Sashe 10
Kashe Fitila Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yau Rumana ta dawo da yunwa saboda dan kudin hannun Maamu tuni ya kare. Abincin rana kuwa dama an soke shi a hankali. Da safe take sawa Laminde tayi musu girki wanda take tafiya wurin aiki dashi a zubawa yaranta. Da rana tace ba zama suke yi ba Laminde ta huta. Sai biyar zuwa shida idan sun dawo a dora na dare. Kana ganinsu har sun fara rama. Idan sunyi waya da Harisu sai tayi ta kokarin danne damuwarta. A matsayinta na uwa ga Awaisu duk yadda suke da su Baaba Hure akwai abin da dole kaji kunyar fadawa duniya. Yau da wata aka yiwa haka da sauki sai ta iya shiga ciki domin tsawatarwa. Amma ita mahaifiyarsa da kanta wurin wa kuma zata kai kara.
Suna zaman jiran abincin dare a dakin Mu'allim ya shigo yana buga ball. Da karfinsa ya mako ta bata fada ko'ina ba sai fuskar Maamu. Rumana ta tashi da sauri ta kwada masa mari. Dama tuni Gimbi tasa yaran suka dena shiga dakin wai bata so suna damun Maamu.
Jin zafin marin yasa ya kwalla kara. Sai ga Gimbi ta shigo a guje ta dauke shi tana tambayar me aka yi masa. Yana rike da kumatu ya fada mata Rumana ce ta mare shi. Batare da neman ba'asi ba ta sauke shi a gaban Maamu tace ya rama.
Rumana ta zaro idanu "Mummy kinga fa wannan katuwar ball din ya bugawa Maamu."
"Shine zaki mare shi saboda mugunta bayan kinsan ba da gangan bane. Ki bari ya rama ko kuma ni na rama masa"
Rumana ta kalli Maamu tana hawaye saboda irin wannan cin zarafi da akeyi musu. Idan da kara ko cin zalinsa akayi tunda Maamu tana wurin bai kamata tayi magana ba.
"Gara ke ki rama masa akan na bari kanin bayana ya mareni" ta fada tana kuka
Motsin tahowar Awaisu Gimbi taji ta rage sautin muryarta
"Bazaki bari ya rama ba?"
"Wallahi bai isa ya mareni ba" fushi da bacin ran da take boyewa ne ya fito yau. Ita bata ki ace ta tattara ta koma gida ba.
Awaisu ya shigo rai a bace ganin yadda take kallon Gimbi ido cikin ido ya daga hannu zai mareta. Sai a lokacin Maamu ta tashi ta rike masa hannu.
"Idan ka taba yarinyar nan zaka hadu da bacin raina Awaisu"
"Maamu kada ki bari Rumana ta tashi a sangarce. Baki ga yadda take yiwa Gimbi rashin kunya bane"
Gimbi dai bata jin me suke fadi da yarensu. Jin an ambaci sunanta ta matso 'yar kwalla
"Abban Haris ka bar maganar nan haka. Bana so Maamu tayi fushi da kai akan wannan 'yar matsalar. Rumana kiyi hakuri kinji"
Tsabar mamaki yasa ta kasa magana ma. Shi kuwa Awaisu ficewa yayi rai a bace a ganinsa sangarta Rumana za'ayi tunda tana yiwa matarsa rashin kunya kuma an hanashi hukunta ta.
Da suka fita Rumana ta fashe da kuka Maamu ta kasa rarrashinta. Ita da idonta har ya kumbura ya kankance cikin dan lokaci amma Awaisu ko kula baiyi ba me zata ce mata a wannan lokacin. A haka Laminde tazo ta kawo musu tuwonsu. Dole suka ci tunda sun wuni da yunwa.
*****
Kallo suke yi a falo tare da yaransu suna taba hira. Hankalin Awaisu ne ya tafi wurin Mu'allim da yake fadawa 'yan uwansa ya iya buga ball da karfi har Maamu ya bugawa a fuska.
Daga kashingidar da yayi ya tashi da sauri "wa ka bugawa ball kace?"
Gimbi tayi saurin tarewa "ku tashi ku tafi ku kwanta dare yayi"
Awaisu ya janyo hannun Mu'allim. Fuskarsa babu alamun wasa ya tambayeshi me ya faru a dakin. Gimbi ya fara kallo sai dai bata da ta cewa a wurin. Dolensa ya fadi abin da yayi da marin da ya sha.
Da sauri Awaisu ya tashi yayi hanyar dakin Maamu. Gimbi ta soma kiransa sai dai ko juyowa baiyi ba.
Yana shiga ya tarar da Maamu a kwance ta rike kankarar pure water a daidai idonta yayin da Rumana har yanzu kuka take yi. Kankarar ya karba ya ga idon ya suntume.
"Subhanallahi Maamu kiyi hakuri. Yanzu nake jin abin da ya faru"
Tashi tayi zaune idonta cike da kwalla tace Rumana ta fita
"dama irin zaman da kake son yi dani kenan ka takura muka taho?"
Kansa ya sunkuyar kasa yana bata hakuri.
"Yaushe rabon da ka shigo dakin nan balle ka duba lafiyarmu? Bance kada kaso iyalinka ba amma ka tuna cewa nima ina da hakki a kanka. Bana neman komai a gareka da ya wuce ka bani girman da Allah Ya bani akanka sannan ka kula da amanar Rumana. Idan ka wulakanta zuri'ar Baaba Hure kafi kowa sanin irin kallon da duniya zata yi maka. Sannan a lahira ka tashi cikin masu tozarta zumunci."
"Kiyi hakuri, nasan nayi kuskure amma zan gyara in sha Allahu. Na rasa abin da yake damuna ni kaina"
Duk da ranta a bace yake amma taji dadi yau ya nuna damuwarsa garesu
"Ka tashi ka tafi ya wuce"
"Asibiti zan kaiki saboda idon. Shi kuma zai gamu dani wallahi."
A fusace ya fita daga dakin. Rumana da take tsaye a gefe yace mata daga yau ta rinka fitowa da Maamu falo suna shan iska baya son suna kulle kansu. Dakin yaran ya wuce Gimbi tana tambayarsa me zaiyi da wayar chaja bai kulata ba sai gani tayi ya fara laftawa Mu'allim dan shekara bakwai a jikinsa. Yana dukansa duk ya cika gidan da ihu Gimbi ta kasa karbar chajar sai ma rabonta data samu a baya.
Maamu tana jinsu ta kwanta abin ta. Bata kin jikokinta amma ta kula da yadda suka bi sahun babarsu wurin banzatar dasu a gidan. Ranar Awaisu da Gimbi barambaram akayi babu mai kula dan uwansa tun bayan da ya gama hukunta Mu'allin tare da ja mata kunne sosai akan Maamu.
Da safe a motarsa suka dauki Rumana zuwa makaranta ya bata dubu biyar yace ta ajiye sauran a gida. Yaso kai Maamu asibiti ma tace ta warke.
*****
Gimbi tana fita da suka kai yara makaranta gidan Anti Bebi ta wuce. Tana kuka ta fada mata irin dukan da Awaisu yayiwa Mu'allim. Gashi tana ganin kamar maganin ya fara sakinsa.
"Ni dai kawai kizo muje gidan Wangesi kada komai ya lalace min"
"Gimbi kenan wato mugu baya so a dandana masa zumarsa sai ya birkice. Don yau daya anyi miki meye na fushi. Can wurin aikin naki fa?"
"Ni dai kawai kizo muje zan san karyar da zanyi musu"
Ko mijinta bata sake lekawa ba ta dauko dan gyalenta suka fice. Gimbi ta sallami nata dreban suka wuce da dan koran Anti Bebi. Wangesi ya bata wasu kwayaye guda hudu duk anyi musu zane da jar tawwada da wasu layu da kulle kullen magani. Komai yayi mata bayanin yadda zata yi amfani dashi ta kawo kudi ta ajiye masa.
Suna komawa gida ta wuce. Kwai daya a kofar dakin Awaisu ta fasa shi ta rufe da door mat. Sauran biyun kuma daya a bayan dakin Maamu dayan kuma ta dafa shi ta cinye.
Da ta gama ta dauki motarta ta koma gidan Anti Bebi sai lokacin tashin yara ta dawo. Manajan bankin da take ya kira Awaisu kan cewa yayi mata magana akan fashi da rashin zuwa da wuri ko kuma fita kafin a tashi. Don ma yana ganin kimarsa ne da tuni ya bata takardar jan kunne.
Hakuri ya bashi tare da godiya. Yana dawowa ya hauta da fadan sai ta gaya masa inda take zuwa. Ta rasa amsar da zata bashi. Abincin da ta zuba rabin maganin kuma yaki ci. Daren ranar yaransa yasa a gaba suka taya Maamu da Rumana hira a falo.
Gimbi kuwa Anti Bebi ta kira tana kuka Wangesi ya ci kudinta a banza.
"Kin fiye wutar ciki. Haka aka ce miki asirin yana kama mutane kamar a fim? A hankali zai cinye shi ya dawo miki tamkar sakarai shashasha"
Tsaki tayi ta ajiye wayar. Ita Anti Bebi bata da aiki sai fadin bakar magana. Awaisunta ba sakarai bane ta fada a zuci tana huci ita kadai.
Sai bayan sati ta kula ya fara sanyi fiye da yadda yayi a baya ma. Sa idonsa akan lamarin su Maamu da suka fara shanawa yanzu babu.
Gidan jiya aka koma inda take horasu da yunwa wai don kada suji dadin gidan su cigaba da zama.13*KASHE FITILA*💡14
*Batul Mamman*💖
*Bayan Sati Uku*
Zaune take gaban madubi tana kwalliya taji kamar ana kiranta. Jagirar hannunta ta ajiye ta fito daga dakin tare da leka falon ta saman bene. Mijinta ne ya shigo rai a bace sai huci yake.
"Shuhada kina ina ne?"
Saurin saukowa tayi har tana hada bene biyu a lokaci daya
"Me ya faru T?"
Mugun kallo ya bita dashi kafin yayi magana "kizo ki fice daga gidan nan na sakeki"
Ji tayi kamar an sakar mata guduma a tsakiyar kanta
"Ka sakeni? T kalmar saki fa ba kalmar wasa bace"
Idanunsa kara rinewa sukeyi suna yin ja saboda bacin ran da ya rasa dalilinsa.
"Ni zaki rainawa hankali, to zamana dake ya kare. Ki tattara ki fita kafin kiji hannuna a jikinki"
Shuhada rasa bakin magana tayi. Anya mijin nata hankalinsa daya kuwa. Ya fita suna farinciki da juna. Me ya kawo wannan chanji haka. Dan matsawa tayi kusa dashi
"T ka zauna don Allah muyi magana. Na rasa gane abin da yake faruwa. Abokanka sun baka wani abu ne kasha da baka sani ba?"
Saukar mari taji har biyu "kina nufin ina shaye shaye ne."
Dafe kuncinta tayi tana kuka "Tajuddeen kana cikin hankalinka kuwa. Nice fa, me nayi maka haka"
Girgiza kai yayi yana yamutsa fuska "tsanarki kawai nayi S. And I want you to get out now kafin raina ya kara baci"
Kuka ne sosai yaci karfinta. Gabadaya kwakwalwarta ta toshe. Mutum ya fita lafiya ya dawo a birkice. Ba karamin so yake nuna mata ba tun kafin aurensu har zuwa yanzu da suka sami shekara daya tare. Gani tayi ya hau sama ya fara cillo mata kayanta ta saman bene. Lallai da gaske yake. Tana kallo ya gama ya sauko ya bude wallet dinsa. Kudi ya debo ya watsa mata a fuska.
"Now get out"
Suna zaman jiran abincin dare a dakin Mu'allim ya shigo yana buga ball. Da karfinsa ya mako ta bata fada ko'ina ba sai fuskar Maamu. Rumana ta tashi da sauri ta kwada masa mari. Dama tuni Gimbi tasa yaran suka dena shiga dakin wai bata so suna damun Maamu.
Jin zafin marin yasa ya kwalla kara. Sai ga Gimbi ta shigo a guje ta dauke shi tana tambayar me aka yi masa. Yana rike da kumatu ya fada mata Rumana ce ta mare shi. Batare da neman ba'asi ba ta sauke shi a gaban Maamu tace ya rama.
Rumana ta zaro idanu "Mummy kinga fa wannan katuwar ball din ya bugawa Maamu."
"Shine zaki mare shi saboda mugunta bayan kinsan ba da gangan bane. Ki bari ya rama ko kuma ni na rama masa"
Rumana ta kalli Maamu tana hawaye saboda irin wannan cin zarafi da akeyi musu. Idan da kara ko cin zalinsa akayi tunda Maamu tana wurin bai kamata tayi magana ba.
"Gara ke ki rama masa akan na bari kanin bayana ya mareni" ta fada tana kuka
Motsin tahowar Awaisu Gimbi taji ta rage sautin muryarta
"Bazaki bari ya rama ba?"
"Wallahi bai isa ya mareni ba" fushi da bacin ran da take boyewa ne ya fito yau. Ita bata ki ace ta tattara ta koma gida ba.
Awaisu ya shigo rai a bace ganin yadda take kallon Gimbi ido cikin ido ya daga hannu zai mareta. Sai a lokacin Maamu ta tashi ta rike masa hannu.
"Idan ka taba yarinyar nan zaka hadu da bacin raina Awaisu"
"Maamu kada ki bari Rumana ta tashi a sangarce. Baki ga yadda take yiwa Gimbi rashin kunya bane"
Gimbi dai bata jin me suke fadi da yarensu. Jin an ambaci sunanta ta matso 'yar kwalla
"Abban Haris ka bar maganar nan haka. Bana so Maamu tayi fushi da kai akan wannan 'yar matsalar. Rumana kiyi hakuri kinji"
Tsabar mamaki yasa ta kasa magana ma. Shi kuwa Awaisu ficewa yayi rai a bace a ganinsa sangarta Rumana za'ayi tunda tana yiwa matarsa rashin kunya kuma an hanashi hukunta ta.
Da suka fita Rumana ta fashe da kuka Maamu ta kasa rarrashinta. Ita da idonta har ya kumbura ya kankance cikin dan lokaci amma Awaisu ko kula baiyi ba me zata ce mata a wannan lokacin. A haka Laminde tazo ta kawo musu tuwonsu. Dole suka ci tunda sun wuni da yunwa.
*****
Kallo suke yi a falo tare da yaransu suna taba hira. Hankalin Awaisu ne ya tafi wurin Mu'allim da yake fadawa 'yan uwansa ya iya buga ball da karfi har Maamu ya bugawa a fuska.
Daga kashingidar da yayi ya tashi da sauri "wa ka bugawa ball kace?"
Gimbi tayi saurin tarewa "ku tashi ku tafi ku kwanta dare yayi"
Awaisu ya janyo hannun Mu'allim. Fuskarsa babu alamun wasa ya tambayeshi me ya faru a dakin. Gimbi ya fara kallo sai dai bata da ta cewa a wurin. Dolensa ya fadi abin da yayi da marin da ya sha.
Da sauri Awaisu ya tashi yayi hanyar dakin Maamu. Gimbi ta soma kiransa sai dai ko juyowa baiyi ba.
Yana shiga ya tarar da Maamu a kwance ta rike kankarar pure water a daidai idonta yayin da Rumana har yanzu kuka take yi. Kankarar ya karba ya ga idon ya suntume.
"Subhanallahi Maamu kiyi hakuri. Yanzu nake jin abin da ya faru"
Tashi tayi zaune idonta cike da kwalla tace Rumana ta fita
"dama irin zaman da kake son yi dani kenan ka takura muka taho?"
Kansa ya sunkuyar kasa yana bata hakuri.
"Yaushe rabon da ka shigo dakin nan balle ka duba lafiyarmu? Bance kada kaso iyalinka ba amma ka tuna cewa nima ina da hakki a kanka. Bana neman komai a gareka da ya wuce ka bani girman da Allah Ya bani akanka sannan ka kula da amanar Rumana. Idan ka wulakanta zuri'ar Baaba Hure kafi kowa sanin irin kallon da duniya zata yi maka. Sannan a lahira ka tashi cikin masu tozarta zumunci."
"Kiyi hakuri, nasan nayi kuskure amma zan gyara in sha Allahu. Na rasa abin da yake damuna ni kaina"
Duk da ranta a bace yake amma taji dadi yau ya nuna damuwarsa garesu
"Ka tashi ka tafi ya wuce"
"Asibiti zan kaiki saboda idon. Shi kuma zai gamu dani wallahi."
A fusace ya fita daga dakin. Rumana da take tsaye a gefe yace mata daga yau ta rinka fitowa da Maamu falo suna shan iska baya son suna kulle kansu. Dakin yaran ya wuce Gimbi tana tambayarsa me zaiyi da wayar chaja bai kulata ba sai gani tayi ya fara laftawa Mu'allim dan shekara bakwai a jikinsa. Yana dukansa duk ya cika gidan da ihu Gimbi ta kasa karbar chajar sai ma rabonta data samu a baya.
Maamu tana jinsu ta kwanta abin ta. Bata kin jikokinta amma ta kula da yadda suka bi sahun babarsu wurin banzatar dasu a gidan. Ranar Awaisu da Gimbi barambaram akayi babu mai kula dan uwansa tun bayan da ya gama hukunta Mu'allin tare da ja mata kunne sosai akan Maamu.
Da safe a motarsa suka dauki Rumana zuwa makaranta ya bata dubu biyar yace ta ajiye sauran a gida. Yaso kai Maamu asibiti ma tace ta warke.
*****
Gimbi tana fita da suka kai yara makaranta gidan Anti Bebi ta wuce. Tana kuka ta fada mata irin dukan da Awaisu yayiwa Mu'allim. Gashi tana ganin kamar maganin ya fara sakinsa.
"Ni dai kawai kizo muje gidan Wangesi kada komai ya lalace min"
"Gimbi kenan wato mugu baya so a dandana masa zumarsa sai ya birkice. Don yau daya anyi miki meye na fushi. Can wurin aikin naki fa?"
"Ni dai kawai kizo muje zan san karyar da zanyi musu"
Ko mijinta bata sake lekawa ba ta dauko dan gyalenta suka fice. Gimbi ta sallami nata dreban suka wuce da dan koran Anti Bebi. Wangesi ya bata wasu kwayaye guda hudu duk anyi musu zane da jar tawwada da wasu layu da kulle kullen magani. Komai yayi mata bayanin yadda zata yi amfani dashi ta kawo kudi ta ajiye masa.
Suna komawa gida ta wuce. Kwai daya a kofar dakin Awaisu ta fasa shi ta rufe da door mat. Sauran biyun kuma daya a bayan dakin Maamu dayan kuma ta dafa shi ta cinye.
Da ta gama ta dauki motarta ta koma gidan Anti Bebi sai lokacin tashin yara ta dawo. Manajan bankin da take ya kira Awaisu kan cewa yayi mata magana akan fashi da rashin zuwa da wuri ko kuma fita kafin a tashi. Don ma yana ganin kimarsa ne da tuni ya bata takardar jan kunne.
Hakuri ya bashi tare da godiya. Yana dawowa ya hauta da fadan sai ta gaya masa inda take zuwa. Ta rasa amsar da zata bashi. Abincin da ta zuba rabin maganin kuma yaki ci. Daren ranar yaransa yasa a gaba suka taya Maamu da Rumana hira a falo.
Gimbi kuwa Anti Bebi ta kira tana kuka Wangesi ya ci kudinta a banza.
"Kin fiye wutar ciki. Haka aka ce miki asirin yana kama mutane kamar a fim? A hankali zai cinye shi ya dawo miki tamkar sakarai shashasha"
Tsaki tayi ta ajiye wayar. Ita Anti Bebi bata da aiki sai fadin bakar magana. Awaisunta ba sakarai bane ta fada a zuci tana huci ita kadai.
Sai bayan sati ta kula ya fara sanyi fiye da yadda yayi a baya ma. Sa idonsa akan lamarin su Maamu da suka fara shanawa yanzu babu.
Gidan jiya aka koma inda take horasu da yunwa wai don kada suji dadin gidan su cigaba da zama.13*KASHE FITILA*💡14
*Batul Mamman*💖
*Bayan Sati Uku*
Zaune take gaban madubi tana kwalliya taji kamar ana kiranta. Jagirar hannunta ta ajiye ta fito daga dakin tare da leka falon ta saman bene. Mijinta ne ya shigo rai a bace sai huci yake.
"Shuhada kina ina ne?"
Saurin saukowa tayi har tana hada bene biyu a lokaci daya
"Me ya faru T?"
Mugun kallo ya bita dashi kafin yayi magana "kizo ki fice daga gidan nan na sakeki"
Ji tayi kamar an sakar mata guduma a tsakiyar kanta
"Ka sakeni? T kalmar saki fa ba kalmar wasa bace"
Idanunsa kara rinewa sukeyi suna yin ja saboda bacin ran da ya rasa dalilinsa.
"Ni zaki rainawa hankali, to zamana dake ya kare. Ki tattara ki fita kafin kiji hannuna a jikinki"
Shuhada rasa bakin magana tayi. Anya mijin nata hankalinsa daya kuwa. Ya fita suna farinciki da juna. Me ya kawo wannan chanji haka. Dan matsawa tayi kusa dashi
"T ka zauna don Allah muyi magana. Na rasa gane abin da yake faruwa. Abokanka sun baka wani abu ne kasha da baka sani ba?"
Saukar mari taji har biyu "kina nufin ina shaye shaye ne."
Dafe kuncinta tayi tana kuka "Tajuddeen kana cikin hankalinka kuwa. Nice fa, me nayi maka haka"
Girgiza kai yayi yana yamutsa fuska "tsanarki kawai nayi S. And I want you to get out now kafin raina ya kara baci"
Kuka ne sosai yaci karfinta. Gabadaya kwakwalwarta ta toshe. Mutum ya fita lafiya ya dawo a birkice. Ba karamin so yake nuna mata ba tun kafin aurensu har zuwa yanzu da suka sami shekara daya tare. Gani tayi ya hau sama ya fara cillo mata kayanta ta saman bene. Lallai da gaske yake. Tana kallo ya gama ya sauko ya bude wallet dinsa. Kudi ya debo ya watsa mata a fuska.
"Now get out"