Sashe 9
Kashe Fitila Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan fitar Gimbi Maamu ko bude abincin bata yi ba ta dauka ta kai kitchen. Lokacin Rumana bata farka daga baccin yunwar da take yi ba. Tana shiga ta ga Laminde ta bude wani flask da shinkafa a ciki tana shirin zubarwa. Abincin Awaisu ne na office ko rabi bai ci ba. Maamu ta rasa yadda zata kwatantawa Laminde ta bata abincin. Can dai ta nuna abincin tace Rumana.
"Rumana zaki bawa?"
Maamu tace eh. Laminde ta mika mata flask din. Karba tayi ta koma daki ta tashi Rumana. Duk da tana so haka ta bar mata. Ita kuwa tana ganin abincin haka ta soma ci babu wanke hannu bare kuskure baki. Maamu na gefe sai hawaye take sharewa batare da ta bari Rumanan ta gani ba. Yarinyar da gidansu ba'a san yunwa ba itace yau ta bawa ragowa. Da Harisu zai ganta yanzu bata san inda zata saka kanta ba. Rumana ta cinye abincin tas ta sude flask din kamar almajiri yaje bara an bashi lomar tuwo uku.
Tana gamawa sai amai tun a dakin ta fara Maamu ta kama ta zuwa bandaki. Tana yi tana kuka domin tun tana fitar da abinci sai da ya koma yawu kawai take zubarwa idan ya yunkuro. Haka Maamu ta gyara wurin tace Rumana ta kwanta. Babu bata lokaci wani baccin ya dauketa baki a bude. A daren Maamu tayi kuka har kanta ya rinka ciwo. A kusa da Rumana tayi bacci.
*****
Bayan asuba Gimbi ta shiga dakin ta tarar da Maamu akan abin sallah ita kuma Rumana tana shafa mai. A ladabce ta gaishe da Maamu kamar bata yi musu komai ba.
"Rumana jiya kika bar kanwarki ta kwana ita kadai. Ko kinfi son kwana a nan ne?"
Kai kawai ta gyada don ta fara tsoron Gimbi yanzu.
Murmushi tayi a ranta tace tafi nono fari.
"To ai babu komai hakan ma yafi. Zaki rinka debewa Maamu kewa"
Daga haka ta fice zuciyarta cike da nishadi. Yanzu zata gyarawa Daula dakin yadda ta tsara tun farko.
Kitchen ta wuce ta samu Laminde har ta gama farfesun kayan cikin da ta sakata. Ta zubawa mijinta da yaranta sannan ta dauko langar Maamu ta soma zubawa.
Laminde tana goge gefen gas cooker din ta saki tsumman tana kallon ikon Allah. Hanji ne Gimbi take ta za6ewa tana zubawa ya kusa rabin langar. Jikinsa duk kitse yayi wani narai narai babu kyaun gani.
Kasa hakuri Laminde tayi "Hajiya nace ko kin manta wannan langar kince ta Maamu ce"
Fuska a hade saboda bata son bada kofar tsawaita zancen tace ban fahimceki ba.
"Na ga kina ta zuba hanji ne a ciki."
"Hanjin ba nama bane? Kinga ki kiyayeni da shisshigi wallahi. Kin saka min ido ni da gidana sai nayi miki bayanin abin da nake yi. To binciken likitoci ya tabbatar da cewa cin dafaffen hanji yana matukar taimakawa tsofaffi da kara musu lafiya"
Awaisu yana daga falo suna jiran ta kawo breakfast shi da yara ya jiyo muryarta tana fada. Kitchen din ya shiga "Me ya faru kuma kike fada da safen nan?"
Rufe langar tayi tace "kyaleni da ita, ina jin ta fara gajiya ne da aikin"
Laminde sai faman bada hakuri take yi.
Ya so jin abin da ya hadasu sai dai shima bai ga fuskar tambaya ba. Yana kallo ta dauki langar tare da bread wanda ta yanka gida hudu ta dauki bari daya sai tea a kofi ta kaiwa Maamu da kanta.
Bayan fitarta Rumana ta gama shirin makaranta. Duk da bata da kwari sosai amma a ganinta fitar zata fiye mata. Kafin ta fita Maamu ta mika mata dari biyu cikin kudin da Harisu ya bata wanda a lokacin tayi ta cewa ya barshi. Ashe zai musu rana.
"Ki sayi abinci a makaranta kici kinji ko. Zan yiwa baban naku magana sai ya rinka baki kudi da safe ko kuma a baki abinci kema"
Rumana tayi mata godiya ta fito falo. Suna zaune dukkansu suna cin abinci suna wasa da yaransu. Awaisu ta gaisar yaran suna tambayarta ina taje jiya basu ganta ba. Murmushi kawai take yi.
"Zauna ki hada tea kuyi sauri kada ku makara" inji Awaisu.
Gimbi ta dan juya ido "har ka manta na fada maka za ta rinka tafiya da kanta. Rumana shiga wurin Laminde kiyi brealfast kinji."
"Me yasa bazata ci a nan ba?" Awaisu ya tambayeta harda dan daga murya kamar zaiyi fadan gaske.
"Bana so Laminde ta ga kamar muna wareta ne. Shiyasa nace su ci tare. Banyi laifi ba ko?" Ta rausayar da kai tana masa fari.
Shiru yayi yana ta auna maganar. Har ransa baiji dadi ba kuma fada yaso yi sai dai yana bude baki yaji bazai iya ba.
"Bakiyi komai ba. Kuyi sauri bana so kowa ya makara"
Daga haka kowa ya karasa cin abincinsa suka tashi zasu tafi. Rumana itama ta fito bayan ta gama cin nata hanjin da bread. Sai tea wanda tana sane ta tsula masa ruwa don ya kara yawa ko zata dade bata ji yunwa ba.
Suna fita itama ta fito ta tafi. Yau bata hadu da su Yusra ba sai a aji. Da break ta hada da kudin da Maamu ta bata da na wurin Umman Yusra ta sayi fanke na dari da meat pie 'yan hamsin guda hudu.
Yusra ta rinka kallonta, ina zata kai wannan abincin ita kadai. Meatpie daya taci da fanke biyu ta saka sauran a jaka zata kaiwa Maamu.
*****
Da farko Maamu kin cin abincin tayi sai daga baya da yunwa ta cigaba da cinta ta dauki kofin tea din ta shanye. Ta bude langa sai ga hanji da romon ya daskare ya hade jikinsa. Idan jiya tana kokonto yau ta tabbatar Gimbi da gaske wulakanta ta take sonyi. Tasan karshenta gidan ne bata so ta zauna musu. To amma komai wahala zata jure. Ta cinye rayuwarta a alfarmar gidan Harisu da Baaba Hure. Yanzu kuwa da kunya ta koma. Idan ta koma din ma ace nata dan ya kasa riketa. Shawara ta yankewa zuciyarta idan ya dawo zata ji ta bakinsa game da wannan gashin kuman da aka fara yi musu. Ko aikatau tazo yi a gidan a tunaninta bata cancanci a wulakanta ta ba. Sai yanzu take kara godewa Allah da aka ki yarda su zo da Baaba. Da bata san da idon da zata kalleta ba don kunya. Haka nan ta rinka cin hanjin tana hawaye.
*****
Da rana Laminde bata kawo abinci ba zuwa da tayi suyi hira. Duk da ba komai take fahimta a zancen ba amma tana jindadin yadda take mutumtata.
Rumana tana dawowa ta dauko abincin jakarta suka ci ita da Maamu. Wannan abu ya tsayawa Maamu a rai sosai. Bakinciki yasa ko fanken hannunta bata gama ci ba ta ajiye. Sai karfe shida su Gimbi suka dawo. Yau ma yaran basu je islamiyya ba. A lokacin ta bude store ta mikowa Laminde semovita tace ta dora tuwo.
Cikin sauri tayi ta gama domin itama ta horu da yunwa. Gimbi da kanta ta raba abincin ta zubawa Maamu tuwo da miya a hade. Rumana itama a plate aka hada mata ta ajiye a kitchen.
A haka suka kwashi sati biyu tana musu kisan mummuke sannan tana auna karfin mulkinta akan Awaisu. Da ta tabbatar aiki yayi kyau ne ta kira Anti Bebi akan tana son na mallaka domin tun a haka tana ganin yadda baya iya yi mata musu ko kadan.12*KASHE FITILA*💡13
*Batul Mamman*💖
Anti Bebi ta rinka yiwa Gimbi dariya
" 'yar gari waye ya fada miki haka nan mata suke zaune, duk wadda tace miki bata dan lekawa wurin neman taimako domin samun zaman lafiya a gidan aurenta karya take yi. Abin da naso uwarki ta fahimta kenan sai ta rinka gayamin maganganu"
Gimbi na jin haka ta daure fuska
"nifa kinga abin da yake hadani dake kenan, akan zagin Mama fa sai naci..." shiru tayi sanin cewa yanzu sirrinta a tafin hannun Anti Bebin yake.
"Karasa mana mara mutumci. Ni zaki zaga Gimbiya. Lallai wuyanki yayi kauri. Yadda na kaiki wurin Wangesi akan mijinki kinsan ba karamin aikina bane na koma akanki ko"
Gaban Gimbi ya fadi a tsorace ta soma bata hakuri. Sai dai tana cikin magana taji ta katse kiran. Da ta sake kira kuwa a kashe taji ta. Yanzu ko da wuka a wuyanta bazata iya kwatanta hanyar zuwa wurin Wangesi na tsangaya ba. Kuma ba karamin aikin Anti Bebi bane taje tasa ayi mata wani mugun abun. A da bata gama sanin wacece ita ba sosai sai yanzu da suke tare. Ban da mijinta da ta shanye hatta mahaifiyarsu wato kakarsu Gimbi bata taba yi mata musu. Duk yadda tace haka ake bawa su Mama umarni kuma dole suyi idan ba haka ba ta nuna musu fushinta sosai. Kuma bata taba yi mata fadan abubuwan da take yi da aure aure ba.
A ranar ta bita gida tayi ta bata hakuri daga karshe suka daidaita.
*****
Watanni biyu kenan da shigar su Maamu cikin kunci a gidan Awaisu. 'Yar hirar da yake zuwa suyi ma sai yayi kwana biyu bata sa shi a ido ba. Ranar da ya zo kuma zai sake yayi ta bata labarai batare da kula ko tambayarta idan tana da damuwa ba. Ya riga ya sakarwa Gimbi komai da ya shafi Maamu da Rumana. Hatta kudin makaranta ko abinci da ta nemi a rinka bawa Rumana cewa yayi zai fadawa Gimbi. Sau tari ya kan tsinci kansa da tunani akan rashin dacewar abin da yake yi mata. Amma ko a bayan idon Gimbi bai taba kuskuren canjawa zuwa Awaisun Harisu da aka sani ba a gaban Maamu.
"Rumana zaki bawa?"
Maamu tace eh. Laminde ta mika mata flask din. Karba tayi ta koma daki ta tashi Rumana. Duk da tana so haka ta bar mata. Ita kuwa tana ganin abincin haka ta soma ci babu wanke hannu bare kuskure baki. Maamu na gefe sai hawaye take sharewa batare da ta bari Rumanan ta gani ba. Yarinyar da gidansu ba'a san yunwa ba itace yau ta bawa ragowa. Da Harisu zai ganta yanzu bata san inda zata saka kanta ba. Rumana ta cinye abincin tas ta sude flask din kamar almajiri yaje bara an bashi lomar tuwo uku.
Tana gamawa sai amai tun a dakin ta fara Maamu ta kama ta zuwa bandaki. Tana yi tana kuka domin tun tana fitar da abinci sai da ya koma yawu kawai take zubarwa idan ya yunkuro. Haka Maamu ta gyara wurin tace Rumana ta kwanta. Babu bata lokaci wani baccin ya dauketa baki a bude. A daren Maamu tayi kuka har kanta ya rinka ciwo. A kusa da Rumana tayi bacci.
*****
Bayan asuba Gimbi ta shiga dakin ta tarar da Maamu akan abin sallah ita kuma Rumana tana shafa mai. A ladabce ta gaishe da Maamu kamar bata yi musu komai ba.
"Rumana jiya kika bar kanwarki ta kwana ita kadai. Ko kinfi son kwana a nan ne?"
Kai kawai ta gyada don ta fara tsoron Gimbi yanzu.
Murmushi tayi a ranta tace tafi nono fari.
"To ai babu komai hakan ma yafi. Zaki rinka debewa Maamu kewa"
Daga haka ta fice zuciyarta cike da nishadi. Yanzu zata gyarawa Daula dakin yadda ta tsara tun farko.
Kitchen ta wuce ta samu Laminde har ta gama farfesun kayan cikin da ta sakata. Ta zubawa mijinta da yaranta sannan ta dauko langar Maamu ta soma zubawa.
Laminde tana goge gefen gas cooker din ta saki tsumman tana kallon ikon Allah. Hanji ne Gimbi take ta za6ewa tana zubawa ya kusa rabin langar. Jikinsa duk kitse yayi wani narai narai babu kyaun gani.
Kasa hakuri Laminde tayi "Hajiya nace ko kin manta wannan langar kince ta Maamu ce"
Fuska a hade saboda bata son bada kofar tsawaita zancen tace ban fahimceki ba.
"Na ga kina ta zuba hanji ne a ciki."
"Hanjin ba nama bane? Kinga ki kiyayeni da shisshigi wallahi. Kin saka min ido ni da gidana sai nayi miki bayanin abin da nake yi. To binciken likitoci ya tabbatar da cewa cin dafaffen hanji yana matukar taimakawa tsofaffi da kara musu lafiya"
Awaisu yana daga falo suna jiran ta kawo breakfast shi da yara ya jiyo muryarta tana fada. Kitchen din ya shiga "Me ya faru kuma kike fada da safen nan?"
Rufe langar tayi tace "kyaleni da ita, ina jin ta fara gajiya ne da aikin"
Laminde sai faman bada hakuri take yi.
Ya so jin abin da ya hadasu sai dai shima bai ga fuskar tambaya ba. Yana kallo ta dauki langar tare da bread wanda ta yanka gida hudu ta dauki bari daya sai tea a kofi ta kaiwa Maamu da kanta.
Bayan fitarta Rumana ta gama shirin makaranta. Duk da bata da kwari sosai amma a ganinta fitar zata fiye mata. Kafin ta fita Maamu ta mika mata dari biyu cikin kudin da Harisu ya bata wanda a lokacin tayi ta cewa ya barshi. Ashe zai musu rana.
"Ki sayi abinci a makaranta kici kinji ko. Zan yiwa baban naku magana sai ya rinka baki kudi da safe ko kuma a baki abinci kema"
Rumana tayi mata godiya ta fito falo. Suna zaune dukkansu suna cin abinci suna wasa da yaransu. Awaisu ta gaisar yaran suna tambayarta ina taje jiya basu ganta ba. Murmushi kawai take yi.
"Zauna ki hada tea kuyi sauri kada ku makara" inji Awaisu.
Gimbi ta dan juya ido "har ka manta na fada maka za ta rinka tafiya da kanta. Rumana shiga wurin Laminde kiyi brealfast kinji."
"Me yasa bazata ci a nan ba?" Awaisu ya tambayeta harda dan daga murya kamar zaiyi fadan gaske.
"Bana so Laminde ta ga kamar muna wareta ne. Shiyasa nace su ci tare. Banyi laifi ba ko?" Ta rausayar da kai tana masa fari.
Shiru yayi yana ta auna maganar. Har ransa baiji dadi ba kuma fada yaso yi sai dai yana bude baki yaji bazai iya ba.
"Bakiyi komai ba. Kuyi sauri bana so kowa ya makara"
Daga haka kowa ya karasa cin abincinsa suka tashi zasu tafi. Rumana itama ta fito bayan ta gama cin nata hanjin da bread. Sai tea wanda tana sane ta tsula masa ruwa don ya kara yawa ko zata dade bata ji yunwa ba.
Suna fita itama ta fito ta tafi. Yau bata hadu da su Yusra ba sai a aji. Da break ta hada da kudin da Maamu ta bata da na wurin Umman Yusra ta sayi fanke na dari da meat pie 'yan hamsin guda hudu.
Yusra ta rinka kallonta, ina zata kai wannan abincin ita kadai. Meatpie daya taci da fanke biyu ta saka sauran a jaka zata kaiwa Maamu.
*****
Da farko Maamu kin cin abincin tayi sai daga baya da yunwa ta cigaba da cinta ta dauki kofin tea din ta shanye. Ta bude langa sai ga hanji da romon ya daskare ya hade jikinsa. Idan jiya tana kokonto yau ta tabbatar Gimbi da gaske wulakanta ta take sonyi. Tasan karshenta gidan ne bata so ta zauna musu. To amma komai wahala zata jure. Ta cinye rayuwarta a alfarmar gidan Harisu da Baaba Hure. Yanzu kuwa da kunya ta koma. Idan ta koma din ma ace nata dan ya kasa riketa. Shawara ta yankewa zuciyarta idan ya dawo zata ji ta bakinsa game da wannan gashin kuman da aka fara yi musu. Ko aikatau tazo yi a gidan a tunaninta bata cancanci a wulakanta ta ba. Sai yanzu take kara godewa Allah da aka ki yarda su zo da Baaba. Da bata san da idon da zata kalleta ba don kunya. Haka nan ta rinka cin hanjin tana hawaye.
*****
Da rana Laminde bata kawo abinci ba zuwa da tayi suyi hira. Duk da ba komai take fahimta a zancen ba amma tana jindadin yadda take mutumtata.
Rumana tana dawowa ta dauko abincin jakarta suka ci ita da Maamu. Wannan abu ya tsayawa Maamu a rai sosai. Bakinciki yasa ko fanken hannunta bata gama ci ba ta ajiye. Sai karfe shida su Gimbi suka dawo. Yau ma yaran basu je islamiyya ba. A lokacin ta bude store ta mikowa Laminde semovita tace ta dora tuwo.
Cikin sauri tayi ta gama domin itama ta horu da yunwa. Gimbi da kanta ta raba abincin ta zubawa Maamu tuwo da miya a hade. Rumana itama a plate aka hada mata ta ajiye a kitchen.
A haka suka kwashi sati biyu tana musu kisan mummuke sannan tana auna karfin mulkinta akan Awaisu. Da ta tabbatar aiki yayi kyau ne ta kira Anti Bebi akan tana son na mallaka domin tun a haka tana ganin yadda baya iya yi mata musu ko kadan.12*KASHE FITILA*💡13
*Batul Mamman*💖
Anti Bebi ta rinka yiwa Gimbi dariya
" 'yar gari waye ya fada miki haka nan mata suke zaune, duk wadda tace miki bata dan lekawa wurin neman taimako domin samun zaman lafiya a gidan aurenta karya take yi. Abin da naso uwarki ta fahimta kenan sai ta rinka gayamin maganganu"
Gimbi na jin haka ta daure fuska
"nifa kinga abin da yake hadani dake kenan, akan zagin Mama fa sai naci..." shiru tayi sanin cewa yanzu sirrinta a tafin hannun Anti Bebin yake.
"Karasa mana mara mutumci. Ni zaki zaga Gimbiya. Lallai wuyanki yayi kauri. Yadda na kaiki wurin Wangesi akan mijinki kinsan ba karamin aikina bane na koma akanki ko"
Gaban Gimbi ya fadi a tsorace ta soma bata hakuri. Sai dai tana cikin magana taji ta katse kiran. Da ta sake kira kuwa a kashe taji ta. Yanzu ko da wuka a wuyanta bazata iya kwatanta hanyar zuwa wurin Wangesi na tsangaya ba. Kuma ba karamin aikin Anti Bebi bane taje tasa ayi mata wani mugun abun. A da bata gama sanin wacece ita ba sosai sai yanzu da suke tare. Ban da mijinta da ta shanye hatta mahaifiyarsu wato kakarsu Gimbi bata taba yi mata musu. Duk yadda tace haka ake bawa su Mama umarni kuma dole suyi idan ba haka ba ta nuna musu fushinta sosai. Kuma bata taba yi mata fadan abubuwan da take yi da aure aure ba.
A ranar ta bita gida tayi ta bata hakuri daga karshe suka daidaita.
*****
Watanni biyu kenan da shigar su Maamu cikin kunci a gidan Awaisu. 'Yar hirar da yake zuwa suyi ma sai yayi kwana biyu bata sa shi a ido ba. Ranar da ya zo kuma zai sake yayi ta bata labarai batare da kula ko tambayarta idan tana da damuwa ba. Ya riga ya sakarwa Gimbi komai da ya shafi Maamu da Rumana. Hatta kudin makaranta ko abinci da ta nemi a rinka bawa Rumana cewa yayi zai fadawa Gimbi. Sau tari ya kan tsinci kansa da tunani akan rashin dacewar abin da yake yi mata. Amma ko a bayan idon Gimbi bai taba kuskuren canjawa zuwa Awaisun Harisu da aka sani ba a gaban Maamu.