Sashe 15
Kashe Fitila Book 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Kuka ta saka saboda tsabar bata damu da Maamu ba shaf ta manta da batun abincin. Na safe ma da tayi saboda ta burge mijinta ne yaji dadi.
"Wallahi Yaya Harisu ina ta aiki ne na sha'afa."
Ummukulsum tace "wannan ba magana bace Gimbi. Akwai wani aiki da zai sha kanki sama da nata da take asibiti? Yanzu ga jinya ga yunwa daga ita har Rumana"
Ido sharbe da hawaye ta rinka basu hakuri. A ranta kuwa duk tsine musu take yi suna neman jaza mata masifa wurin miji.
Baaba Hure tamkar ta cinyeta da fada. Tana yi Awaisu yana yi don ya kule karshe. Harisu ne ya rinka basu hakuri. Su Tikeke kuwa an sami abin kallo da gulma. Marasa jin hausa sosai babu damar tofawa.
Duk wani haushin Gimbi da yake ji kwanakin baya ya kasa magana tun jiya da ya ga Maamu a wannan yanayin yaji kamar an bude masa ido. A fusace yace mata taje ta dauko abincin. Wani tsoron ya sake kamata domin batayi dasu ba. Hasali ma dai babu sauran abinci a gidan. Awaisu yayi fadan da hausa ya koma saka yarensa kamar ya kai mata duka. Baaba Hure ko a jikinta saboda tun maganar da sukayi akanta take jin Gimbi ba matar kirki bace. Harisu ya ja shi gefe ya soma nasa fadan
"Wani sabon salo ne ka koya zaka zubarwa matarka mutumci a gaban baki. Dubi yadda suke kallonka. Kana tunanin wannan labarin bazai je Fika ba"
Kwalla ce take barazanar fita daga idonsa saboda tunanin yaya Maamu ta wuni. Yaje da azahar daga wurin aiki amma ita dasu Laminde babu wanda ya fada masa
"Yaya ace tun abincin safe saboda Allah"
Harisu ya dafa shi yana murmushi "to kuka zaka yi min? Awaisu 'ya'yanka hudu fa. Muje su koma suyi girkin kafin dare ya karayi a hanamu shiga"
"Bari kawai ma saya a hanya. Karfe tara suke hana shiga sai goma na safe kuma"
Tare suka koma suka shiga motocin. Wasu na motar Sunday tunda babba ce school bus sauran Awaisu ya diba. Gimbi tayi turus a waje ganin Bomoi ya shige gaba abinsa. A dakile Awaisu ya nuna mata bus din
"Idan zaki je ki koma bus din inda mata suke"
Ranta na kuna kamar tace bazata ba ta koma ta shiga tsakiyar Ammu da Hinde. Kallonta suka rinka yi ta kasa motsin kirki saboda sun matseta.
*****
Suna zuwa a kwance suka sami Rumana a gadon da yake gefen na Maamu tana bacci. A kasa kan abin sallah kuma Laminde ce take cin dafaffiyar gyada. Naira hamsin gareta shine ta siyo musu ita da Rumana suka ci suka sha ruwa. Maamu taki ci tana kwance tana hawaye. Yaushe ne danta zai waiwayeta???
Muryar Baaba Hure taji ta soma yunkurin tashi. Maman Rumana ke rike da hannunta ta karasa da ita bakin gadon saboda dishi dishi take gani. A haka ma don anyiwa idon aiki ne.
Hannu ta mika tana laluben Maamu. Ji tayi Maamu cikin muryar dake nuni da tana jin jiki tace "Baaba"
Baaba Hure sai hawaye "Maamu sannu, sannu 'yar uwa. Kai Awaisu ku zuba mata abincin nan"
Gimbi ce tayi saurin mika hannu zata karbi ledojin ya harareta sannan ya bawa Maman Rumana. Ummukulsum tace "Maamu kin rame sosai"
Riko hannun Ummukulsum din tayi "hmmm kayya Ummu jikin tsufa ne kawai, Ina yaran , yaya wajensu Auta Zakiyya"
Rumana cikin bacci taji kamar muryar babanta. Firgigit ta tashi. Abin mamaki harda Mamanta da Baaba. Wani tsalle tayi ta diro ta kankame Harisu. Shi kam kunya ma ta bashi a gaban mutane. Ta tafi zata rungume mamanta ta harareta irin abin 'yar fari. Sai kawai ta koma jikin Baaba ta kankameta.
Sun gama gaisawa Laminde da Rumana suna gefe suna cin abinci sauran suna ta hira. Basu bar asibitin ba sai shadayan dare. Nurses suna ta zuwa ana cewa su bar hayaniya.
Likita ya bukaci ganin Awaisu kafin su tafi. Fada sosai yayi masa duk da karancin shekarunsa akan shi na barin Maamu da yunwa. Duka allurai da maganinta tun azahar ba'a yi mata ba saboda bata ci abinci ba. Sannan jikinta ma yana nuni da alamun rashin kuzari saboda tana bukatar wasu sinadarai a jikinta. Shi dai sai hakuri yake bayarwa yana tunanin wai me Gimbi take yi har Maamu take zama da yunwa. A wani bangaren tuhumar kansa yake da rashin kulawa wadda bai san dalilinta ba
******
Wurin shabiyu da rabi kowa yaje ya kwanata Awaisu da Gimbi suna ta fada. Bashi hakuri take yi amma kamar tana ingiza shi. Bandaki ta shiga tayiwa Anti Bebi text ta sanar da ita. Shawara ta duk da batayi mata dadi ba haka ta karba kafin gobe ta nemi Wangesi.
Wurin Baaba taje tayi sa'a bata kwanta ba. Nan ta kwantar da kai ta bata hakuri ta roketa akan ta bawa Awaisu hakuri. A zatonta tuban gaskene tacewa Awaisu magana ta kare daga lokacin. Ya dai ce to amma juya mata baya ma yayi da suka kwanta. Kafin nan kuma yasa ta bawa Ammu da Maman Rumana dakinta saboda wancan yayi musu kadan. Ita Ummukulsum ta canji Laminde zata kwana a asibitin
Da safe matan suka tayata girki tana ta kokarin jansu a jiki.
*****
Anti Bebi karfe bakwai ta fice daga gida sai kauyen Nasarawa state inda Wangesi yake. Magunguna ya bayar da wasu layu da za'a binne a gidan. Kafin shabiyu ta dawo gida. Wanka tayi ta shirya sannan tace Alhaji yazo ya kaita dubiyar surukar Gimbi. Tun tana chan zazzabi ya kamashi a office ya dawo gida. Wani nau'in asirin akayi masa. Da ya dawo Shuhada ce ta tarbe shi ko kallonta yaki yi. Kudin mota take so ya bata itama ta bar musu gidan.
Suna fitowa daga daki Anti Bebi ta marairace wai yace Shuhada tazo suje tare saboda zaman gidan bazai mata dadi ba. Har ransa yaji dadin ta damu da yarsa amma ita Shuhada bata sonta. Dolenta ta fito suka tafi tare. Anti Bebi ta hakimce a baya Shuhada na gaba. Daga bayan mota take ta bashi umarni yana toh kamar wani bawanta. Kafin su je asibitin Shuhada har kuka tayi ganin yadda Daddynta ya koma a gaban mace.
*****
Alh Mudi da Mama suna bayan mota dreba na jansu zasu je duba Maamu. Fada sosai yayiwa Gimbi a waya bayan ya sami labarin rashin lafiyar a bakin Saminu. Su da suke garin ace basu da labari har su Harisu sun zo shi kuma Saminu yana hanya. Gimbi hakuri ta bayar kawai. Yadda bata damu da Maamu ba bata ga dalilin da sai sunzo dubiya ba.
Dakin yau a cike idan kaga Maamu da Rumana tamkar ranar sallah. Su Mama ne suka fara zuwa ana gaisawa sai ga Anti Bebi ta shigo tana fara'a. Tuni Gimbi ta rikice ganin kallon da Mama da Alhaji suke yi mata. Ita kuwa Anti Bebi don ta bawa Mama haushi ta tafi ta rungumo Gimbi
"Gimbiya yaya mai jikin. Tun shekaranjiya da kika fada min hankalina ya tashi. Jiya da kika min waya kuma baki ne dani ban samu nazo ba"
Mama ji tayi kamar ta rufe Gimbi da duka a wurin.18
"Wallahi Yaya Harisu ina ta aiki ne na sha'afa."
Ummukulsum tace "wannan ba magana bace Gimbi. Akwai wani aiki da zai sha kanki sama da nata da take asibiti? Yanzu ga jinya ga yunwa daga ita har Rumana"
Ido sharbe da hawaye ta rinka basu hakuri. A ranta kuwa duk tsine musu take yi suna neman jaza mata masifa wurin miji.
Baaba Hure tamkar ta cinyeta da fada. Tana yi Awaisu yana yi don ya kule karshe. Harisu ne ya rinka basu hakuri. Su Tikeke kuwa an sami abin kallo da gulma. Marasa jin hausa sosai babu damar tofawa.
Duk wani haushin Gimbi da yake ji kwanakin baya ya kasa magana tun jiya da ya ga Maamu a wannan yanayin yaji kamar an bude masa ido. A fusace yace mata taje ta dauko abincin. Wani tsoron ya sake kamata domin batayi dasu ba. Hasali ma dai babu sauran abinci a gidan. Awaisu yayi fadan da hausa ya koma saka yarensa kamar ya kai mata duka. Baaba Hure ko a jikinta saboda tun maganar da sukayi akanta take jin Gimbi ba matar kirki bace. Harisu ya ja shi gefe ya soma nasa fadan
"Wani sabon salo ne ka koya zaka zubarwa matarka mutumci a gaban baki. Dubi yadda suke kallonka. Kana tunanin wannan labarin bazai je Fika ba"
Kwalla ce take barazanar fita daga idonsa saboda tunanin yaya Maamu ta wuni. Yaje da azahar daga wurin aiki amma ita dasu Laminde babu wanda ya fada masa
"Yaya ace tun abincin safe saboda Allah"
Harisu ya dafa shi yana murmushi "to kuka zaka yi min? Awaisu 'ya'yanka hudu fa. Muje su koma suyi girkin kafin dare ya karayi a hanamu shiga"
"Bari kawai ma saya a hanya. Karfe tara suke hana shiga sai goma na safe kuma"
Tare suka koma suka shiga motocin. Wasu na motar Sunday tunda babba ce school bus sauran Awaisu ya diba. Gimbi tayi turus a waje ganin Bomoi ya shige gaba abinsa. A dakile Awaisu ya nuna mata bus din
"Idan zaki je ki koma bus din inda mata suke"
Ranta na kuna kamar tace bazata ba ta koma ta shiga tsakiyar Ammu da Hinde. Kallonta suka rinka yi ta kasa motsin kirki saboda sun matseta.
*****
Suna zuwa a kwance suka sami Rumana a gadon da yake gefen na Maamu tana bacci. A kasa kan abin sallah kuma Laminde ce take cin dafaffiyar gyada. Naira hamsin gareta shine ta siyo musu ita da Rumana suka ci suka sha ruwa. Maamu taki ci tana kwance tana hawaye. Yaushe ne danta zai waiwayeta???
Muryar Baaba Hure taji ta soma yunkurin tashi. Maman Rumana ke rike da hannunta ta karasa da ita bakin gadon saboda dishi dishi take gani. A haka ma don anyiwa idon aiki ne.
Hannu ta mika tana laluben Maamu. Ji tayi Maamu cikin muryar dake nuni da tana jin jiki tace "Baaba"
Baaba Hure sai hawaye "Maamu sannu, sannu 'yar uwa. Kai Awaisu ku zuba mata abincin nan"
Gimbi ce tayi saurin mika hannu zata karbi ledojin ya harareta sannan ya bawa Maman Rumana. Ummukulsum tace "Maamu kin rame sosai"
Riko hannun Ummukulsum din tayi "hmmm kayya Ummu jikin tsufa ne kawai, Ina yaran , yaya wajensu Auta Zakiyya"
Rumana cikin bacci taji kamar muryar babanta. Firgigit ta tashi. Abin mamaki harda Mamanta da Baaba. Wani tsalle tayi ta diro ta kankame Harisu. Shi kam kunya ma ta bashi a gaban mutane. Ta tafi zata rungume mamanta ta harareta irin abin 'yar fari. Sai kawai ta koma jikin Baaba ta kankameta.
Sun gama gaisawa Laminde da Rumana suna gefe suna cin abinci sauran suna ta hira. Basu bar asibitin ba sai shadayan dare. Nurses suna ta zuwa ana cewa su bar hayaniya.
Likita ya bukaci ganin Awaisu kafin su tafi. Fada sosai yayi masa duk da karancin shekarunsa akan shi na barin Maamu da yunwa. Duka allurai da maganinta tun azahar ba'a yi mata ba saboda bata ci abinci ba. Sannan jikinta ma yana nuni da alamun rashin kuzari saboda tana bukatar wasu sinadarai a jikinta. Shi dai sai hakuri yake bayarwa yana tunanin wai me Gimbi take yi har Maamu take zama da yunwa. A wani bangaren tuhumar kansa yake da rashin kulawa wadda bai san dalilinta ba
******
Wurin shabiyu da rabi kowa yaje ya kwanata Awaisu da Gimbi suna ta fada. Bashi hakuri take yi amma kamar tana ingiza shi. Bandaki ta shiga tayiwa Anti Bebi text ta sanar da ita. Shawara ta duk da batayi mata dadi ba haka ta karba kafin gobe ta nemi Wangesi.
Wurin Baaba taje tayi sa'a bata kwanta ba. Nan ta kwantar da kai ta bata hakuri ta roketa akan ta bawa Awaisu hakuri. A zatonta tuban gaskene tacewa Awaisu magana ta kare daga lokacin. Ya dai ce to amma juya mata baya ma yayi da suka kwanta. Kafin nan kuma yasa ta bawa Ammu da Maman Rumana dakinta saboda wancan yayi musu kadan. Ita Ummukulsum ta canji Laminde zata kwana a asibitin
Da safe matan suka tayata girki tana ta kokarin jansu a jiki.
*****
Anti Bebi karfe bakwai ta fice daga gida sai kauyen Nasarawa state inda Wangesi yake. Magunguna ya bayar da wasu layu da za'a binne a gidan. Kafin shabiyu ta dawo gida. Wanka tayi ta shirya sannan tace Alhaji yazo ya kaita dubiyar surukar Gimbi. Tun tana chan zazzabi ya kamashi a office ya dawo gida. Wani nau'in asirin akayi masa. Da ya dawo Shuhada ce ta tarbe shi ko kallonta yaki yi. Kudin mota take so ya bata itama ta bar musu gidan.
Suna fitowa daga daki Anti Bebi ta marairace wai yace Shuhada tazo suje tare saboda zaman gidan bazai mata dadi ba. Har ransa yaji dadin ta damu da yarsa amma ita Shuhada bata sonta. Dolenta ta fito suka tafi tare. Anti Bebi ta hakimce a baya Shuhada na gaba. Daga bayan mota take ta bashi umarni yana toh kamar wani bawanta. Kafin su je asibitin Shuhada har kuka tayi ganin yadda Daddynta ya koma a gaban mace.
*****
Alh Mudi da Mama suna bayan mota dreba na jansu zasu je duba Maamu. Fada sosai yayiwa Gimbi a waya bayan ya sami labarin rashin lafiyar a bakin Saminu. Su da suke garin ace basu da labari har su Harisu sun zo shi kuma Saminu yana hanya. Gimbi hakuri ta bayar kawai. Yadda bata damu da Maamu ba bata ga dalilin da sai sunzo dubiya ba.
Dakin yau a cike idan kaga Maamu da Rumana tamkar ranar sallah. Su Mama ne suka fara zuwa ana gaisawa sai ga Anti Bebi ta shigo tana fara'a. Tuni Gimbi ta rikice ganin kallon da Mama da Alhaji suke yi mata. Ita kuwa Anti Bebi don ta bawa Mama haushi ta tafi ta rungumo Gimbi
"Gimbiya yaya mai jikin. Tun shekaranjiya da kika fada min hankalina ya tashi. Jiya da kika min waya kuma baki ne dani ban samu nazo ba"
Mama ji tayi kamar ta rufe Gimbi da duka a wurin.18