Sashe 5
Ibtihal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“ina kika je tsawon shekaru Aunty kika daina xuwa ganinmu duk friday sai munyi kukan rashin ganinki idan Abbey ya zo sai munce ya nemo mana ke don Allah aunty karki ƙara tafiya ki daina zuwa ganinmu muna sonki muna so ki zama mamanmu Muna matuƙar ƙaunarki”
ta ƙarasa faɗa cikin kuka suma sauran Yaran sai suka hau kuka suna cewa”karki ƙara tafiya ki barmu Aunty Muna so ki zama mamamu”
Sosai Suka Karyar da zuciyar Ibtihal har bata san sanda Hawaye suka zobo ba ta maza ta goge tare da shafa kan Ikhlas ta ce”insha Allah bazan ƙara tafiya na barku ba har Abada ku share hawayenku Yaran aunty oya……………✍🏽
*SHARE SHARE SHARE PLX YAN AMANA*
https://chat.whatsapp.com/JYPWPtF78zlIr2kJcbp6ms?mode=gi_t
_*Miss Hajo ce*_🤙🏿
🪅*IBTIHAL*🪅
~MALLAKAR~
*HAJARA L SADEQ*
(miss Hajo)
MARUBUCIYAR👇🏼
Auren wata tara
Ni da yaya arman
Matar uncle
Najmat abiy
Komai mukaddari ne
Khadijatul Sabren
Ribar so
Mata ta ce
*And now*
*IBTIHAL*
*DEDICATED TO MY HUSBAND*
🅿️…………………………..*04*
Lokaci guda duk suka bar kukan tare da fara tsalle ta goge ƙwallan da suka cika mata idanu tare da sakar musu murmushi ta na kama hannun Ikhlas da farida saboda daman chan sunfi shaƙuwa suka nufi wajen da suke zama duk lokacin da ta zo,
Ɗaya daga cikin mai kula da su dattijuwa ta nufo ta da murmushi tare da cewa”jikata Hajiya Ibtihal wata sabon gani”
“ta ɗanyi ɗan murmushi tare da cewa”
Alhamdulillahi mama salame mun sameku lafiya”
Ta na zama gefenta ta ce “lfyqlau sai kewa shekaru da yawa Allah ya sa dai lafiya”
Ta ce “lafiya qlau na yi tafiya ne ban dawo ba sai satin nan “
Ta ce”Allasarki fatan andawo lfy”
Ta ce”Alhamdulillahi ya ƙoƙari”
Ta ce “ƙoƙari na wajenku hajiya mu da aikin biyanmu ake ladan ai na wajenku masu ƙoƙarin”
Ibtihal ta ce”da kinsan ɗubbin ladan da kuke samu a aikin nan mama salame da baki faɗa haka ba kula da yaro ba ƙaramun lada ba ne musamman kuma akace Maraya “
Ta ce “Hakane amma ai hajiya kina Ƙoƙari duk sati fa sai an aiko saƙo wanda na tabbatar daga wajenki ya ke zuwa dukda bakya nan sannan mai kawo saƙon ya ƙi ba da koda numberki yara duk sati suyi ta tsammanin zuwanki “
Ta yi shiru dai batare da tace komai ba sai ɗan murmushi,
Chochulate,Biscuits,Halawa,Mayukan shafawa masu tsada,sabulai,Maclean,Takalma ,Kayan shan iska kasantuwar zafi,da turaruka tare da kayan wasar da tayo musu shopping duk ta basu suka dinga tsalle suna murna tare da mata adduo’i da fatan alkhairi tamkar ba yara ba a ƙarshe duk suka ce Allah ya bata miji na gari don sun San auntyn na su budurwace a ganinsu ,
ba ƙaramun sanyi da daɗi Ibtihal take ji ba duk ranar da yaran nan suna mata addua ta na matuƙar jin daɗin addu’in na su Sannan ta na ƙarajin ƙarfin gwuiwar taimaka musu.
lokacin break na yi duk suka koma class Mama Hauwa ma ɗayar mai kula da su da suka ɗanyi sabo ta zo suka gaisa cike da girmamawa ta koma bakin aikinta,
Zaune suke ita da mama salame samar ƙatuwar tanarma ƙarƙashin wata bishiyar zaitun,
Dafo ta kaɗan mama salame tayi ganin yanda kamar ta zurmiya a duniyar tunani ta ce ,
jikata ko dai akwai abunda ke damunki na kula ko wancen lokacin kina yawan tafiya tunani wanda ke kanki bakya sanin lokacin da kike shiga wannan yanayin a dinga godewa Allah duk wani rufin asiri na duniya Allah yayi muku saidai kawai kuyi fatan samun lahira itama kuma insha Allah ke da mai gidan nan kun sameta don a masu kuɗi irinku ƙalilan ne”
Ibtihal ta yi wani murmushin yaƙe tare da cewa “hmmm Mama wasu mutanen a ganinsu kuɗi kawai sune jin daɗin rayuwa indai ka na da kuɗi ba ka da wata matsala wanda basusan ƙalubalen rayuwa da jarabawar rayuwa ba a kuɗi take ba talaka da mai kuɗi dukkaninsu halittar Allah ne kuma kowannensu bai fi ƙarfin jarabta ba wasu ga kuɗin amma ba ya jin daɗin su ko kaɗan wasu ga kuɗin Allah ya rarabcesu da ciwo,wasu marasa jin Ƴaƴa,wani jarabtar mata,wata jarabtar miji,wani jarabtar ƴan uwa ,wani jarabtar iyaye,wani jarabtar kishiya,wata uwar miji,wani Aboki Amini ,wani rashin haihuwa,Gasu nan dayawa ita jarabtar rayuwa ba a kuɗi take ba”
Mama salame ta katse ta da cewa”ke kuwa ƴata a wannan ƙarancin shekarun naki me zai haɗaki da damuwa haka?
Cike da gajiya da sanyata surutu da mama salame ke yi ta ce”Mu bar maganar mama salame”
Ta ce “Hmmm to shikenan jikata Allah yaye miki abunda ke damunki ya cika rayuwarku da farinciki har Abada Ke da Alhaji *Marzouq Malek*
“ta amsa da Ameen “ta na maimaita *Alhaji Marzouq a cikin ranta kamar ta san sunan”
Mama salame ta ce “Wlh jikata Sai yanzu na kula maganarki Hakane kam jarabawar rayuwa mu gashinan ma a gabanmu muna gani Alhaji Marzouq mai gidan nan ne da nake baki labari tunda yake shekara sha biyu da Aure amma Allah bai basa haihuwa ba kuma bawai haihuwarce bayayi ba da farko a a tuggu da sharrin mace ya gamu dashi wanda ta zalunce sa ta cutar masa da rayuwa domin halin yanzu likitoci sun tabbatar masa ba zai sake haihuwa ba har abada gashi mutum ne mai tsananin kyauta da kirki ga karrama ɗan Adam bai ɗauki dukiyar da mulkin da Allah ya ba sa a bakin komai ba ki duba kiga yaran nan da yake kula da su ko iyayensu sai haka yayi masu gata iya gata ilimin arabi da na zamani sutura me kyau ci da sha me kyau yaran nan kaji ma sai sun ture mu kanmu da muke kula da su wani gata ne baiyi mana ba dukkanin meturorin da ke kula da wajen nan babu wacce ba a sayawa gida aka kaita makka ba Albashin ko da yake biyanmu wlh ko wani malamin asibitin gwamnati bazai gwada mana albashi ba samun ɗan siyasa a ƙasar nan irin bawan Allahn nan sai antona ke ƴata sai ma ince miki wlh babu mu har yqnzu fatanmu da burinmu bai wuce Allah ya cikawa Bawan Allahn nan burinsa ba a duniya ya basa haihuwa tare da mata tagari “
Ta ƙarasa maganar ta na shafce hawaye”
Shiru Ibtihal ta yi ta na kallon mama Salame da ke kuka afujajan hakanan ta ji ta na son sanin waye bawan Allahn nan ta tabbata maganganun mama salame babu ƙarya a ciki domin ita sheda ce jin cewa ɗan siyasa ne abun yayi matuƙar bata mamaki daman muna da irin ƴan siyasa masu irin wannan halayar a ƙasar nan?”
ta tambayi kanta har a ranta ta ji ta na son jin labarinsa kallon mama salame tayi tare da miƙa mata handkitchiep ta ce “ki bar kukan mama salame da ga labari kuma sai kuka”
Ta na shafce majina ta ce “
“Bazaki gane ba ƴar nan domin duk wanda yasan Alhaji Marzouq yasan Ƙaunar sa da yara da chutarwar da akayi masa akan hakan dole ya koka masa”
Ibtihal ta ce”ai kukan bazaiyi magani ba mama Allah ya basa haihuwar me Albarka zakuyi masa fata”
Ta ce “ƴata munayi mu yanzu fatanmu ma ya yi auren da addu’armu kenan domin yayi alƙawarin ya gama aure har abada”
Ibtihal a ranta ta ce “daman akwai mai ra’ayi irin nawa na gama aure har abada “
A zahiri ta zuba mata idanu ta ce “Mama ba kince ya yi aure shekara Sha Biyu baya ba”
Mama salame ta jinjina kai ta ce “hmmm ke dai bari ƴata har bana son tuna labarin bawan Allahn nan mace tayi masa Giɓin da bazai taɓa mantawa ba a rayuwa ya ga tuggu da sharrin mata”
Cike da zaƙuwa da son jin labarinsa ta ce “me macen tayi masa mama daman har akwai chutarwa da mace mai rauni zata iya yiwa ɗa namiji da bai ɗauki mace a bakin komai ba face ƙasƙantacciyar marar galihun da take ƙarƙashinsa a tunani na maza ke zaluntar mata ba wai mace ta zalinci namiji ba”
Mama salamatu ta ce”waya faɗa maki haka ƴata to ai wani sheɗancin da mace zatayi wlh rabinsa namiji bazai iya ba matan kala-kala ne kamar yanda mazan suma suke haka duk ɗan adam ɗin da kika gani da halinsa wani shi mutumin kirki ne mumuni mai tsoron Alkah da tsoron lahiransa wani ko kwata-kwata ma babu Allah a ransa yo sheɗancin da wani musulmin zaiyi ai kafiri ma arne bazai yisa ba donma dai wasu musuluncin na su a baki ne amma sun jima da barinsa yanzu kamar Hajiya Mariya tsohuwar matar Alhaji a gaskiya ban yarda da musulucinta ba”
Cike da zaƙuwa Ibtihal ta ce “ita kuwa mama salamatu me ta aikata haka”
Ta na tauna goro ta ce “zan baki labarin Alhaji Marzouq Kamar yanda kika buƙata ƴata kafin ta gyara zama ta ce Asalin Mahaifinsa da mahaifiyar sa haifaffun………………..✍🏽
*_Miss Hajo ce*_🤙🏿
🪅*IBTIHAL*🪅
~MALLAKAR~
*HAJARA L SADEQ*
(miss Hajo)
MARUBUCIYAR👇🏼
Auren wata tara
Ni da yaya arman
Matar uncle
Najmat abiy
Komai mukaddari ne
Khadijatul Sabren
Ribar so
Mata ta ce
*And now*
*IBTIHAL*
*DEDICATED TO MY HUSBAND*
🅿️…………………………..*05*
Asalin Mahaifinsa da Mahaifiyarsa Haifaffun Garin Haɗeja ne da ke Jahar Jigawa mahaifiyarsa Hajara ita kaɗai Mahaifiyarta ta haifa ta koma ga Allah a wajen haihuwar ɗanta na biyu da har an cire rai da sake haihuwarta tare da cikin suka koma ga Allah wanda lokacin shekarun Hajara goma sha ɗaya a duniya ,
ta ƙarasa faɗa cikin kuka suma sauran Yaran sai suka hau kuka suna cewa”karki ƙara tafiya ki barmu Aunty Muna so ki zama mamamu”
Sosai Suka Karyar da zuciyar Ibtihal har bata san sanda Hawaye suka zobo ba ta maza ta goge tare da shafa kan Ikhlas ta ce”insha Allah bazan ƙara tafiya na barku ba har Abada ku share hawayenku Yaran aunty oya……………✍🏽
*SHARE SHARE SHARE PLX YAN AMANA*
https://chat.whatsapp.com/JYPWPtF78zlIr2kJcbp6ms?mode=gi_t
_*Miss Hajo ce*_🤙🏿
🪅*IBTIHAL*🪅
~MALLAKAR~
*HAJARA L SADEQ*
(miss Hajo)
MARUBUCIYAR👇🏼
Auren wata tara
Ni da yaya arman
Matar uncle
Najmat abiy
Komai mukaddari ne
Khadijatul Sabren
Ribar so
Mata ta ce
*And now*
*IBTIHAL*
*DEDICATED TO MY HUSBAND*
🅿️…………………………..*04*
Lokaci guda duk suka bar kukan tare da fara tsalle ta goge ƙwallan da suka cika mata idanu tare da sakar musu murmushi ta na kama hannun Ikhlas da farida saboda daman chan sunfi shaƙuwa suka nufi wajen da suke zama duk lokacin da ta zo,
Ɗaya daga cikin mai kula da su dattijuwa ta nufo ta da murmushi tare da cewa”jikata Hajiya Ibtihal wata sabon gani”
“ta ɗanyi ɗan murmushi tare da cewa”
Alhamdulillahi mama salame mun sameku lafiya”
Ta na zama gefenta ta ce “lfyqlau sai kewa shekaru da yawa Allah ya sa dai lafiya”
Ta ce “lafiya qlau na yi tafiya ne ban dawo ba sai satin nan “
Ta ce”Allasarki fatan andawo lfy”
Ta ce”Alhamdulillahi ya ƙoƙari”
Ta ce “ƙoƙari na wajenku hajiya mu da aikin biyanmu ake ladan ai na wajenku masu ƙoƙarin”
Ibtihal ta ce”da kinsan ɗubbin ladan da kuke samu a aikin nan mama salame da baki faɗa haka ba kula da yaro ba ƙaramun lada ba ne musamman kuma akace Maraya “
Ta ce “Hakane amma ai hajiya kina Ƙoƙari duk sati fa sai an aiko saƙo wanda na tabbatar daga wajenki ya ke zuwa dukda bakya nan sannan mai kawo saƙon ya ƙi ba da koda numberki yara duk sati suyi ta tsammanin zuwanki “
Ta yi shiru dai batare da tace komai ba sai ɗan murmushi,
Chochulate,Biscuits,Halawa,Mayukan shafawa masu tsada,sabulai,Maclean,Takalma ,Kayan shan iska kasantuwar zafi,da turaruka tare da kayan wasar da tayo musu shopping duk ta basu suka dinga tsalle suna murna tare da mata adduo’i da fatan alkhairi tamkar ba yara ba a ƙarshe duk suka ce Allah ya bata miji na gari don sun San auntyn na su budurwace a ganinsu ,
ba ƙaramun sanyi da daɗi Ibtihal take ji ba duk ranar da yaran nan suna mata addua ta na matuƙar jin daɗin addu’in na su Sannan ta na ƙarajin ƙarfin gwuiwar taimaka musu.
lokacin break na yi duk suka koma class Mama Hauwa ma ɗayar mai kula da su da suka ɗanyi sabo ta zo suka gaisa cike da girmamawa ta koma bakin aikinta,
Zaune suke ita da mama salame samar ƙatuwar tanarma ƙarƙashin wata bishiyar zaitun,
Dafo ta kaɗan mama salame tayi ganin yanda kamar ta zurmiya a duniyar tunani ta ce ,
jikata ko dai akwai abunda ke damunki na kula ko wancen lokacin kina yawan tafiya tunani wanda ke kanki bakya sanin lokacin da kike shiga wannan yanayin a dinga godewa Allah duk wani rufin asiri na duniya Allah yayi muku saidai kawai kuyi fatan samun lahira itama kuma insha Allah ke da mai gidan nan kun sameta don a masu kuɗi irinku ƙalilan ne”
Ibtihal ta yi wani murmushin yaƙe tare da cewa “hmmm Mama wasu mutanen a ganinsu kuɗi kawai sune jin daɗin rayuwa indai ka na da kuɗi ba ka da wata matsala wanda basusan ƙalubalen rayuwa da jarabawar rayuwa ba a kuɗi take ba talaka da mai kuɗi dukkaninsu halittar Allah ne kuma kowannensu bai fi ƙarfin jarabta ba wasu ga kuɗin amma ba ya jin daɗin su ko kaɗan wasu ga kuɗin Allah ya rarabcesu da ciwo,wasu marasa jin Ƴaƴa,wani jarabtar mata,wata jarabtar miji,wani jarabtar ƴan uwa ,wani jarabtar iyaye,wani jarabtar kishiya,wata uwar miji,wani Aboki Amini ,wani rashin haihuwa,Gasu nan dayawa ita jarabtar rayuwa ba a kuɗi take ba”
Mama salame ta katse ta da cewa”ke kuwa ƴata a wannan ƙarancin shekarun naki me zai haɗaki da damuwa haka?
Cike da gajiya da sanyata surutu da mama salame ke yi ta ce”Mu bar maganar mama salame”
Ta ce “Hmmm to shikenan jikata Allah yaye miki abunda ke damunki ya cika rayuwarku da farinciki har Abada Ke da Alhaji *Marzouq Malek*
“ta amsa da Ameen “ta na maimaita *Alhaji Marzouq a cikin ranta kamar ta san sunan”
Mama salame ta ce “Wlh jikata Sai yanzu na kula maganarki Hakane kam jarabawar rayuwa mu gashinan ma a gabanmu muna gani Alhaji Marzouq mai gidan nan ne da nake baki labari tunda yake shekara sha biyu da Aure amma Allah bai basa haihuwa ba kuma bawai haihuwarce bayayi ba da farko a a tuggu da sharrin mace ya gamu dashi wanda ta zalunce sa ta cutar masa da rayuwa domin halin yanzu likitoci sun tabbatar masa ba zai sake haihuwa ba har abada gashi mutum ne mai tsananin kyauta da kirki ga karrama ɗan Adam bai ɗauki dukiyar da mulkin da Allah ya ba sa a bakin komai ba ki duba kiga yaran nan da yake kula da su ko iyayensu sai haka yayi masu gata iya gata ilimin arabi da na zamani sutura me kyau ci da sha me kyau yaran nan kaji ma sai sun ture mu kanmu da muke kula da su wani gata ne baiyi mana ba dukkanin meturorin da ke kula da wajen nan babu wacce ba a sayawa gida aka kaita makka ba Albashin ko da yake biyanmu wlh ko wani malamin asibitin gwamnati bazai gwada mana albashi ba samun ɗan siyasa a ƙasar nan irin bawan Allahn nan sai antona ke ƴata sai ma ince miki wlh babu mu har yqnzu fatanmu da burinmu bai wuce Allah ya cikawa Bawan Allahn nan burinsa ba a duniya ya basa haihuwa tare da mata tagari “
Ta ƙarasa maganar ta na shafce hawaye”
Shiru Ibtihal ta yi ta na kallon mama Salame da ke kuka afujajan hakanan ta ji ta na son sanin waye bawan Allahn nan ta tabbata maganganun mama salame babu ƙarya a ciki domin ita sheda ce jin cewa ɗan siyasa ne abun yayi matuƙar bata mamaki daman muna da irin ƴan siyasa masu irin wannan halayar a ƙasar nan?”
ta tambayi kanta har a ranta ta ji ta na son jin labarinsa kallon mama salame tayi tare da miƙa mata handkitchiep ta ce “ki bar kukan mama salame da ga labari kuma sai kuka”
Ta na shafce majina ta ce “
“Bazaki gane ba ƴar nan domin duk wanda yasan Alhaji Marzouq yasan Ƙaunar sa da yara da chutarwar da akayi masa akan hakan dole ya koka masa”
Ibtihal ta ce”ai kukan bazaiyi magani ba mama Allah ya basa haihuwar me Albarka zakuyi masa fata”
Ta ce “ƴata munayi mu yanzu fatanmu ma ya yi auren da addu’armu kenan domin yayi alƙawarin ya gama aure har abada”
Ibtihal a ranta ta ce “daman akwai mai ra’ayi irin nawa na gama aure har abada “
A zahiri ta zuba mata idanu ta ce “Mama ba kince ya yi aure shekara Sha Biyu baya ba”
Mama salame ta jinjina kai ta ce “hmmm ke dai bari ƴata har bana son tuna labarin bawan Allahn nan mace tayi masa Giɓin da bazai taɓa mantawa ba a rayuwa ya ga tuggu da sharrin mata”
Cike da zaƙuwa da son jin labarinsa ta ce “me macen tayi masa mama daman har akwai chutarwa da mace mai rauni zata iya yiwa ɗa namiji da bai ɗauki mace a bakin komai ba face ƙasƙantacciyar marar galihun da take ƙarƙashinsa a tunani na maza ke zaluntar mata ba wai mace ta zalinci namiji ba”
Mama salamatu ta ce”waya faɗa maki haka ƴata to ai wani sheɗancin da mace zatayi wlh rabinsa namiji bazai iya ba matan kala-kala ne kamar yanda mazan suma suke haka duk ɗan adam ɗin da kika gani da halinsa wani shi mutumin kirki ne mumuni mai tsoron Alkah da tsoron lahiransa wani ko kwata-kwata ma babu Allah a ransa yo sheɗancin da wani musulmin zaiyi ai kafiri ma arne bazai yisa ba donma dai wasu musuluncin na su a baki ne amma sun jima da barinsa yanzu kamar Hajiya Mariya tsohuwar matar Alhaji a gaskiya ban yarda da musulucinta ba”
Cike da zaƙuwa Ibtihal ta ce “ita kuwa mama salamatu me ta aikata haka”
Ta na tauna goro ta ce “zan baki labarin Alhaji Marzouq Kamar yanda kika buƙata ƴata kafin ta gyara zama ta ce Asalin Mahaifinsa da mahaifiyar sa haifaffun………………..✍🏽
*_Miss Hajo ce*_🤙🏿
🪅*IBTIHAL*🪅
~MALLAKAR~
*HAJARA L SADEQ*
(miss Hajo)
MARUBUCIYAR👇🏼
Auren wata tara
Ni da yaya arman
Matar uncle
Najmat abiy
Komai mukaddari ne
Khadijatul Sabren
Ribar so
Mata ta ce
*And now*
*IBTIHAL*
*DEDICATED TO MY HUSBAND*
🅿️…………………………..*05*
Asalin Mahaifinsa da Mahaifiyarsa Haifaffun Garin Haɗeja ne da ke Jahar Jigawa mahaifiyarsa Hajara ita kaɗai Mahaifiyarta ta haifa ta koma ga Allah a wajen haihuwar ɗanta na biyu da har an cire rai da sake haihuwarta tare da cikin suka koma ga Allah wanda lokacin shekarun Hajara goma sha ɗaya a duniya ,