Sashe 14
Kashe Fitila Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai kuma ya gyara tsayuwa yana kwantar da kai gaban Harisu "Maamu mutun ce, wato ba don haduwarta da Mal Sa'adu mai rasuwa ba dama ni naso na aureta saboda kula da maraya. Kuma gashi ni ban haihu ba. Shiyasa nake jin yaron nan a raina sosai. Kaga sau biyar fa yana bani jari. Yaro yayi halin iyayensa wurin karamci"
Harisu gyada kai kawai yake yi ya samu ya bar wurin. Baaba Hure ta hadashi da aiki. Me zai sa tace kowa sai yaje. Tausayin Awaisu da Gimbi wadda za'a hada da baki ne ya kama shi.
Yana kallo Bomai ya kulle gwanjonsa ya saba a kafada yayi hanyar titi.
*****
"Hinde maza maza fito ki fara hada kaya"
Hinde na bandaki ta fito da sauri bota a hannu. Ajiye botar tayi ta sa hannu ta toshe gefen hanci ta rangada guda tana tafa hannuwa
"Ayyiriririiiii, sai yau kaga damar sakin nawa, to ka sani kuma ka jira ina gama idda zan sami miji da ya amsa sunansa ba irinka ba kashi da rai. Nawa kayi min ne sakin"
Botar da ta fito da ita ya dauka ya kafa a baki ya sha ruwan sannan ya kuskure baki ya tofar.
"Dadina dake wutar ciki, baki ji bayani ba kin hau suki burutsu. To ai sai ki tafi nima na huta"
"To dai gaya min me ya faru idan ba sakin bane kake min wannan kiran"
Kan kullin gwanjon ya dare ya zauna "Abuja zamu koma gidan dana"
Wata muguwar shaka Hinde tayi masa har yana zaro idanu "munafuki ashe har da gareka ban sani ba. A wace tashar ka hadu da babarsa"
Hannunta yake duka da kyar yana cewa "Awai,aaaaw,awsu"
Sassauta rikon tayi yace "AWAISU ne fa dan marigayi yayana. Kasheni zakiyi ne?"
Hinde ta zauna shirim a gefensa tare da murza masa wuyan.
"Kaine baka iya kawo labari ba. Kace Awaisu na Maamu"
Nan ya labarta mata yadda sukayi da Harisu da kuma kudurinsa
"Yace kwana biyu zamuyi. Amma so nake ki hada kayan kamar na sati. Sai kuma mu saka kamar uku uku a jikinmu kada a ga Ghana mazigo din kayanmu da girma. Idan munje zan sa ya nema min aiki. Kema ki rinka yiwa Gimbiyar nan ladabi. Kinsan durkusawa wada ba gajiyawa bane."
Hinde sai murna zasu Abuja. Ko Bomai bai fada ba bata ga dalilin da zaisa idan sun je ta dawo Fika ba. Kallonta yayi ta shige daki ta fara fiddo kayansu zata wanke yace
"Hinde don Allah idan munje kada ki nuna hali, banda dauke dauke kinji ko"
Harara ta galla masa idonta kamar ya fado. Me zai kaita sata kuma yanzu, ita da tayi a gidan biki 'yan mata sukayi mata duka sai da hakorinta na kasa ya cire.
******
Daren ranar Gimbi kasa bacci tayi. A haka ma don bata san mutum nawa ne masu zuwa ba. Sau biyu Awaisu yana farkawa ya ganta a zaune sai tace masa jikin Maamu ke damunta. Gashi likita yace harda rashin cin abinci sosai. Harda kukanta tace
"My dear ko zaka tambayi Maamu me tafi so sai na rinka dafa mata. Gobe zan dauki hutu ko na sati ne na kula da ita"
"Kema kinsan bazasu baki wannan hutun ba. Ki bari kawai tunda akwai masu zuwa"
Murmushi tayi, don tana tunanin a goben Anti Bebi zata kaiwa Wangesi bukatarta akan ogansu. Sake marairaicewa tayi
"Duk laifina ne da nake zuwa aiki bana iya kulawa da ita yadda ya kamata. Kullum da safe idan naje fada mata zan fita Maamu sai tayi min addua. Yanzu idan suka zo aka ce na barta da yunwa fa."
Kuka ta fashe dashi Awaisu ya rarrasheta. Karshe tace masa zata bar aikin kawai ta kula da gida. Ga mamakinta sai taga ya bata goyon baya. A zuci tace wato shima bakinciki yake da aikin. To yanzu ta fara.
*****
Da safe tunda babu Laminde gashi tana son burge Awaisu haka tayi farfesun kayan ciki da dankali ta hadawa Maamu Awaisu ya kai asibiti. Bayan su Haris sun tafi makaranta ta fadawa Anti Bebi halin da take ciki da bakin da zasu zo.
"Zage damtse zakiyi ki kyautata musu kada wani ya sami bakin magana akanki" inji Anti Bebi.
Ai kuwa ta wuni a kitchen tana girkin tarbar baki mutum hudu ko dubiya bata samu zuwa ba. Sai yamma likis suka iso mota biyu. Awaisu ma shigowarsa kenan kuma Haris yayi masa waya ya sanar dashi karin da aka samu yace ya amince duka su taho tare akwai wurin kwana. Sai dai kuma ya manta bai fadawa Gimbi ba. Jin tsayuwar mota tabi yaranta suka taho da gudu tarbarsu Baaba Hure. Sai ga Gimbi murmushi ya makale a gefen baki. Mutane ta gani wanda ta sani da wanda bata taba gani ba.
Baaba Hure, Anti Ummukulsum, Harisu, Maman Rumana, Kawu Bashar, Ammu matar Hadi, Tikeken Hajja, Bomai da matarsa Hinde. Mutum takwas. Tun a zuci ta fara kuka.17*KASHE FITILA*💡18
*Batul Mamman*💖
Zuciyar Gimbi harbawa ta rinka yi sosai saboda wani bacin rai da ya danneta. Kasa daurewa tayi duk iya kokarinta ta fashe musu da kukan bakinciki mai sauti. Ai kuwa hankalinsu Baaba Hure ya tashi matuka sun zata ko Maamu rai yayi halinsa ne. Da yake ta fara kwarewa da kissa irin ta Anti Bebi sai tayi saurin goge hawayen harda rungumo Baaba tana kallon Harisu a zatonta shi kadai yake jin Hausa.
"Wallahi tsabar murnar ganinku ne Yaya. Tun jiya da yace zaku zo nake murna. Allah Sarki Maamu yau zan gani ni da ita wa yafi murnar zuwanku"
Daga gefe taji ance "kissa adon mata, Bomoi ka ga wadda ta fini"
Hinde ta fada da sunan rada duk da tasan ana jinta kuma da hausa. Bomoi ya galla mata harara ya kalli Gimbi yana murmushin dole. Daga zuwansu zata nemi janyo musu bakin jini wurin matar gida.
A razane Gimbi ta kalli Hinde har cikinta yana kadawa. Sakin fuska tayi ba arziki kamar bata fahimceta ba tace su shigo ciki. Mukullin wani daki ta waje ta bawa Harisu inda ya taba masauki lokacin zuwansu Hajji. Nan suka shiga shi da Kawu Bashar da Bomoi wanda yake ta zuba surutun haduwar gidan dansa gudan jininsa.
Daula ce tayiwa Baaba Hure jagora zuwa dakin Maamu inda zata zauna. Wani daki a gefensa kuma Gimbi tace Ummukulsum, Maman Rumana, Ammu, Hinde da Tikeke su shiga suyi wanka sannan su fito cin abinci.
Tikeke ta zumburo baki "Haba Hajiya ko ruwa bamu sha ba zaki ce muyi wanka. Allah Ya gani sai naci abinci nake iya komai."
Ammu ta riko hannun Tikeke tana kokarin fita daga dakin zata koma falo inda ta hango kwanukan abinci an jere su. Kokawar fizgewa Tikeke ta somayi Ammu ta canja harshe tace zata fadawa Kawu Bashar. Rai a bace ta kwace hannunta ta shiga bandakin tare ta bugu kofa.
Jiki a sanyaye Gimbi ta fita daga dakin. Yau kuma irin bakin da tayi kenan ta fada a zuci. Falon taji kamar yana warin gumi a cewarta ta dauko air freshner ta shiga fesawa. Juyawar da zatayi ta hada ido da Baaba Hure tayi saurin ja da baya.
Baaba ta saki fuska
"Dama kwan fitilar bandakin ne naga ya mutu. Idan akwai wani ki taimaka a saka min don in yamma tayi ba gani nake sosai ba bare kuma a duhu"
Mamaki ne ya bayyana sosai a fuskar Gimbi jin Baaba tana hausa. Dazu ma taji wata tayi a waje. Yanzu bata isa ta juya harshe tayi gulmarsu a gabansu ba kenan.
"Baaba bari idan Abban Haris ya dawo sai a saka miki ki shiga"
Baaba ta dafata da hannu daya tana dan tafiya
"muje ki kaini naki sai nayi alwala a can. Banyi sallar la'asar ba ga magariba tana gabatowa"
Ba'a son ranta ta kai Baaba bandakinta ba. Maamu kuwa ko hanyar dakin bata taba takawa da kafarta ba. Tana zaune tana ji Baaba Hure tana kaki. Takaici ya isheta ta fita ta koma dakin Awaisu sannan ta kira Anti Bebi.
"Na shiga uku Anti, su takwas kamar ance musu ta mutu. Ina zan kaisu"
"Ba na son shirme kinji ko. Ki tashi ki je duk yadda suke so kiyi musu. Idan kika bari suka gane wani abu to karshenta su ki tafiya da wuri. Kinga garin neman gira kin rasa ido"
Maganar Anti Bebi gaskiya ce. Da saurinta ta shiga kitchen ta dora macaroni tunda dama shinkafa da miya tayi da kuma tuwon dare. Kafin ta gama Awaisu ya shigo ya tafi wurinsu Harisu suna gaisawa.
Sai da sukayi sallar magariba suka ci abinci sannan suka fara shirin tafiya asibiti gabadayansu. Gimbi tana ta raha da rawar kai ita me son surukai. Sun firfito waje Awaisu ya kira drebansa da yake kai yara makaranta ya bashi mukullin mota
"Sunday gashi ka debe su Yaya Ummukulsum ka wuce dasu asibitin da aka kwantar da Maamu. Zan tsaya a atm ne sannan na taho da su Baaba"
Sunday ya dan rissina a ladabce "Oga yaushene Hajiya babu lafiya, wane asibiti ne.?"
Awaisu yaji kamar ya raina masa hankali yace "Inda ka kai musu abincin rana mana"
"Ban fita ba tunda mun dawo da su Haris"
Idanun Awaisu suka kankance yana kallon Gimbi "da kanki kika kai musu abincin rana? Ina na daren ne ma ban ga an dauko ba"
Idanun Gimbi nan da nan suka yo waje ta rasa amsar bayarwa. Baaba Hure tana kallonta tasan bata da gaskiya
"Gimbiya kada kice min ba'a kaiwa Maamu abincin rana ba bare na dare"
"Uhmmm, uhmmm" nan fa jikinta ya soma rawa ganin idanu a kanta ga Awaisu yana wani huci kamar mayunwacin zaki. Irin wannan fushin nasa ba kasafai yake ba. Kuma a tunaninta yanzu da Wangesi ya gama masa aiki bai isa yayi mata ko da mugun kallo ba.
Tsawa ya daka mata kamar ya kai mata duka "ki bani amsa mana"
Harisu ne yayi magana ganin ransa da na Baaba Hure a bace yake. Yaran ya fara cewa su shiga motar Sunday sannan yace "Awaisu meye haka ne kake yi mata tsawa gaban yara. Gimbiya an kai abincin?"
Harisu gyada kai kawai yake yi ya samu ya bar wurin. Baaba Hure ta hadashi da aiki. Me zai sa tace kowa sai yaje. Tausayin Awaisu da Gimbi wadda za'a hada da baki ne ya kama shi.
Yana kallo Bomai ya kulle gwanjonsa ya saba a kafada yayi hanyar titi.
*****
"Hinde maza maza fito ki fara hada kaya"
Hinde na bandaki ta fito da sauri bota a hannu. Ajiye botar tayi ta sa hannu ta toshe gefen hanci ta rangada guda tana tafa hannuwa
"Ayyiriririiiii, sai yau kaga damar sakin nawa, to ka sani kuma ka jira ina gama idda zan sami miji da ya amsa sunansa ba irinka ba kashi da rai. Nawa kayi min ne sakin"
Botar da ta fito da ita ya dauka ya kafa a baki ya sha ruwan sannan ya kuskure baki ya tofar.
"Dadina dake wutar ciki, baki ji bayani ba kin hau suki burutsu. To ai sai ki tafi nima na huta"
"To dai gaya min me ya faru idan ba sakin bane kake min wannan kiran"
Kan kullin gwanjon ya dare ya zauna "Abuja zamu koma gidan dana"
Wata muguwar shaka Hinde tayi masa har yana zaro idanu "munafuki ashe har da gareka ban sani ba. A wace tashar ka hadu da babarsa"
Hannunta yake duka da kyar yana cewa "Awai,aaaaw,awsu"
Sassauta rikon tayi yace "AWAISU ne fa dan marigayi yayana. Kasheni zakiyi ne?"
Hinde ta zauna shirim a gefensa tare da murza masa wuyan.
"Kaine baka iya kawo labari ba. Kace Awaisu na Maamu"
Nan ya labarta mata yadda sukayi da Harisu da kuma kudurinsa
"Yace kwana biyu zamuyi. Amma so nake ki hada kayan kamar na sati. Sai kuma mu saka kamar uku uku a jikinmu kada a ga Ghana mazigo din kayanmu da girma. Idan munje zan sa ya nema min aiki. Kema ki rinka yiwa Gimbiyar nan ladabi. Kinsan durkusawa wada ba gajiyawa bane."
Hinde sai murna zasu Abuja. Ko Bomai bai fada ba bata ga dalilin da zaisa idan sun je ta dawo Fika ba. Kallonta yayi ta shige daki ta fara fiddo kayansu zata wanke yace
"Hinde don Allah idan munje kada ki nuna hali, banda dauke dauke kinji ko"
Harara ta galla masa idonta kamar ya fado. Me zai kaita sata kuma yanzu, ita da tayi a gidan biki 'yan mata sukayi mata duka sai da hakorinta na kasa ya cire.
******
Daren ranar Gimbi kasa bacci tayi. A haka ma don bata san mutum nawa ne masu zuwa ba. Sau biyu Awaisu yana farkawa ya ganta a zaune sai tace masa jikin Maamu ke damunta. Gashi likita yace harda rashin cin abinci sosai. Harda kukanta tace
"My dear ko zaka tambayi Maamu me tafi so sai na rinka dafa mata. Gobe zan dauki hutu ko na sati ne na kula da ita"
"Kema kinsan bazasu baki wannan hutun ba. Ki bari kawai tunda akwai masu zuwa"
Murmushi tayi, don tana tunanin a goben Anti Bebi zata kaiwa Wangesi bukatarta akan ogansu. Sake marairaicewa tayi
"Duk laifina ne da nake zuwa aiki bana iya kulawa da ita yadda ya kamata. Kullum da safe idan naje fada mata zan fita Maamu sai tayi min addua. Yanzu idan suka zo aka ce na barta da yunwa fa."
Kuka ta fashe dashi Awaisu ya rarrasheta. Karshe tace masa zata bar aikin kawai ta kula da gida. Ga mamakinta sai taga ya bata goyon baya. A zuci tace wato shima bakinciki yake da aikin. To yanzu ta fara.
*****
Da safe tunda babu Laminde gashi tana son burge Awaisu haka tayi farfesun kayan ciki da dankali ta hadawa Maamu Awaisu ya kai asibiti. Bayan su Haris sun tafi makaranta ta fadawa Anti Bebi halin da take ciki da bakin da zasu zo.
"Zage damtse zakiyi ki kyautata musu kada wani ya sami bakin magana akanki" inji Anti Bebi.
Ai kuwa ta wuni a kitchen tana girkin tarbar baki mutum hudu ko dubiya bata samu zuwa ba. Sai yamma likis suka iso mota biyu. Awaisu ma shigowarsa kenan kuma Haris yayi masa waya ya sanar dashi karin da aka samu yace ya amince duka su taho tare akwai wurin kwana. Sai dai kuma ya manta bai fadawa Gimbi ba. Jin tsayuwar mota tabi yaranta suka taho da gudu tarbarsu Baaba Hure. Sai ga Gimbi murmushi ya makale a gefen baki. Mutane ta gani wanda ta sani da wanda bata taba gani ba.
Baaba Hure, Anti Ummukulsum, Harisu, Maman Rumana, Kawu Bashar, Ammu matar Hadi, Tikeken Hajja, Bomai da matarsa Hinde. Mutum takwas. Tun a zuci ta fara kuka.17*KASHE FITILA*💡18
*Batul Mamman*💖
Zuciyar Gimbi harbawa ta rinka yi sosai saboda wani bacin rai da ya danneta. Kasa daurewa tayi duk iya kokarinta ta fashe musu da kukan bakinciki mai sauti. Ai kuwa hankalinsu Baaba Hure ya tashi matuka sun zata ko Maamu rai yayi halinsa ne. Da yake ta fara kwarewa da kissa irin ta Anti Bebi sai tayi saurin goge hawayen harda rungumo Baaba tana kallon Harisu a zatonta shi kadai yake jin Hausa.
"Wallahi tsabar murnar ganinku ne Yaya. Tun jiya da yace zaku zo nake murna. Allah Sarki Maamu yau zan gani ni da ita wa yafi murnar zuwanku"
Daga gefe taji ance "kissa adon mata, Bomoi ka ga wadda ta fini"
Hinde ta fada da sunan rada duk da tasan ana jinta kuma da hausa. Bomoi ya galla mata harara ya kalli Gimbi yana murmushin dole. Daga zuwansu zata nemi janyo musu bakin jini wurin matar gida.
A razane Gimbi ta kalli Hinde har cikinta yana kadawa. Sakin fuska tayi ba arziki kamar bata fahimceta ba tace su shigo ciki. Mukullin wani daki ta waje ta bawa Harisu inda ya taba masauki lokacin zuwansu Hajji. Nan suka shiga shi da Kawu Bashar da Bomoi wanda yake ta zuba surutun haduwar gidan dansa gudan jininsa.
Daula ce tayiwa Baaba Hure jagora zuwa dakin Maamu inda zata zauna. Wani daki a gefensa kuma Gimbi tace Ummukulsum, Maman Rumana, Ammu, Hinde da Tikeke su shiga suyi wanka sannan su fito cin abinci.
Tikeke ta zumburo baki "Haba Hajiya ko ruwa bamu sha ba zaki ce muyi wanka. Allah Ya gani sai naci abinci nake iya komai."
Ammu ta riko hannun Tikeke tana kokarin fita daga dakin zata koma falo inda ta hango kwanukan abinci an jere su. Kokawar fizgewa Tikeke ta somayi Ammu ta canja harshe tace zata fadawa Kawu Bashar. Rai a bace ta kwace hannunta ta shiga bandakin tare ta bugu kofa.
Jiki a sanyaye Gimbi ta fita daga dakin. Yau kuma irin bakin da tayi kenan ta fada a zuci. Falon taji kamar yana warin gumi a cewarta ta dauko air freshner ta shiga fesawa. Juyawar da zatayi ta hada ido da Baaba Hure tayi saurin ja da baya.
Baaba ta saki fuska
"Dama kwan fitilar bandakin ne naga ya mutu. Idan akwai wani ki taimaka a saka min don in yamma tayi ba gani nake sosai ba bare kuma a duhu"
Mamaki ne ya bayyana sosai a fuskar Gimbi jin Baaba tana hausa. Dazu ma taji wata tayi a waje. Yanzu bata isa ta juya harshe tayi gulmarsu a gabansu ba kenan.
"Baaba bari idan Abban Haris ya dawo sai a saka miki ki shiga"
Baaba ta dafata da hannu daya tana dan tafiya
"muje ki kaini naki sai nayi alwala a can. Banyi sallar la'asar ba ga magariba tana gabatowa"
Ba'a son ranta ta kai Baaba bandakinta ba. Maamu kuwa ko hanyar dakin bata taba takawa da kafarta ba. Tana zaune tana ji Baaba Hure tana kaki. Takaici ya isheta ta fita ta koma dakin Awaisu sannan ta kira Anti Bebi.
"Na shiga uku Anti, su takwas kamar ance musu ta mutu. Ina zan kaisu"
"Ba na son shirme kinji ko. Ki tashi ki je duk yadda suke so kiyi musu. Idan kika bari suka gane wani abu to karshenta su ki tafiya da wuri. Kinga garin neman gira kin rasa ido"
Maganar Anti Bebi gaskiya ce. Da saurinta ta shiga kitchen ta dora macaroni tunda dama shinkafa da miya tayi da kuma tuwon dare. Kafin ta gama Awaisu ya shigo ya tafi wurinsu Harisu suna gaisawa.
Sai da sukayi sallar magariba suka ci abinci sannan suka fara shirin tafiya asibiti gabadayansu. Gimbi tana ta raha da rawar kai ita me son surukai. Sun firfito waje Awaisu ya kira drebansa da yake kai yara makaranta ya bashi mukullin mota
"Sunday gashi ka debe su Yaya Ummukulsum ka wuce dasu asibitin da aka kwantar da Maamu. Zan tsaya a atm ne sannan na taho da su Baaba"
Sunday ya dan rissina a ladabce "Oga yaushene Hajiya babu lafiya, wane asibiti ne.?"
Awaisu yaji kamar ya raina masa hankali yace "Inda ka kai musu abincin rana mana"
"Ban fita ba tunda mun dawo da su Haris"
Idanun Awaisu suka kankance yana kallon Gimbi "da kanki kika kai musu abincin rana? Ina na daren ne ma ban ga an dauko ba"
Idanun Gimbi nan da nan suka yo waje ta rasa amsar bayarwa. Baaba Hure tana kallonta tasan bata da gaskiya
"Gimbiya kada kice min ba'a kaiwa Maamu abincin rana ba bare na dare"
"Uhmmm, uhmmm" nan fa jikinta ya soma rawa ganin idanu a kanta ga Awaisu yana wani huci kamar mayunwacin zaki. Irin wannan fushin nasa ba kasafai yake ba. Kuma a tunaninta yanzu da Wangesi ya gama masa aiki bai isa yayi mata ko da mugun kallo ba.
Tsawa ya daka mata kamar ya kai mata duka "ki bani amsa mana"
Harisu ne yayi magana ganin ransa da na Baaba Hure a bace yake. Yaran ya fara cewa su shiga motar Sunday sannan yace "Awaisu meye haka ne kake yi mata tsawa gaban yara. Gimbiya an kai abincin?"