Sashe 8
Ibtihal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mutuwar malam mutari ta matuƙar girgiza Hajara tare da wasu ƙalilan daga cikin ƴaƴansa saɓanin sauran da murnar hakan sukayi tare da mugayen matansa,
Alhaji Marzouq ma yayi matuƙar jin mutuwar aminin nasa saida ya yi kwana ukku duk wani abu da akaci a zaman makokin shi ya ɗauki nauyin komai,ya lallashi Hajara sosai akan tayi haƙuri ta ɗauki ƙaddara wanda da zai tafi da kuka suka rabu da jikan nasa saboda kusan duk sati biyu daman sai ya zo ganinsa shi da malam mutari hakan ya sa ya saba dashi dukda yaron ya taso ba ba me son magana ba,
Ranar da malam ya cika kwana bakwai da mutuwa sukace a raba gado kowa ya kama gabansa a washegari ne abun mamaki saiga Malek ya zo musu ta’aziya wanda hajara ta tabbatar tirsasawar mahaifinsa ne,
Tunda ya zo idonsa akan yaron amma ya kasa cewa komai da zai tafi ya miƙawa hajara takarda tare da tafiya abunsa wamda ta na buɗewa ta ga takardar saki ukku ce ta ji ba daɗi amma ta wani ɓangaren taji daɗin hakan ko ba komai ya raba ta da nauyin auren sa da bata san matsayinsa ba,
An raba gado anba kowa nasa wanda manyan mazan ƴaƴan haule duk suka handame gonaki da sauran kadarorin malam bisa zalunci wanda hakan ya haifar da gagarumin tashin hankali tsakaninsu don marariya da ƴaƴanta sukace basu yarda ba nan aka dinga rigimgimu a ƙarshe dai ba yanda suka iya dole suka haƙura ita daman hajara ƴar kallo ce domin raɗaɗin mutuwar mahaifinta ce kawai a ranta ta ƙara zama shiru-shiru akan da an raba gado wanda ita saidai ma tace an sammata wani fegi ƙwara ɗaya aka bata wanda ita kanta tasan manya manyan gonakin malam sunfi Ashirin banda gidaje da feguna da rumbunan kayayyakin gona batace komai ba domin ba dukiya ba ce a gabanta,.
Nan fa sukace dole zata bar musu gida domin bata da gado a gidan ranar hajara ta yi kukan da bata taɓa irin sa ba ranar ta san yanda rayuwar maraici take ta na ji ta na gani aka rabata da gidan ubanta korar wulaƙanci da ƙasƙanci da ita da yaronta a ranar rasa wajen kwana tayi ƴan uwanta aurarru a gari dukkaninsu ta je gidansu akan su taimaketa da wajen kwana na yau ɗaya kafin gobe tayi shawarar wajen zuwa amma suka hanata ranar sai a tashar mota ta kwana washegari sanin bata da mafita ga ba kuɗi hannunta hakan ya sanya ta je ta nemu dillalai ta sayar da ƙaramun fegin gadon ta ganin a gaggauce take akayi mata cinikin wulaƙanci ta na buƙatar kuɗi hakan ya sa dole ta haƙura ta sayar ta amsa kuɗin.
tunanin wajen zuwa ta ke kawai hakanan zuciyar ta bata da ta tafi Kaduna domin lokacin da tayi karatu a zaria suna ɗan zuwa kaduna haka nan tsarin garin da yanda mutanen garin ke mu’amulansu ya matuƙar burgeta domin bata da mafitar da ya wuce haka indai ta na neman rufin asirinta da na ɗanta ranar sai sha ɗayan dare ta isa garin Kaduna,
A ranar ma a tashar mota ta kwana in taƙaita miki labarin ƴata domin ya na da yawa hajara ta yi mabanbanta sana’oi anan Kaduna domin rufawa kanta asiri Dukda ta sha fama saboda kyawunta amma haka ta tsare mutuncinta da na ɗanta aikatau ne a gida je kawai batayi ba amma sana’a wankau ,guga ,Ba irin sana’ar da batayi ba domin a ƙuɗaɗen da tazo da shi ta kama hayar ɗaki ɗaya a wani gida su bakwai sauran kuɗin kuma ta fara juyawa,
rayuwa na tafiya da daɗi ba daɗi kullum cikin faɗi tashin neman halak take dukda irin gidan da take amma bata shiga harkar kowa haka shima Marzouq ya taso da ƙwazo tun ya na shekara Shida ya san neman na kansa tun hajara na masa faɗa har ta haƙura shi ne sayar da bread,Sayar da pure water tashar mota duk don ya taimakawa mahaifiyarsa domin duk lokacin da yaga ta na wahalar nan ya najin Ɗaci a cikin ransa .
watarana kwatsam hajara ta ji sanarwa a gidan radio akan ana neman masu takardun karatu tundaga masu sakandire har zuwa ,Digiri duk wani mai takardun ya zo ana nemansa a sakateriya ranar litinin”
Ba tare da tunanin zata samu ba haka nan dai ta je ta kai takardunta domin daman suna tare da ita sam wahala ta ma mantar da ita tayi wani karatu,
Allah mai iko sai gashi fitowar farko ta samu aiki domin lokacin masu irin takardunsu ake nema basu da yawa bare ita da takardarta tayi mugun kyau,
Ranar da ta amsa offer ɗinta a hannu tayi matuƙar murna da farinciki ta godewa Allah babu iyaka ,
Ta fara aikinta cikin nasara da kwarewa a wata makarantar sakandire,
Mace ce mai kwazo da ta saba da nema ko da ta samu aiki sai sana’arta ta ƙara bunƙasa ta dinga sarin atamfofi,shaddoji,Takalma,yadika,ta na rabawa sauran ma’aikata da anyi albashi su haɗa mata kuɗinta gefe guda ta na kula da karatun ɗanta da ta sauya masa makaranta ta maida sa ta kuɗi mai kyau.
Lokacin da Marzouq ya gama sakandire Hajara ba ƙaramun cigaba ta samu ba ta saya gida ta saya mota hakan ya sa ta buɗewa Marzouq shagon atamfofi da shaddoji da yadika ganin ya zama saurayi kafin Result ɗinsu ya fito ta sama masa Addmission ya fara sana’a ,
dukda yanda ƴan mata suka masa chaaa saboda ganin kyakyawan saurayi ɗan ƙwalisa ba ya kula kowa kamar yanda ya ke shiru shiru in kaga dariyarsa da fara’arsa ko maganarsa doguwa to da mahaifiyarsa ne Kallo ɗaya zakayi masa kasan akwai abu a ransa domin mahaifiyarsa ba ta ɓoye masa komai ba game da tarihinsa da nata baice komai ba amma tana ganin tsananin tsanar mahaifinsa a ransa ba irin yanda batayi ba akan ya shirya ta kaisa wajen Kakansa saboda halin rayuwa idan itace yau ba itace gobe ba amma fir ya ƙiya hakanan ta haƙura domin ita ɗinma kanta bazatace ga inda gidan kakan nasa yake ba domin duk zaman da tayi bata taɓa zuwa koda sau ɗaya ba ta aje batun a gefe dukda a ranta ba ta manta halaccin Alhaji Marzouq a garesu ba.
*MARZOUQ MALEK*
Shine sunan da ake kiransa a makaranta dukda baya son haɗa sunansa da malek da ake haɗasa ya so sunan kakansa na wajen uwa aka sanya masa amma fir hajara ta ƙiya saboda darajar kakansa ,
Sosai take samun cigaba a wajen aiki gefe guda marzouq na kula da shagon da ta buɗe masa,
A haka jarabawarsu tayi kyau haka Jamb Ɗinsa yayi mugun cin da saida aka gayyacesa interview bayan angama masa aka tabbatar da eh yaron da gaske shi ya ci yaro ne mai matuƙar ƙwazo a cikin wanda sukayi masa interview din akwai wani DR NAZIR wanda tunda ya ɗora idonsa akan yaron ya ji ya matuƙar burgesa sannan ya na ganin kamar akwai Kamannin Hajara a fuskar yaron wanda ya kasa mantata har yanzu……..✍🏽
_*Miss Hajo ce*_🤙🏿
🪅*IBTIHAL*🪅
~MALLAKAR~
*HAJARA L SADEQ*
(miss Hajo)
MARUBUCIYAR👇🏼
Auren wata tara
Ni da yaya arman
Matar uncle
Najmat abiy
Komai mukaddari ne
Khadijatul Sabren
Ribar so
Mata ta ce
*And now*
*IBTIHAL*
*DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI 07026166536*
*DEAZATOH Tawa ƴar amana shafin nan naki ne kyauta Alkhairin Allah ya kai maki har gadon baccinki nasara ta lulluɓe rayuwarki yakawo mana twins mu zo Kd shan suna*😘😘😘😘
*DEDICATED TO MY HUSBAND*
🅿️…………………………..*07*
A lokacin Dr Nazir ya basa number sa saboda lokacin waya ta zo har ta ɗan fara wadata akan in yana buƙatar wani taimako ya tuntuɓesa zai taimaka masa sosai insha Allah shima ya amsa number sa,
A hankali shaƙuwa ta shiga tsakaninsa da DR Nazir ya zame masa tamkar uba mai basa shawara zuwa lokacin Hajara ba ta taɓa haɗuwa da DR nazir ba ta na jin dai labarinsa a wajen ɗanta da yanda ya ke basa shawarwari akan karatunsa.
kwatsam rana ɗaya DR nazir ya kira Marzouq akan ya sama masa Schoolership a Ƙasar Switzerland koda Marzouq ya zowa da hajara da labarin rumgumesa ta yi ta na masa kukan farinciki shi a ransa baya son tafiyar domin baya son abunda zaiyi nisa da shi da mahaifiyarsa amma ganin yanda ta nuna farincikin ta akan hakan sai yaji ƙwarin gwuiwar hakan.
Dole hajara ta buƙaci da ya kaita har gidan DR Nazir ɗinnan dai yau tayi masa godiya ,
ya rakata har gidan wanda lokacin da sukayi ido da juna ba ƙaramun mamaki ne ya kama su ba ganin juna Hajara ta nuna sa ta ce Nazir shima ya na nunata da zallar mamaki ya ce Hajara Daman zan sake ganinki ,
sai gani sukayi suna hawaye Marzouq ya tsaya kallon ikon Allah ya na mamakin sanda suka san juna ,
Hajara kuka ta sa domin bata taɓa tunanin sake ganin Nazir a rayuwarta ba dukda duk shekarun nan bata manta da shi ba da irin soyayyar da sukayi a lokacin ne ya ke sanar mata kamar yanda suka tsara kafin ta bar makaranta don tun lokacin bayan sati ukku ya je tare da iyayensa har wajen mahaifinta kamar yanda ta kwatanta masa aka shaida musu ta yi aure ranar ya yi kukan da baitaba irinsa ba ya yi jinyar watanni kafin mahaifinsa ya basa haƙuri ya haɗasa Aure da ƴar uwarsa daman kuma ta na sonsa shima kuma ya haƙura ya amsheta hannu bibbiyu ta haifa masa yara biyu duk Maza Ashraf da Sadeq kafin shekara ukku baya Allah yayi mata rasuwa sanadin ciwon Hanta,
Alhaji Marzouq ma yayi matuƙar jin mutuwar aminin nasa saida ya yi kwana ukku duk wani abu da akaci a zaman makokin shi ya ɗauki nauyin komai,ya lallashi Hajara sosai akan tayi haƙuri ta ɗauki ƙaddara wanda da zai tafi da kuka suka rabu da jikan nasa saboda kusan duk sati biyu daman sai ya zo ganinsa shi da malam mutari hakan ya sa ya saba dashi dukda yaron ya taso ba ba me son magana ba,
Ranar da malam ya cika kwana bakwai da mutuwa sukace a raba gado kowa ya kama gabansa a washegari ne abun mamaki saiga Malek ya zo musu ta’aziya wanda hajara ta tabbatar tirsasawar mahaifinsa ne,
Tunda ya zo idonsa akan yaron amma ya kasa cewa komai da zai tafi ya miƙawa hajara takarda tare da tafiya abunsa wamda ta na buɗewa ta ga takardar saki ukku ce ta ji ba daɗi amma ta wani ɓangaren taji daɗin hakan ko ba komai ya raba ta da nauyin auren sa da bata san matsayinsa ba,
An raba gado anba kowa nasa wanda manyan mazan ƴaƴan haule duk suka handame gonaki da sauran kadarorin malam bisa zalunci wanda hakan ya haifar da gagarumin tashin hankali tsakaninsu don marariya da ƴaƴanta sukace basu yarda ba nan aka dinga rigimgimu a ƙarshe dai ba yanda suka iya dole suka haƙura ita daman hajara ƴar kallo ce domin raɗaɗin mutuwar mahaifinta ce kawai a ranta ta ƙara zama shiru-shiru akan da an raba gado wanda ita saidai ma tace an sammata wani fegi ƙwara ɗaya aka bata wanda ita kanta tasan manya manyan gonakin malam sunfi Ashirin banda gidaje da feguna da rumbunan kayayyakin gona batace komai ba domin ba dukiya ba ce a gabanta,.
Nan fa sukace dole zata bar musu gida domin bata da gado a gidan ranar hajara ta yi kukan da bata taɓa irin sa ba ranar ta san yanda rayuwar maraici take ta na ji ta na gani aka rabata da gidan ubanta korar wulaƙanci da ƙasƙanci da ita da yaronta a ranar rasa wajen kwana tayi ƴan uwanta aurarru a gari dukkaninsu ta je gidansu akan su taimaketa da wajen kwana na yau ɗaya kafin gobe tayi shawarar wajen zuwa amma suka hanata ranar sai a tashar mota ta kwana washegari sanin bata da mafita ga ba kuɗi hannunta hakan ya sanya ta je ta nemu dillalai ta sayar da ƙaramun fegin gadon ta ganin a gaggauce take akayi mata cinikin wulaƙanci ta na buƙatar kuɗi hakan ya sa dole ta haƙura ta sayar ta amsa kuɗin.
tunanin wajen zuwa ta ke kawai hakanan zuciyar ta bata da ta tafi Kaduna domin lokacin da tayi karatu a zaria suna ɗan zuwa kaduna haka nan tsarin garin da yanda mutanen garin ke mu’amulansu ya matuƙar burgeta domin bata da mafitar da ya wuce haka indai ta na neman rufin asirinta da na ɗanta ranar sai sha ɗayan dare ta isa garin Kaduna,
A ranar ma a tashar mota ta kwana in taƙaita miki labarin ƴata domin ya na da yawa hajara ta yi mabanbanta sana’oi anan Kaduna domin rufawa kanta asiri Dukda ta sha fama saboda kyawunta amma haka ta tsare mutuncinta da na ɗanta aikatau ne a gida je kawai batayi ba amma sana’a wankau ,guga ,Ba irin sana’ar da batayi ba domin a ƙuɗaɗen da tazo da shi ta kama hayar ɗaki ɗaya a wani gida su bakwai sauran kuɗin kuma ta fara juyawa,
rayuwa na tafiya da daɗi ba daɗi kullum cikin faɗi tashin neman halak take dukda irin gidan da take amma bata shiga harkar kowa haka shima Marzouq ya taso da ƙwazo tun ya na shekara Shida ya san neman na kansa tun hajara na masa faɗa har ta haƙura shi ne sayar da bread,Sayar da pure water tashar mota duk don ya taimakawa mahaifiyarsa domin duk lokacin da yaga ta na wahalar nan ya najin Ɗaci a cikin ransa .
watarana kwatsam hajara ta ji sanarwa a gidan radio akan ana neman masu takardun karatu tundaga masu sakandire har zuwa ,Digiri duk wani mai takardun ya zo ana nemansa a sakateriya ranar litinin”
Ba tare da tunanin zata samu ba haka nan dai ta je ta kai takardunta domin daman suna tare da ita sam wahala ta ma mantar da ita tayi wani karatu,
Allah mai iko sai gashi fitowar farko ta samu aiki domin lokacin masu irin takardunsu ake nema basu da yawa bare ita da takardarta tayi mugun kyau,
Ranar da ta amsa offer ɗinta a hannu tayi matuƙar murna da farinciki ta godewa Allah babu iyaka ,
Ta fara aikinta cikin nasara da kwarewa a wata makarantar sakandire,
Mace ce mai kwazo da ta saba da nema ko da ta samu aiki sai sana’arta ta ƙara bunƙasa ta dinga sarin atamfofi,shaddoji,Takalma,yadika,ta na rabawa sauran ma’aikata da anyi albashi su haɗa mata kuɗinta gefe guda ta na kula da karatun ɗanta da ta sauya masa makaranta ta maida sa ta kuɗi mai kyau.
Lokacin da Marzouq ya gama sakandire Hajara ba ƙaramun cigaba ta samu ba ta saya gida ta saya mota hakan ya sa ta buɗewa Marzouq shagon atamfofi da shaddoji da yadika ganin ya zama saurayi kafin Result ɗinsu ya fito ta sama masa Addmission ya fara sana’a ,
dukda yanda ƴan mata suka masa chaaa saboda ganin kyakyawan saurayi ɗan ƙwalisa ba ya kula kowa kamar yanda ya ke shiru shiru in kaga dariyarsa da fara’arsa ko maganarsa doguwa to da mahaifiyarsa ne Kallo ɗaya zakayi masa kasan akwai abu a ransa domin mahaifiyarsa ba ta ɓoye masa komai ba game da tarihinsa da nata baice komai ba amma tana ganin tsananin tsanar mahaifinsa a ransa ba irin yanda batayi ba akan ya shirya ta kaisa wajen Kakansa saboda halin rayuwa idan itace yau ba itace gobe ba amma fir ya ƙiya hakanan ta haƙura domin ita ɗinma kanta bazatace ga inda gidan kakan nasa yake ba domin duk zaman da tayi bata taɓa zuwa koda sau ɗaya ba ta aje batun a gefe dukda a ranta ba ta manta halaccin Alhaji Marzouq a garesu ba.
*MARZOUQ MALEK*
Shine sunan da ake kiransa a makaranta dukda baya son haɗa sunansa da malek da ake haɗasa ya so sunan kakansa na wajen uwa aka sanya masa amma fir hajara ta ƙiya saboda darajar kakansa ,
Sosai take samun cigaba a wajen aiki gefe guda marzouq na kula da shagon da ta buɗe masa,
A haka jarabawarsu tayi kyau haka Jamb Ɗinsa yayi mugun cin da saida aka gayyacesa interview bayan angama masa aka tabbatar da eh yaron da gaske shi ya ci yaro ne mai matuƙar ƙwazo a cikin wanda sukayi masa interview din akwai wani DR NAZIR wanda tunda ya ɗora idonsa akan yaron ya ji ya matuƙar burgesa sannan ya na ganin kamar akwai Kamannin Hajara a fuskar yaron wanda ya kasa mantata har yanzu……..✍🏽
_*Miss Hajo ce*_🤙🏿
🪅*IBTIHAL*🪅
~MALLAKAR~
*HAJARA L SADEQ*
(miss Hajo)
MARUBUCIYAR👇🏼
Auren wata tara
Ni da yaya arman
Matar uncle
Najmat abiy
Komai mukaddari ne
Khadijatul Sabren
Ribar so
Mata ta ce
*And now*
*IBTIHAL*
*DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI 07026166536*
*DEAZATOH Tawa ƴar amana shafin nan naki ne kyauta Alkhairin Allah ya kai maki har gadon baccinki nasara ta lulluɓe rayuwarki yakawo mana twins mu zo Kd shan suna*😘😘😘😘
*DEDICATED TO MY HUSBAND*
🅿️…………………………..*07*
A lokacin Dr Nazir ya basa number sa saboda lokacin waya ta zo har ta ɗan fara wadata akan in yana buƙatar wani taimako ya tuntuɓesa zai taimaka masa sosai insha Allah shima ya amsa number sa,
A hankali shaƙuwa ta shiga tsakaninsa da DR Nazir ya zame masa tamkar uba mai basa shawara zuwa lokacin Hajara ba ta taɓa haɗuwa da DR nazir ba ta na jin dai labarinsa a wajen ɗanta da yanda ya ke basa shawarwari akan karatunsa.
kwatsam rana ɗaya DR nazir ya kira Marzouq akan ya sama masa Schoolership a Ƙasar Switzerland koda Marzouq ya zowa da hajara da labarin rumgumesa ta yi ta na masa kukan farinciki shi a ransa baya son tafiyar domin baya son abunda zaiyi nisa da shi da mahaifiyarsa amma ganin yanda ta nuna farincikin ta akan hakan sai yaji ƙwarin gwuiwar hakan.
Dole hajara ta buƙaci da ya kaita har gidan DR Nazir ɗinnan dai yau tayi masa godiya ,
ya rakata har gidan wanda lokacin da sukayi ido da juna ba ƙaramun mamaki ne ya kama su ba ganin juna Hajara ta nuna sa ta ce Nazir shima ya na nunata da zallar mamaki ya ce Hajara Daman zan sake ganinki ,
sai gani sukayi suna hawaye Marzouq ya tsaya kallon ikon Allah ya na mamakin sanda suka san juna ,
Hajara kuka ta sa domin bata taɓa tunanin sake ganin Nazir a rayuwarta ba dukda duk shekarun nan bata manta da shi ba da irin soyayyar da sukayi a lokacin ne ya ke sanar mata kamar yanda suka tsara kafin ta bar makaranta don tun lokacin bayan sati ukku ya je tare da iyayensa har wajen mahaifinta kamar yanda ta kwatanta masa aka shaida musu ta yi aure ranar ya yi kukan da baitaba irinsa ba ya yi jinyar watanni kafin mahaifinsa ya basa haƙuri ya haɗasa Aure da ƴar uwarsa daman kuma ta na sonsa shima kuma ya haƙura ya amsheta hannu bibbiyu ta haifa masa yara biyu duk Maza Ashraf da Sadeq kafin shekara ukku baya Allah yayi mata rasuwa sanadin ciwon Hanta,