
*DAGA ALLAH NE*
*HANYAR LIBIYA*
*'DABI'A*
*ZUBAR HAWAYE*
*NAMIJIN DUNIYA*
```BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM.```
PAGE 1-2
Shigowa gida yayi ko sallama babu, yafara ball da wani baho daya gani a gefen tsakar gidan, cikin bala'i yafara magana"aikin banza aikin wofi, ni za'a kawoma iskanci a cikin gidan nan?, toh zan yimiki wulak'anci, Aysher ina kike, yooo gani d'an iska ko? Ina magana kina ciki kin maidani shashasha, kai uban giji kayi mana arziki ina ganin wulak'anci a gurin matar nan, bazaki fito ba saina shigo har d'akin na nakad'a miki duka, a gaban 'ya'yan naki kaza uwar son 'ya'ya.?"
Da sauri har tana cin tuntu6e ta fito, tana cewa"kayi hak'uri Abban Aslam, wallahi Afra ce take so tayi bacci, shine nake lalla6ata dan nasamu tayi bacci na k'arasa aiki na."
Doguwar tsaki ya saki, kafin yafara magana cikin kumfar baki"Kinji tsiyar ba, daga anyi miki magana sai kice 'ya'ya sai bala'in son 'ya'ya, wuce kibani guri nidai Allah kawomin ranar da zan rabu da wannan bala'in, saboda banda kud'i kin mayar dani d'an iska, shashasha ko?"
"Kayi hak'uri Abban Aslam ba haka bane, ka gafarceni idan na 6ata maka rai." Ta k'arasa fad'a tare da juyawa dan komawa d'akin ta.
Fusgota yayi kafin ya wanketa da mari, yafara magana cikin hargagi"Ehhh mana wato gani d'an iska ina magana kin tafi kin barni wato nagayawa iska ko.?"
Hanunta dafe da kuncin ta tafara magana tana hawaye tace"Kayi Hakuri Abban Aslam, kace natafi, na juya domin tafiyar, amman yanzu kace nayi maka badai-dai ba, kadaure ka sanar dani laifin dana aikata gareka kake hukunta ni, ta wannan hanyar dan Allah, auren so mukayi ni dakai, bawanda akayima dole amman kwata-kwata baifi zaman shekara d'aya mukayi cikin kwanciyar hankali ba.?"
"Hmmm tuhumata kikeyi,? Nace tuhumata kikeyi, tunda na aureki wane cigaba nasamu sam babu wani cigaba kullum sai komawa baya nakeyi, duk abokaina sun fini kud'i da arziki, nikam tabbas na auro mai farar k'afa, zama nin nan ina ake auren so? Sai dai auren kud'i, to bari kiji dakyau, ina nan nasa ayimin binciken matar aure, auren jari zanyi, 'yar alasawa, muga tsiya, shashasha kawai."
Yana gama fad'in haka yasa kai yafice dan barin gidan.
Komawa tayi da baya ta shige d'aki, zama tayi ta rafka tagumi, shin me natsarema Abban Aslam lokaci guda ya canja min?, talaucin nan bani na d'ora mana ba, lallai nice ma mai farar k'afar?, ikon Allah.
Bayan ta gama komai ta gyara gidan tsaff ta d'auko turaren tsinke mai rangwamen kud'i ta kunna, kud'in da Yayanta Nasiru ya bata shekaran jiya da taje gida dashi ta sake amfani yau dan yimusu cefane, Macaroni ta dafa da dankalin turawa, ta siyo d'ayen kifinta ta soya ta watsa a ciki.
Bayan ta gama komai ta share gidan, ga goge ko ina tsaf, tashiga wanka ta fito ta kimtsa, cikin kwalliyarta mai sauk'i, hak'ik'a AYSHER tanada kyau, koda ace batayi kwalliya ba, dubeta yanzu kamar bata ta6a haihuwar yara har guda biyu ba.
Tana zaune a falo ya shigo yana cika yana batsewa, salama yayi ciki-ciki, Aysher ta amsa tare da fad'in"Sannu da dawowa Abban Aslam."
"Yauwa sannu" ya fad'a a dake.
Tace"Me zaka farayi wanka ko cin abinci.?"
"Bazanyi wankan ba, nace bazanyi wankan ba ko dole ne, zoki mak'ureni nayi dole uwata."
"Yi hakuri barin kawo maka abinci."
(Tak'arasa fad'a tare da mik'ewa dan zuwa kawo mashi abinci)
Try ta d'auko mai d'auke da food flask da plate da cokali, ta k'araso gaban sa ta ajiye tare da bud'ewa ta zuba masa, ruwa ta d'auko a roba ta ajiye masa a gaban sa, duk yana binta da kallo saida ta gama tace"Bismillah"
Yace"Kina wani yimin abu isa-isa idan tak'amarki yau ban baki kud'in cefane ba kiyimin list, in sha Allahu zan biyaki idan nayi kud'i."
"Kayi hak'uri duk maganar baikai haka ba."
"'Daukar abincin yayi yafara ci kamar dole, daga k'arshe dai zagewa yayi, yaci yayi kat, kafin ya mik'e a 3 seater, yana satan kallon matar sa, tayi masa kyau take wani sha'awata ya lullu6eshi."
"Zan shiga ciki Abban Aslam saida safe, saika shigo."
Yace"Aikin kenan, toh banyadda ba kijira nagama kallo, har lokacin tashina yayi mushiga tare, inada buk'ata, kinsan ai dole zan buk'ace ki wannan kwalliya haka dan tsabar jarabarki ta motsa shiyasa kika yimin ita, kijira zan biyaki hakkinki, kar Allah yakamani kodan saboda haka narasa ganin dai-dai, barin gama mushige dan nasan ko kinshiga ciki ba bacci zaki iya ba, mayya kawai."
Maganar tasa tayima Aysher ciwo, amman ba yadda zatayi, komawa tayi ta zauna tana kissima abubuwa dayawa a ranta, wato yanada buk'atar ta amman shine zai juya maganar kanta, Allah kayimin agaji........
MAMAN HANAN
ZAUREN LITTATTAFAN HAUSA.
[12/23/2017, 18:37] Zeeett Zamaniwrite Group Novels: 💐💐💐💐💐
*MAFARIN LAMARIN*
DAGA TASKAR
*ZAMANI WRITER'S ASSOCIATION (Z.W.A)*
©Zeetty
PAGE 3-4
Washe gari da wani masifar yatashi, ko karyawan safe bai tsaya yayi a gidan ba.
Ita dai Aysher baiwar Allah fara gyaran gidan tayi tsaff tayima yaranta wanka ta shirya Aslam yatafi School.
Tagumi tayi tana tunanin halin mijinta da zaman su na da, da kuma na yanzu, tashare hawayen dake zubowa daga fuskar ta, hannu ta d'aga tana rokon Allah ya kawo mata mafita, amman cikin ranta ta kuduri wani abu a cikin sa.
12:00pm yashigo gidan da sallama kafin ya d'ora daga inda ya tsaya fad'i yake"Ke matsiyaciya fito, za'ayita ta k'are nagaji da wannan bak'in talaucin naki, daman tunda naga kinnace saini abin yabani mamaki, ashe kinsan kalarki wato mai farar k'afa ne ke, Mamana da kanta yau tace na hak'ura da wannan auren da kullum babu cigaba sai ci baya."
Cikin K'walla Aysher ta fara magana"Kayi hakuri Abba Aslam, karka rabu dani a wannan yanayin, koma zaka sakeni ina rok'onka Alfarma kabarni nayi zaman 'ya'yana dan Allah."
"Mtswwww kinji tsiyar taki ba?, ana magana sai ki fara cewa yaran ki, toh ke kika haifarmin su, kinsan dai ke kad'ai bazakiyi cikin su ki haife ba, sai da taimakona, yara kuma 'ya'yana ne dan haka zan sakeki yau basai gobe ba, ko Allah zai azurtani na huta da wannan bak'in talaucin da kika jefani tunda na aure ki, gurin aiki nawa ina kai takadduna amman haryau ba wanda suka kirani."
"Kayi hakuri Abban Aslam idan har kayi hakuri ni kaina akwai lokacin da zan rabu dakai, lokacin nakejira yazo, zan rabu dakai rabuwa ta har abada."
"Zancen banza zancen wofi, sai sanda kika gama tatseni na rasa wanda zan kama sannan kikeso na rabu dake ko?, muna fuka dabadan nasan halin yan gidan ku ba kuma yayan ki abokina ne, dasai nace ko mayya na aura."
Kafin Aysher ta bud'i baki tace wani abu taji duka ta ko ina a gaban k'aramar yarinyar ta, Aysher tana kuka Afra tana kuka, baikula suba saida yayi mata ligis kafin ya tsalleke k'afarsa yabar gidan ko kallon 'yar tashi baiyi ba, ballantana ya waiwayo yaga halin da matar tashi take ciki.
A hankali Aysher ta rarrafa taje kusa da 'yarta ta rungumo tana lallashinta, itama yarinyar tasa hannu akan mahaifiyar ta alamar tana lallashinta, abin gwanin ban tausayi.
Aysher tana yashe a tsakar gidan takasa motsawa nan da can, saboda jikin ta gaba d'aya yagama tsami ciwo yake mata, 1:00pm k'anwar ta Maryam tashigo gidan Hannun ta d'auke da Aslam wanda yataso daga school suka had'u a hanya.
Dasauri Maryam ta saki hannun Aslam ta zura da gudu, dan ganin halin da yayarta take ciki, ta k'arasa tare da kamo hanun 'yar uwar nata tana girgiza mata kai tana cewa"Aunty kardai ace haryanzu bakiyi girman daina duk ba a gurin YAYA SAMIR?, toh wallahi anyi na farko, anyi na k'arshe, yau saina fad'ama Umma da Baba dan wallahi bazaiyiwu ki zamo jaka a gurin sa ba, bayan duk hallaccin da kikayi masa a baya, aiban manta da d'an kunne da sarkarki da Gold da kika siyar kika bashi kud'in akan yaja jari ba, yace ya had'u da 'yan damfara bayan shine cikakken madanfari saboda tayaya zaka bada kud'i kace ayi maka kud'i, saboda son banza, toh yau za'ayita ta k'are dole ya rabu dake Aunty Aysher." Cikin fad'a da 6abin rai Maryam take fad'in haka kasan cewarta masifaffiya ce ta k'arshe.
Cikin sanyin ta Aysher ta d'ago kanta tace"Kiyi hakuri Maryam karki fad'a a gida, wannan abun yazamo sirri tsakanina dake, karki manta sau nawa Baba da Yaya suke zuwa sunayi masa fad'a akan dukan nan amman haryau ya kasa bari, idan kika fad'a agida raba auren za'ayi dan haka Yaya yace, nikuma banshirya rabuwa dashi ba yanzu, dan haka dan Allah kirufamin asiri, akwai lokacin da zaizo dole na rabu dashi, kid'auka wannan abin da Abban Aslam yakemin a matsayin tawa kaddaran da zan tarar a gidan aure na, taimaka ki juyemin ruwa nayi wanka, na shirya ko zanji sauk'in ciwo jikin nan Maryam."
_"Aunty Aysher bazata ta6a canja wannan sanyin halin nata ba, shiyasa take cutuwa dayawa."_
Cikin Zuciyar maryam take fad'in haka, sannu Aunty Allah kawo miki mafita, (tafad'a tare da kamo hanun yayar ta dan Zuwa band'aki). Ameen Maryam (tabata amsa)