Sashe 13
Kashe Fitila Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tafawa sukayi kamar sa'annin juna.
"So nake yi ta koma garinsu kawai ya rinka yi mata aike. Zaman tare damu ne bana so. Duk abi a sawa mutane ido. "
Sai ta dan rage murya har sai da Shuhada ta dan kara bene biyu domin taji da kyau. Dayake wurin zagaye ne basa ganin juna
"Kuma ina so ko za'a dauke hankalin Mama daga kan gidana. Ai na fada miki ranar da tazo yadda muka kare"
Anti Bebi ta hangame baki " Iyye, Gimbiya kina burgeni. Kin cika mace wadda tasan meye 'yancin rayuwa. Wasu 'yan bokon miji da danginsa suyi ta gasa su amma sai su rinka iyayi wai basa bin malamai. Kuma duk karya ne. Tunda da kanki kika nema to kisawa ranki Amina ta bar shiga sabgar da baki sakata ba"
Duk da Gimbi bata so abin ya kai haka ba amma ta fara jindadin mallaka da juya miji. Burinta karuwa yake yi domin yanzu har ogansu a banki take son ya dena mata maganar latti.
Shuhada tana tsaye zuciyarta har bugawa takeyi don tsoron matan nan. Wannan wace irin masifa ce muke daukarwa kanmu akan duniyar da bazata dore ba. Komawa tayi saman a hankali jikinta a sabule. Sai a lokacin taji tausayin mutumin da hannun Anti Bebi ya taba. Lallai ya aurowa kansa masifa.
*****
Karfe biyar da rabi Laminde ta dawo gida. Tasan dama yaran suna Islamiyya. Rashin ganin Gimbi yasa tayi tunanin ko sun kai Maamu asibiti, kwarai taji tausayinta dazu. Ku6ewa ta zauna gurzawa kafin su dawo a bata shinkafar tuwo ta dora. Tana aikin su Rumana suka shigo. Dakinsu ta wuce ta cire kayan makaranta sannan ta shiga bandaki yin alwala saboda an fara kiran magariba.
Tana budewa ta ga Maamu a kwance ko motsin kirki bata yi. Ga jikinta alamun ta sake yin gudawa a wurin. Ihun kuka Rumana ta saka tana kiran Laminde. Sai gata a guje tare da su Haris.
Duk su biyun sun rude suna zaton ta mutu ne. Suna kokarin dagata su Awaisu suka dawo ya tsaya wurin maigadi Gimbi ta shigo. Daula ce ta fada mata Maamu babu lafiya tabi bayanta. Daga bakin kofar bandakin ta toshe hancinta.
"Hmmmm warin meye wannan haka"
Tana kallo da kyar Maamu take bude ido ta jingina da jikin Rumana ita kuma Laminde tana tara ruwa a bokiti da zata dauraye mata jiki tace .
"Maamu ce babu lafiya, a kwance nan muka ganta"
Tabe baki tayi "Toh, to Allah Ya sauwake. Gyara mata jikin kafin na dawo"
Tana fita ta ga Awaisu a falo Haris yana fada masa. Da sauri ta karaso da alamun gigicewa har tana jifa da mayafi.
"Abban Haris juya mu kai Maamu asibiti bata da lafiya."
Duk yadda yake nuna rashin kulawarsa damuwa ce ta ziyarce shi ya ruga dakin a guje. Ganin Rumana ta kasa rike Maamu sosai kafin Laminde ta dauko musu nata sabulun saboda nasu saura guntu da suke amfani dashi anki basu wani. Mantawa yayi da kayan jikinsa ya shiga ciki ya dagata ya saka a bahu sannan ya soma dibar ruwan yana wanke mata jiki da hannunsa yana kiran sunanta cikin tashin hankali kada ta mutu. Da Laminde ta kawo sabulun hannun Rumana ta ja suka fita ta rufe kofar. Rumana tana son komawa Laminde ta girgiza kai.
"Ki bar Kawunki ya sami ladan mahaifiyarsa Rumana. Dauko mata kaya kafin ya gama"
"Namiji ne fa" ta fada tana yatsina fuska. Tuni Kawun nata ya fice mata a rai.
Laminde tayi murmushi "to naji bari naje ya bani nayi mata wanka"
Gimbi ce ta shigo tana tambayar yana ina suka nuna mata bandakin. Muryarsa taji yana cewa "Gimbi zo kiyi mata wanka zan chanja kaya muje asibiti"
Gabanta har faduwa yayi, wannan kazantar ta jikinta zata taba.....
Laminde tana kallonta sai ta shiga tace zata yi mata. Tsoro taji kada da gangan Gimbi ta saketa ta fadi.
Bayan anyi mata wankan ne Laminde ta kula hannunta daya ya kumbura ta wurin babban yatsanta ga dukkan alamu tayi targade. Haka ta shiryata Awaisu da Gimbi suka kaita asibiti. Suna can ya kasa zama har likita ya fito yace suna mata karin ruwa sannan anyi mata gyaran targade. Hankalinsa duk baya jikinsa sai da ya ganta. Da kyar take magana idanu duk sun fada ciki tace ya kirawo mata Harisu a waya. Gimbi jin an ambaci sunan daya makiyin nata ta kasa kunne sai dai bata jin me Awaisu yake fada da yarensu har ya gama wayar.
Juyowa yayi yace "Gobe in sha Allah Yaya Harisu zai zo da daya daga cikin matansa da Baaba Hure. Ina tsammani zasu taho da kanin Maamu ma. Ki kira Laminde a gyara musu dakin baki kafin mu koma gida"
Kirjinta ne ya buga, mutanen da ta raina zasu cika mata gida.16*KASHE FITILA*💡17
*Batul Mamman*💖
Awaisu bai lura da yadda Gimbi ta chanja da wuri ba daga jin maganar zuwan su Harisu ya mika mata mukullin mota.
"Kije gida ki taho muku da kayan bukata na kwana. Idan kin dawo sai na tafi da motar"
Zaro idanu tayi tana neman amsar da zata bashi domin gujewa kwana da Maamu. Itama Maamu da ta gane me ya fada murya can kasa saboda ciwo tace masa ya tafi da matarsa a kawo mata Laminde ko Rumana. Da ta ga zaiyi gardama tace saboda yara ne. A ranta kuwa cewa take gara ta kwana ita kadai da a barta da Gimbi.
*****
Harisu dakin Baaba yaje ya fada mata Maamu babu lafiya. Hankalinta kuwa ya tashi tace to yaje ya sanarwa 'yan uwanta. Har zai fita ta sake kiransa.
"Dangin mahaifin Awaisu ma ya kamata ka fada musu. Ai kana jin yadda suke yada mana magana wai ya tare a jikinmu baya musu komai"
Harisu ya sha kunu "haba Baaba har yaushe zaki bari zancensu ya dameki. Allah Yana gani yadda duk zuwansa garin nan sai yaje kuma yayi musu alheri. Neman rigima ne kawai"
"Duk da haka kaje ka fada musu ko zasu tura wani yaje dubiya".
"Har na fadawa Awaisun kila muje da kanin Maamu ko wani dai cikinsu. Mu da zamu je dubiya kada kuma a dorawa iyalinsa wahala"
Baaba Hure tayi wani murmushi wanda ita kadai ta san ma'anarsa.
"Baka saba yi min musu ba Harisu. Nace ka fada musu yadda zasu tura wakilinsu dubiya. 'Yan uwanka ma zan sa a kirasu a waya ko mutum biyu a samu. Cikin matanka ka dauki babar Rumana saboda ta gano 'yarta tunda ka hana a kawota hutu. Sauran suma a hankali sai kaje dasu tare ko daya bayan daya"
Harisu kasa motsawa yayi jin wannan hadi na Baaba. Duk girman gidan Awaisu idan sukayi yawa zasu takura musu ne. Ga mara lafiya kuma ga baki da wanne zasu ji.
"Yaya kaki tafiya ne?"
Takalmansa ya saka yayi waje. Ita kuwa Baaba Hure ta gyara kwanciyarta tana jira ya dawo ya kira mata Awaisu ta ji yaya jikin Maamu. Ba komai yasa take son tarawa Gimbi jama'a ba sai bakar maganar da suka yi mata ita da Anti Bebi a rashin sanin bahaushiya ce. So take ta tabbatar Gimbi bata son dangin Awaisu da gaske ne ko kuwa dai 'yar tsama ce irin ta mata da dangin mijinta.
*****
Gidansu Maamu ya fara zuwa inda duka yayyenta maza da kanne suke tare da iyalansu. Bangaren wani cikin 'yan uwan yaje suka gaisa ya sanar dasu abin da ke faruwa. Nan da nan 'yan uwa suka taru ana jajantawa sannan suka ce zasuyi shawara wanda zaije a madadinsu.
Harisu yana fita Hajja Jume matar babban wan Maamu wanda ya dade da rasuwa ta dogaro sandarta ta taho.
"Yanzu labari yazo min za'a tafi wurin Safara'u dubiya ko"
Bashar wanda yake matsayin babba yanzu ya hade rai yana hararar Atika jikar Hajja uwar hada gurmi.
"Tikeke akan gulma zanyi maganinki"
Hajja ta daga sanda tana fada "wanda ya fasa Bashar, nace wanda ya fasa. Yarinya duk kun takura mata kamar ita kadai ce jika. Duk abinku a nan gidan zata zauna. Bani da kowa a gabana sai ita. Tunda tazo ku da iyalanku kun hade mata kai kamar ka jininku ba"
Tikeke ta sunkuyar da kai ita a dole a bar tausayi ce "Hajja babu komai dama na fada miki ne kada a gama rabon waye zaije Abuja gidan Kawu Awaisu a barmu a nan"
Hadi yayi caraf yace "kada ma kusa rai, ni da Yaya Bashar zamu je. Ai ba gayya za'ayi musu ba"
"Wallahi baku isa ba Hadi. Ni zaku nunawa wariya don nawa mijin ya rasu. To ni da Tikeke kamar munje mun gama. Idan da kara ni ya kamata na fadi masu zuwa tunda yaron nan dana ne. Malam da Safa'ra'u ciki daya suka fito ba kamar wasu 'yan uba ba"
Hayaniya ce ta kaure sosai a tsakaninsu karshe aka tsaya akan za'a tafi da Tikeke, Kawu Bashar da matar Hadi. Idan basuyi haka ba tijarar Hajja bata tsallake kowa. Ba karamin aikinta bane ma tasa danta baban Tikeke ya kaisu tunda dreba ne.
****
Kasuwa Harisu ya koma can wurin masu gwanjo ya hadu da Bomai kanin baban Awaisu. Dattijo ne rigimamme na ajin karshe. Yana cikin masu yiwa Harisu habaici wai sun shanye Awaisu baya bi ta kansu. Bayan jarin gwanjon ma shine ya bashi.
"Alh Harisu kenan, yau an leko mu"
"Kawu Bomai yaya kasuwa?"
Kan benci ya zauna yana zukar sigari kafa daya kan daya.
"Gata nan muna fama. Yaya akayi ne?"
Kamar yadda ya sanar da 'yan uwan Maamu haka ya fadawa Bomai. Wani tsalle ya daka ya tashi dama shi ba jiki ba sai tsawo.
"Maamu tamu ce babu lafiya? Kace ban ga ta zama ba. Kayi kyan kai sosai da ka fada min. Asubar fari zanzo nan gidan naka mu tafi"
"Sai wuraren karfe tara zamu tafi. Nace su sauran zaka sanar dasu ko naje na fada musu. Awaisu yace jikin da sauki dai"
Matsowa yayi daf da Harisu "Tunda na sani ka bar maganar kawai ni zan sanar dasu."
"So nake yi ta koma garinsu kawai ya rinka yi mata aike. Zaman tare damu ne bana so. Duk abi a sawa mutane ido. "
Sai ta dan rage murya har sai da Shuhada ta dan kara bene biyu domin taji da kyau. Dayake wurin zagaye ne basa ganin juna
"Kuma ina so ko za'a dauke hankalin Mama daga kan gidana. Ai na fada miki ranar da tazo yadda muka kare"
Anti Bebi ta hangame baki " Iyye, Gimbiya kina burgeni. Kin cika mace wadda tasan meye 'yancin rayuwa. Wasu 'yan bokon miji da danginsa suyi ta gasa su amma sai su rinka iyayi wai basa bin malamai. Kuma duk karya ne. Tunda da kanki kika nema to kisawa ranki Amina ta bar shiga sabgar da baki sakata ba"
Duk da Gimbi bata so abin ya kai haka ba amma ta fara jindadin mallaka da juya miji. Burinta karuwa yake yi domin yanzu har ogansu a banki take son ya dena mata maganar latti.
Shuhada tana tsaye zuciyarta har bugawa takeyi don tsoron matan nan. Wannan wace irin masifa ce muke daukarwa kanmu akan duniyar da bazata dore ba. Komawa tayi saman a hankali jikinta a sabule. Sai a lokacin taji tausayin mutumin da hannun Anti Bebi ya taba. Lallai ya aurowa kansa masifa.
*****
Karfe biyar da rabi Laminde ta dawo gida. Tasan dama yaran suna Islamiyya. Rashin ganin Gimbi yasa tayi tunanin ko sun kai Maamu asibiti, kwarai taji tausayinta dazu. Ku6ewa ta zauna gurzawa kafin su dawo a bata shinkafar tuwo ta dora. Tana aikin su Rumana suka shigo. Dakinsu ta wuce ta cire kayan makaranta sannan ta shiga bandaki yin alwala saboda an fara kiran magariba.
Tana budewa ta ga Maamu a kwance ko motsin kirki bata yi. Ga jikinta alamun ta sake yin gudawa a wurin. Ihun kuka Rumana ta saka tana kiran Laminde. Sai gata a guje tare da su Haris.
Duk su biyun sun rude suna zaton ta mutu ne. Suna kokarin dagata su Awaisu suka dawo ya tsaya wurin maigadi Gimbi ta shigo. Daula ce ta fada mata Maamu babu lafiya tabi bayanta. Daga bakin kofar bandakin ta toshe hancinta.
"Hmmmm warin meye wannan haka"
Tana kallo da kyar Maamu take bude ido ta jingina da jikin Rumana ita kuma Laminde tana tara ruwa a bokiti da zata dauraye mata jiki tace .
"Maamu ce babu lafiya, a kwance nan muka ganta"
Tabe baki tayi "Toh, to Allah Ya sauwake. Gyara mata jikin kafin na dawo"
Tana fita ta ga Awaisu a falo Haris yana fada masa. Da sauri ta karaso da alamun gigicewa har tana jifa da mayafi.
"Abban Haris juya mu kai Maamu asibiti bata da lafiya."
Duk yadda yake nuna rashin kulawarsa damuwa ce ta ziyarce shi ya ruga dakin a guje. Ganin Rumana ta kasa rike Maamu sosai kafin Laminde ta dauko musu nata sabulun saboda nasu saura guntu da suke amfani dashi anki basu wani. Mantawa yayi da kayan jikinsa ya shiga ciki ya dagata ya saka a bahu sannan ya soma dibar ruwan yana wanke mata jiki da hannunsa yana kiran sunanta cikin tashin hankali kada ta mutu. Da Laminde ta kawo sabulun hannun Rumana ta ja suka fita ta rufe kofar. Rumana tana son komawa Laminde ta girgiza kai.
"Ki bar Kawunki ya sami ladan mahaifiyarsa Rumana. Dauko mata kaya kafin ya gama"
"Namiji ne fa" ta fada tana yatsina fuska. Tuni Kawun nata ya fice mata a rai.
Laminde tayi murmushi "to naji bari naje ya bani nayi mata wanka"
Gimbi ce ta shigo tana tambayar yana ina suka nuna mata bandakin. Muryarsa taji yana cewa "Gimbi zo kiyi mata wanka zan chanja kaya muje asibiti"
Gabanta har faduwa yayi, wannan kazantar ta jikinta zata taba.....
Laminde tana kallonta sai ta shiga tace zata yi mata. Tsoro taji kada da gangan Gimbi ta saketa ta fadi.
Bayan anyi mata wankan ne Laminde ta kula hannunta daya ya kumbura ta wurin babban yatsanta ga dukkan alamu tayi targade. Haka ta shiryata Awaisu da Gimbi suka kaita asibiti. Suna can ya kasa zama har likita ya fito yace suna mata karin ruwa sannan anyi mata gyaran targade. Hankalinsa duk baya jikinsa sai da ya ganta. Da kyar take magana idanu duk sun fada ciki tace ya kirawo mata Harisu a waya. Gimbi jin an ambaci sunan daya makiyin nata ta kasa kunne sai dai bata jin me Awaisu yake fada da yarensu har ya gama wayar.
Juyowa yayi yace "Gobe in sha Allah Yaya Harisu zai zo da daya daga cikin matansa da Baaba Hure. Ina tsammani zasu taho da kanin Maamu ma. Ki kira Laminde a gyara musu dakin baki kafin mu koma gida"
Kirjinta ne ya buga, mutanen da ta raina zasu cika mata gida.16*KASHE FITILA*💡17
*Batul Mamman*💖
Awaisu bai lura da yadda Gimbi ta chanja da wuri ba daga jin maganar zuwan su Harisu ya mika mata mukullin mota.
"Kije gida ki taho muku da kayan bukata na kwana. Idan kin dawo sai na tafi da motar"
Zaro idanu tayi tana neman amsar da zata bashi domin gujewa kwana da Maamu. Itama Maamu da ta gane me ya fada murya can kasa saboda ciwo tace masa ya tafi da matarsa a kawo mata Laminde ko Rumana. Da ta ga zaiyi gardama tace saboda yara ne. A ranta kuwa cewa take gara ta kwana ita kadai da a barta da Gimbi.
*****
Harisu dakin Baaba yaje ya fada mata Maamu babu lafiya. Hankalinta kuwa ya tashi tace to yaje ya sanarwa 'yan uwanta. Har zai fita ta sake kiransa.
"Dangin mahaifin Awaisu ma ya kamata ka fada musu. Ai kana jin yadda suke yada mana magana wai ya tare a jikinmu baya musu komai"
Harisu ya sha kunu "haba Baaba har yaushe zaki bari zancensu ya dameki. Allah Yana gani yadda duk zuwansa garin nan sai yaje kuma yayi musu alheri. Neman rigima ne kawai"
"Duk da haka kaje ka fada musu ko zasu tura wani yaje dubiya".
"Har na fadawa Awaisun kila muje da kanin Maamu ko wani dai cikinsu. Mu da zamu je dubiya kada kuma a dorawa iyalinsa wahala"
Baaba Hure tayi wani murmushi wanda ita kadai ta san ma'anarsa.
"Baka saba yi min musu ba Harisu. Nace ka fada musu yadda zasu tura wakilinsu dubiya. 'Yan uwanka ma zan sa a kirasu a waya ko mutum biyu a samu. Cikin matanka ka dauki babar Rumana saboda ta gano 'yarta tunda ka hana a kawota hutu. Sauran suma a hankali sai kaje dasu tare ko daya bayan daya"
Harisu kasa motsawa yayi jin wannan hadi na Baaba. Duk girman gidan Awaisu idan sukayi yawa zasu takura musu ne. Ga mara lafiya kuma ga baki da wanne zasu ji.
"Yaya kaki tafiya ne?"
Takalmansa ya saka yayi waje. Ita kuwa Baaba Hure ta gyara kwanciyarta tana jira ya dawo ya kira mata Awaisu ta ji yaya jikin Maamu. Ba komai yasa take son tarawa Gimbi jama'a ba sai bakar maganar da suka yi mata ita da Anti Bebi a rashin sanin bahaushiya ce. So take ta tabbatar Gimbi bata son dangin Awaisu da gaske ne ko kuwa dai 'yar tsama ce irin ta mata da dangin mijinta.
*****
Gidansu Maamu ya fara zuwa inda duka yayyenta maza da kanne suke tare da iyalansu. Bangaren wani cikin 'yan uwan yaje suka gaisa ya sanar dasu abin da ke faruwa. Nan da nan 'yan uwa suka taru ana jajantawa sannan suka ce zasuyi shawara wanda zaije a madadinsu.
Harisu yana fita Hajja Jume matar babban wan Maamu wanda ya dade da rasuwa ta dogaro sandarta ta taho.
"Yanzu labari yazo min za'a tafi wurin Safara'u dubiya ko"
Bashar wanda yake matsayin babba yanzu ya hade rai yana hararar Atika jikar Hajja uwar hada gurmi.
"Tikeke akan gulma zanyi maganinki"
Hajja ta daga sanda tana fada "wanda ya fasa Bashar, nace wanda ya fasa. Yarinya duk kun takura mata kamar ita kadai ce jika. Duk abinku a nan gidan zata zauna. Bani da kowa a gabana sai ita. Tunda tazo ku da iyalanku kun hade mata kai kamar ka jininku ba"
Tikeke ta sunkuyar da kai ita a dole a bar tausayi ce "Hajja babu komai dama na fada miki ne kada a gama rabon waye zaije Abuja gidan Kawu Awaisu a barmu a nan"
Hadi yayi caraf yace "kada ma kusa rai, ni da Yaya Bashar zamu je. Ai ba gayya za'ayi musu ba"
"Wallahi baku isa ba Hadi. Ni zaku nunawa wariya don nawa mijin ya rasu. To ni da Tikeke kamar munje mun gama. Idan da kara ni ya kamata na fadi masu zuwa tunda yaron nan dana ne. Malam da Safa'ra'u ciki daya suka fito ba kamar wasu 'yan uba ba"
Hayaniya ce ta kaure sosai a tsakaninsu karshe aka tsaya akan za'a tafi da Tikeke, Kawu Bashar da matar Hadi. Idan basuyi haka ba tijarar Hajja bata tsallake kowa. Ba karamin aikinta bane ma tasa danta baban Tikeke ya kaisu tunda dreba ne.
****
Kasuwa Harisu ya koma can wurin masu gwanjo ya hadu da Bomai kanin baban Awaisu. Dattijo ne rigimamme na ajin karshe. Yana cikin masu yiwa Harisu habaici wai sun shanye Awaisu baya bi ta kansu. Bayan jarin gwanjon ma shine ya bashi.
"Alh Harisu kenan, yau an leko mu"
"Kawu Bomai yaya kasuwa?"
Kan benci ya zauna yana zukar sigari kafa daya kan daya.
"Gata nan muna fama. Yaya akayi ne?"
Kamar yadda ya sanar da 'yan uwan Maamu haka ya fadawa Bomai. Wani tsalle ya daka ya tashi dama shi ba jiki ba sai tsawo.
"Maamu tamu ce babu lafiya? Kace ban ga ta zama ba. Kayi kyan kai sosai da ka fada min. Asubar fari zanzo nan gidan naka mu tafi"
"Sai wuraren karfe tara zamu tafi. Nace su sauran zaka sanar dasu ko naje na fada musu. Awaisu yace jikin da sauki dai"
Matsowa yayi daf da Harisu "Tunda na sani ka bar maganar kawai ni zan sanar dasu."