Sashe 13
Ibtihal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abba ya lallasheta daƙyal ya samu ta yi shiru Aunty Salma ta kwana da ita wanda har zuwa lokacin ba ta Farka ba Ita kanta Aunty salma Hankalinta a mugun tashe yake da samun wannan sabon Labarin haka Safa don kuka ta dingayi daƙyal ta bi Hajiya da su Abba gida don cewa tayi ita ma nan zata kwana,Yusuf ko ya kasa zaune ya kasa Tsaye.
Wasa-wasa washegari har 1:30 Ibtihal ba ta farfaɗo ba Dukkanin ƴan uwanta hankalinsu a matuƙar tashe yake sanin halin rayuwa ya sanya Abba Kiran mom cikin hikima ya sanar da ita idan babu damuwa ta zo ƙasar ko yau ta samu jirgi ta taho,
Hankalin mom ya matuƙar tashi wanda tun a wayar ta ke tambayar wa ya mutu don Allah kar a Ɓoye mata Abba ya ce ba mutuwa ba ce ya lallashe daƙyal,
Ga mamaki har daren ranar Ibtihal ba ta farfaɗo ba wanda su kansu likitocin abun ya fara tsorata su sai ta kai sun sauya mata waje sun maida ta inda ba a barin kowa shiga saidai leƙe duk an zagayeta da na’ouroori,
Safa da ke gefen Mamanta ta ɗora kanta kafaɗarta ta na hawaye itama aunty salmar daurewa ta ke ta na lallashinta lokacin ne mom ta kira aunty salma ta yi
mamakin ganin number ta ta Nigeria bayan ta ɗauka ta ce,
“salma me ke faruwa munzo gidan Hajiya ba kowa Mai gadi ke sanar mun kuna asibiti wanne asibitin me ya samu Hajiyar innalillahi wa inna ilaihiraji’un”
Aunty salma ta ce “Kinga Aunty Nafisa ki kwantar da hankalinki ga Marwan nan yanzu zaizo ya ɗaukeku ya kawoku asibitin”
Suna gama wayar marwan ya tafi ɗauko su mom cikin mintuna Ashirin sai ga su su ukku Ka na kallon mom zaka san tabbas jinin Ibtihal ce domin kamanninsu sun ɓaci baka taɓa cewa mom ta haifi kamar ibtihal,kyakyawa ƴar gayu mai matsakaicin jiki sai wata Matashiyar kyakyawar budurwa wacce zatayi sa’anni da Ibtihal Ta na Riƙe da wata kyakyawar yarinya da tayi bacci ta kwanta a kafaɗarta daga bayansu kuma wata dattijuwa a ƙalla tayi shekaru hamsin itama fara mai kama da su mom sai yanzu na lura tundaga kan su har Aunty salma kamar su ɗaya haka yaransu duk suna kamannin juna saidai wani yafi wani kyawu,
Kamar mom zatayi gudu ta rigo ba wajen da ta nufa sai hajiya da ke zaune ta yi tagumi ta rungumeta ta na Sauke ajiyar zuciya ta ce “Alhamdulillahi da na sameki Lafiya Hajiyata “
kafin ta sauke nauyayyar ajiyar zuciya hajiya ta shafa bayanta ta na rungumeta kafin ta tsagaita itama aunty Aisha haka ta zo ta rungume Hajiya duk suna sauke ajiyar zuciya Safa ce ta yi saurin Amsar Afren da har lokacin ta ke sharar baccin gajiya,
nan aka ɗan gaggaisa sama-sama don hankalin kowa ba jikinsa ya ke ba mom ce hankalinta ya yi tsananin tashi ganin ta ga kowa banda ibtihal hankali tashe ta kalli hajiya ta ce”Hajiya wa ye ba lafiya”
Hajiya na kama hannunta cikin sigar lallashi ta ce “bana son ki ɗaga hankalinki kinji Ibtihal ce amma insha Allah za ta samu sauƙi nan kusa”
Wani irin faɗuwa gaban mom ya yi ta ce “innalillahi Hajiya me ya sameta”
daidai likita na ƙarasowa wajen fuskarsa kawai za ka kalla ka san akwai damuwa ya ce”muna buƙatar mutum biyu makusanta *IBTIHAL ADAM* ya na gama faɗar haka ya koma office ɗinsa daidai Abba ya bisa da sauri tare da Aunty salma,
Damuwa ƙarara a fuskar Dr Najib bayan sun zauna ya ce “Alhaji magana ce ta gaggawa muna buƙatar jini a gaggauce domin yarinyar na buƙatar jini kuma mun gwada jininta O Negative ne wanda cikin kashi ɗari masu irinsa basu da yawa idan akwai mai irinsa a dangi a bincika da gaggawa”
“Innalillahi wa inna ilaihiraji’un Aunty salma ta faɗa hawaye na siraro mata saboda dukkaninsu sun san Kaf Babu mai irin jininta a Family Ɗinsu dukkaninsu mafi yawaici O Possitive ne “
Abba ya ce”Dr Babu yanda za ayi kaf family ɗinmu ita kaɗai ce mai irin jinin nan ko nawa ne zan kashe tunda nasan kuna ɗaukar number masu irin jinin saboda irin haka ta kama don Allah a taimaka a ceci ran Ƴata”
Dr ya ce “innalillahi wa inna ilaihiraji’un Wallahi Alhaji Mutum biyu ne idan irin haka ta kama suke bayarwa ko ba a nema ba suna zuwa da ansha watanni a Ɗauka na farko *SANATA MARZOUQ MALEK* sai Alhaji Bukar to shi Alhaji bukar ya na ma garinsu yanxu haka Allah yayiwa mahaifinsa. Rasuwa shi sanin da nayi Alhaji Marzouq ba ya Ƙasar sauran waɗanda kuma muke da su mutum ukku ne kuma duk mata kaga bazaiyu ba”
Hawaye na xuba idanun Aunty salma ta ce “Shikenan yanzu Dr zamu rasa ƴarmu babu wata mafita”
Dr na shirin Magana Wata Nurse ta shigo fuskarta washe cike da girmamawa ta ce “Dr Munyi babban Baƙo Sanata Marzouq ne ya zo duba marasa lafiya kamar yanda ya saba zuwa lokaci zuwa lokaci”
Dr ya sauke wata nauyayyar ajiyar zuciya ya na miƙewa da zallar farinciki ya fice Abba da Aunty Salma suka bi bayansa suma cikin sauri”
Lokacin ne wani kyakyawan matashi ke shigowa cikin taku irin na Hamshaƙan maza Fari ne ba Kal ba kyakyawa ajin farko wanda ko ɗan uwansa namiji ya kallesa dole ya ƙara kalla ballantana ƴan matan wannan zamani,
Dukda kasancewar sanye ya ke cikin manyan kaya farar tsadaddar shaddar da tayi masifar yimasa kyau Sajen nan nasa kallo ɗaya zaka masa kasan na musamman ne masu irinsa ƙalilan ne kodan ya danganta da gyaran da suke samu ,
idanunsa sanye cikin wani farin tsadadden glass da ya ƙara ƙawata baiwar kyawunsa kansa sanye da hula da ta dace da kayansa takalman ƙafafunsa kaɗai ya isa kayi ƙauyanci sam yanda gayu da tsabta gami da kyan jiki ya ratsa sa baka taɓa ɗaukar ya kai shekaru Arba’in zaka ɗauka bazai wuce 35yrs ba ya yi wuta,
Gaba Ɗaya wajen karaɗewa ya yi da daddaɗan ƙamshin turarensa mai matuƙar daɗi da sanyin shaƙa,
“Ranka ya daɗe barka da zuwa”
Dr ya faɗa cike da girgimamawa har ya na haɗawa da russunawa bayan ya basa hannu sukayi musabaha Cikin daddaɗan muryarsa mai cike da miskilanci da rashin son magana ya ce”ya masu jiki”
Muryar sam ba ta ma fita,
Dr ya ce “masu jiki alhamdulillahi ranka ya daɗe ya fama da jama’a “ya faɗa suna yin gaba don masa jagora kamar ko yaushe idan yazo duba marasa lafiya.
Daidai lokacin Abba na ƙarasa zowa wajen da murmushin nuna sanayya ya nufi wajensu tare da cewa”Sanata Marzouq”
Cike da ladabi marzouq ya miƙawa Abba hannu ya ce “ranka ya daɗe barka da yamma”
Ya ce “A ah saidai muce ranmu ya daɗe tare “duk sukayi murmushi Abba ya ce”Ya majalissar kwana biyu ba a ganinka”
Ya ce “Na yi tafiya ne Ɗazu ba jimawa dawowata Ƙasar”
Abba ya ce”Allah ya taimaka “
Duk suka ɗunguma har Abba Bayan securityn Marzouq ya dakatar da su .
Ɗaya bayan ɗaya duk gadon da yaje ya musu ya jiki sai ya aje musu bandir kudaɗe masu yawan gaske suna gaba ya na tambayar Dr akwai issue na Aiki waɗanda ba su da hali”
Dr ya ce”Eh akwai na mutane huɗu mararsa ƙarfi yanzu dai akwai issue mai girma ranka ya daɗe na irin taimakon da kakeyi Yarinyar Sanata Bashir Dikko ce ke buƙatar jini kuma jinin irin naka ne an bincika kaf ba a samu ba har ma mun cire rai da rayuwar yarinyar sai gashi Allah ya kawo mana kai”
Cikin sauri ya kalli Dr ya ce “Subhanallah ai abunda ya dace ayi tun farko meyasa ba ka faɗa da wuri ba ayi sauri muje a ɗauka”
Cikin ƙalilan mimtuna akayi masa text ɗin duk da ya dace aka tabbatar ba matsala tattare dashi kafin a ɗeba jinin leda Ɗaya da gaggauwa akaje aka maƙala mata Abba harda hawayen farinciki ya kama hannun Marzouq ya ce.
“Bani da bakin da zan gode maka bisa ceton rayuwar ƴata da kayi Sanata nagode Allah ya biya maka dukkanin buƙatun ka na Alkhairi ya ƙara maka nasara da ci gaba a dukkan al’amuranka kamar yanda na saba faɗa yau zan maomaita a gabanka *MARZOUQ MALEK* kai ɗin na musamman ne a cikin Al’umma ririnka basu da yawa a duniya”
Sam nauyin godiyar da Abba keyi masa yakeji don bai ɗauki hakan a wani babban abu ba “
Bayan ya huta Ya tashi ya na kallon Abba ya ce “ mu je na duba ƴar taka sai mu wuce”
Bisa jagorancin Dr tare da Abba suka nufa Ɗakin da Ibtihal ta ke kwance hannu ɗaya maƙale da ruwa ɗayan kuma maƙale da jinin da ya fara shiga jikinta”
Samun kansa ya yi da zuba mata ido fuskarta ta yi fayau kyawunta ya ƙara bayyana dukda kasantuwar idanunta na a rufe numfashinta ne kawai zai tabbatar maka da ta na raye wani irin tausayin halin da take ciki ne lokaci guda ya shige shi don duk wanda yasan marzouq ya san mutum ne mai tsananin tausayi minti ukku cikakke baiyi ba ya miƙawa Abba hannu sukayi musabaha ya ce “Allah ya bata lafiya yallaɓai “
Abba ya ce “Ameen ranka ya daɗe ina ƙara matuƙar godiya Allah y saka da mafificin alkhairi”
Suka fito tare momy da ke kuka jikin hajiya da ke ta lallashinta Abba ya kalla ya ce”ki kwantar da hankalinki Nafisa Allah ya kawo mana agajin gaggawar da bamu taɓa tsammani nan kusa ba yanzu haka An saka mata jinin insha Allah zata samu lafiya nan kusa sannan ciwon zuciya ma muna fatan zata rabu dashi gaba ɗaya da yardar Allah”
Da sauri ta ɗago ta ce “Yaya da gaske a ina aka samun jinin bayan an tabbatar da baza’a samesa nan kusa ba “
Ya nuna mata Marzouq da ya duƙa ya gaishe da hajiya cikin sauri momy na hawaye ta ce “mungode Allah ya saka da alkhairi ya biya maka buƙatunka na alkhairi”
Wasa-wasa washegari har 1:30 Ibtihal ba ta farfaɗo ba Dukkanin ƴan uwanta hankalinsu a matuƙar tashe yake sanin halin rayuwa ya sanya Abba Kiran mom cikin hikima ya sanar da ita idan babu damuwa ta zo ƙasar ko yau ta samu jirgi ta taho,
Hankalin mom ya matuƙar tashi wanda tun a wayar ta ke tambayar wa ya mutu don Allah kar a Ɓoye mata Abba ya ce ba mutuwa ba ce ya lallashe daƙyal,
Ga mamaki har daren ranar Ibtihal ba ta farfaɗo ba wanda su kansu likitocin abun ya fara tsorata su sai ta kai sun sauya mata waje sun maida ta inda ba a barin kowa shiga saidai leƙe duk an zagayeta da na’ouroori,
Safa da ke gefen Mamanta ta ɗora kanta kafaɗarta ta na hawaye itama aunty salmar daurewa ta ke ta na lallashinta lokacin ne mom ta kira aunty salma ta yi
mamakin ganin number ta ta Nigeria bayan ta ɗauka ta ce,
“salma me ke faruwa munzo gidan Hajiya ba kowa Mai gadi ke sanar mun kuna asibiti wanne asibitin me ya samu Hajiyar innalillahi wa inna ilaihiraji’un”
Aunty salma ta ce “Kinga Aunty Nafisa ki kwantar da hankalinki ga Marwan nan yanzu zaizo ya ɗaukeku ya kawoku asibitin”
Suna gama wayar marwan ya tafi ɗauko su mom cikin mintuna Ashirin sai ga su su ukku Ka na kallon mom zaka san tabbas jinin Ibtihal ce domin kamanninsu sun ɓaci baka taɓa cewa mom ta haifi kamar ibtihal,kyakyawa ƴar gayu mai matsakaicin jiki sai wata Matashiyar kyakyawar budurwa wacce zatayi sa’anni da Ibtihal Ta na Riƙe da wata kyakyawar yarinya da tayi bacci ta kwanta a kafaɗarta daga bayansu kuma wata dattijuwa a ƙalla tayi shekaru hamsin itama fara mai kama da su mom sai yanzu na lura tundaga kan su har Aunty salma kamar su ɗaya haka yaransu duk suna kamannin juna saidai wani yafi wani kyawu,
Kamar mom zatayi gudu ta rigo ba wajen da ta nufa sai hajiya da ke zaune ta yi tagumi ta rungumeta ta na Sauke ajiyar zuciya ta ce “Alhamdulillahi da na sameki Lafiya Hajiyata “
kafin ta sauke nauyayyar ajiyar zuciya hajiya ta shafa bayanta ta na rungumeta kafin ta tsagaita itama aunty Aisha haka ta zo ta rungume Hajiya duk suna sauke ajiyar zuciya Safa ce ta yi saurin Amsar Afren da har lokacin ta ke sharar baccin gajiya,
nan aka ɗan gaggaisa sama-sama don hankalin kowa ba jikinsa ya ke ba mom ce hankalinta ya yi tsananin tashi ganin ta ga kowa banda ibtihal hankali tashe ta kalli hajiya ta ce”Hajiya wa ye ba lafiya”
Hajiya na kama hannunta cikin sigar lallashi ta ce “bana son ki ɗaga hankalinki kinji Ibtihal ce amma insha Allah za ta samu sauƙi nan kusa”
Wani irin faɗuwa gaban mom ya yi ta ce “innalillahi Hajiya me ya sameta”
daidai likita na ƙarasowa wajen fuskarsa kawai za ka kalla ka san akwai damuwa ya ce”muna buƙatar mutum biyu makusanta *IBTIHAL ADAM* ya na gama faɗar haka ya koma office ɗinsa daidai Abba ya bisa da sauri tare da Aunty salma,
Damuwa ƙarara a fuskar Dr Najib bayan sun zauna ya ce “Alhaji magana ce ta gaggawa muna buƙatar jini a gaggauce domin yarinyar na buƙatar jini kuma mun gwada jininta O Negative ne wanda cikin kashi ɗari masu irinsa basu da yawa idan akwai mai irinsa a dangi a bincika da gaggawa”
“Innalillahi wa inna ilaihiraji’un Aunty salma ta faɗa hawaye na siraro mata saboda dukkaninsu sun san Kaf Babu mai irin jininta a Family Ɗinsu dukkaninsu mafi yawaici O Possitive ne “
Abba ya ce”Dr Babu yanda za ayi kaf family ɗinmu ita kaɗai ce mai irin jinin nan ko nawa ne zan kashe tunda nasan kuna ɗaukar number masu irin jinin saboda irin haka ta kama don Allah a taimaka a ceci ran Ƴata”
Dr ya ce “innalillahi wa inna ilaihiraji’un Wallahi Alhaji Mutum biyu ne idan irin haka ta kama suke bayarwa ko ba a nema ba suna zuwa da ansha watanni a Ɗauka na farko *SANATA MARZOUQ MALEK* sai Alhaji Bukar to shi Alhaji bukar ya na ma garinsu yanxu haka Allah yayiwa mahaifinsa. Rasuwa shi sanin da nayi Alhaji Marzouq ba ya Ƙasar sauran waɗanda kuma muke da su mutum ukku ne kuma duk mata kaga bazaiyu ba”
Hawaye na xuba idanun Aunty salma ta ce “Shikenan yanzu Dr zamu rasa ƴarmu babu wata mafita”
Dr na shirin Magana Wata Nurse ta shigo fuskarta washe cike da girmamawa ta ce “Dr Munyi babban Baƙo Sanata Marzouq ne ya zo duba marasa lafiya kamar yanda ya saba zuwa lokaci zuwa lokaci”
Dr ya sauke wata nauyayyar ajiyar zuciya ya na miƙewa da zallar farinciki ya fice Abba da Aunty Salma suka bi bayansa suma cikin sauri”
Lokacin ne wani kyakyawan matashi ke shigowa cikin taku irin na Hamshaƙan maza Fari ne ba Kal ba kyakyawa ajin farko wanda ko ɗan uwansa namiji ya kallesa dole ya ƙara kalla ballantana ƴan matan wannan zamani,
Dukda kasancewar sanye ya ke cikin manyan kaya farar tsadaddar shaddar da tayi masifar yimasa kyau Sajen nan nasa kallo ɗaya zaka masa kasan na musamman ne masu irinsa ƙalilan ne kodan ya danganta da gyaran da suke samu ,
idanunsa sanye cikin wani farin tsadadden glass da ya ƙara ƙawata baiwar kyawunsa kansa sanye da hula da ta dace da kayansa takalman ƙafafunsa kaɗai ya isa kayi ƙauyanci sam yanda gayu da tsabta gami da kyan jiki ya ratsa sa baka taɓa ɗaukar ya kai shekaru Arba’in zaka ɗauka bazai wuce 35yrs ba ya yi wuta,
Gaba Ɗaya wajen karaɗewa ya yi da daddaɗan ƙamshin turarensa mai matuƙar daɗi da sanyin shaƙa,
“Ranka ya daɗe barka da zuwa”
Dr ya faɗa cike da girgimamawa har ya na haɗawa da russunawa bayan ya basa hannu sukayi musabaha Cikin daddaɗan muryarsa mai cike da miskilanci da rashin son magana ya ce”ya masu jiki”
Muryar sam ba ta ma fita,
Dr ya ce “masu jiki alhamdulillahi ranka ya daɗe ya fama da jama’a “ya faɗa suna yin gaba don masa jagora kamar ko yaushe idan yazo duba marasa lafiya.
Daidai lokacin Abba na ƙarasa zowa wajen da murmushin nuna sanayya ya nufi wajensu tare da cewa”Sanata Marzouq”
Cike da ladabi marzouq ya miƙawa Abba hannu ya ce “ranka ya daɗe barka da yamma”
Ya ce “A ah saidai muce ranmu ya daɗe tare “duk sukayi murmushi Abba ya ce”Ya majalissar kwana biyu ba a ganinka”
Ya ce “Na yi tafiya ne Ɗazu ba jimawa dawowata Ƙasar”
Abba ya ce”Allah ya taimaka “
Duk suka ɗunguma har Abba Bayan securityn Marzouq ya dakatar da su .
Ɗaya bayan ɗaya duk gadon da yaje ya musu ya jiki sai ya aje musu bandir kudaɗe masu yawan gaske suna gaba ya na tambayar Dr akwai issue na Aiki waɗanda ba su da hali”
Dr ya ce”Eh akwai na mutane huɗu mararsa ƙarfi yanzu dai akwai issue mai girma ranka ya daɗe na irin taimakon da kakeyi Yarinyar Sanata Bashir Dikko ce ke buƙatar jini kuma jinin irin naka ne an bincika kaf ba a samu ba har ma mun cire rai da rayuwar yarinyar sai gashi Allah ya kawo mana kai”
Cikin sauri ya kalli Dr ya ce “Subhanallah ai abunda ya dace ayi tun farko meyasa ba ka faɗa da wuri ba ayi sauri muje a ɗauka”
Cikin ƙalilan mimtuna akayi masa text ɗin duk da ya dace aka tabbatar ba matsala tattare dashi kafin a ɗeba jinin leda Ɗaya da gaggauwa akaje aka maƙala mata Abba harda hawayen farinciki ya kama hannun Marzouq ya ce.
“Bani da bakin da zan gode maka bisa ceton rayuwar ƴata da kayi Sanata nagode Allah ya biya maka dukkanin buƙatun ka na Alkhairi ya ƙara maka nasara da ci gaba a dukkan al’amuranka kamar yanda na saba faɗa yau zan maomaita a gabanka *MARZOUQ MALEK* kai ɗin na musamman ne a cikin Al’umma ririnka basu da yawa a duniya”
Sam nauyin godiyar da Abba keyi masa yakeji don bai ɗauki hakan a wani babban abu ba “
Bayan ya huta Ya tashi ya na kallon Abba ya ce “ mu je na duba ƴar taka sai mu wuce”
Bisa jagorancin Dr tare da Abba suka nufa Ɗakin da Ibtihal ta ke kwance hannu ɗaya maƙale da ruwa ɗayan kuma maƙale da jinin da ya fara shiga jikinta”
Samun kansa ya yi da zuba mata ido fuskarta ta yi fayau kyawunta ya ƙara bayyana dukda kasantuwar idanunta na a rufe numfashinta ne kawai zai tabbatar maka da ta na raye wani irin tausayin halin da take ciki ne lokaci guda ya shige shi don duk wanda yasan marzouq ya san mutum ne mai tsananin tausayi minti ukku cikakke baiyi ba ya miƙawa Abba hannu sukayi musabaha ya ce “Allah ya bata lafiya yallaɓai “
Abba ya ce “Ameen ranka ya daɗe ina ƙara matuƙar godiya Allah y saka da mafificin alkhairi”
Suka fito tare momy da ke kuka jikin hajiya da ke ta lallashinta Abba ya kalla ya ce”ki kwantar da hankalinki Nafisa Allah ya kawo mana agajin gaggawar da bamu taɓa tsammani nan kusa ba yanzu haka An saka mata jinin insha Allah zata samu lafiya nan kusa sannan ciwon zuciya ma muna fatan zata rabu dashi gaba ɗaya da yardar Allah”
Da sauri ta ɗago ta ce “Yaya da gaske a ina aka samun jinin bayan an tabbatar da baza’a samesa nan kusa ba “
Ya nuna mata Marzouq da ya duƙa ya gaishe da hajiya cikin sauri momy na hawaye ta ce “mungode Allah ya saka da alkhairi ya biya maka buƙatunka na alkhairi”