Sashe 14
Ibtihal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya amsa da Amen ya na mai jin daɗin Addu’ar na ta Hajiya ma Albarka ta sanya masa da adduo’i kala-kala kafin ta kalli yarinyar da tunda suka zo tare lokacin afren ta tashi a bacci shikenan suka hau wasa ta ce “Jikata zo ki tafi kar babanki ya tafi ya barki”
Lokaci guda ta sanya kuka ta na maƙale kafaɗa “
Duk sukayi murmushi Aunty salma ta ce “bazaki bi baban naki ba”?
Ta gyaɗa kai ta na hawaye cike da muryar sangarta ta ce “Wajen Ƙawata Afren zan zauna”
Sosai mamaki ya kama Marzouq Tasnem mai masifar rashin son mutane da ƙiyiwa idan ba gidansu ba ko gidan kakanninta ba ta yarda ta zauna itace yau za ta ce zata zauna wajen mutanen da bata sonsu ba”
Ranƙwafowa yayi ya na rage tsawo tare da dafa kanta ya ce”a hanya zan saya miki chochulate sannan gobe da kaina zan kawoki wajen ƙawartaki kinji”
Ta sanya kuka ta ce “a a Daddy a nan zan zauna”……………✍🏽
_*Miss Hajo ce*_🤙🏿
🪅*IBTIHAL*🪅
~MALLAKAR~
*HAJARA L SADEQ*
(miss Hajo)
MARUBUCIYAR👇🏼
Auren wata tara
Ni da yaya arman
Matar uncle
Najmat abiy
Komai mukaddari ne
Khadijatul Sabren
Ribar so
Mata ta ce
*And now*
*IBTIHAL*
*Shafin nan naku ne Hindu Bulama Uwar Lena Tare da Matar Mijinta Allah ƙara muku basirar sabarbaɗo sharhi mai tashin kai Alkhairin Allah yakai muku har gadon baccinku*😘😘
*DEDICATED TO MY HUSBAND*
🅿️…………………………..*10*
Afren ma na ganin ƙawarta za ta tafi ta sanya kuka ,
Kowa ya dinga mamaki wanda daƙyal Safa ta ɗauke afren da ke Haure Haure ita kuma Tasnem Ahmad da ya tsaya tare da security ya na ta game a tab ɗinsa ya ɗauketa wanda kamar zata kada shi don bori Suka yi sallama suna barin wajen wanda har suka tada motocinsu kuka da ihu Tasnem ta ke itama kuma Afren.
*ASOKORO*
Hmmmm Lallai Arziƙi na inda ya ke na faɗa ina ƙarewa wani tsadadden tsararren katafaren wani mentions da ya yi fice a arear kallo,
Tundaga yanayin tsarin gidan kasan turawa suka gina irin gidajen nan ne da idan a hoto ka gani za ka rantse Zane ne Gida har gida tamkar ba a ƙasa nigeria ba,
Ashe banyi kallo ba saida na ƙarasa shiga Cikin compound bayan wuce gate na farko da ya ke shaƙe da security tamkar gidan shugaban ƙasa,
Duk yanda na so irin kwatanta muku yanda Mentions ɗinnan ya ke mai karatu ɓata lokaci ne na ga daular da bantaɓaga irinta ba wanda har saida na yi hawaye da Fatan Allah ya bamu Aljanna,
Ƙaton mention ne da idan ka na son nufar wani ɓangaren na gidan ma idan ba mai jurar doguwar tafiya ba ne to fa to ka na buƙatar Mota amma sauran Ɓangarorin ba shi da tazara sosai,
Ɓangare ne a ƙalla Biyar Wanda kowannensu ya tsaru iya tsaruwa sai Sauran filin gidan da aƙalla za a iya ƙara irin ginin wannan goma a ciki,
Gidan ya tsaru da shuke-shuken zamani tare da decoration masu matuƙar ƙayatarwa.
A wani Ƙaton falo na tsinci Kaina Ashe kalllon waje daban da na ciki,
nidai tsaf da ba da kaina na shigo ba tsintar kaina nayi kawai a wajen to fa zan rantse Ba Ƙasa Nigeria nake ba Dukiya ta yi kuka a palourm Ƙasaitattun Kujeru ne na Alfarma kaiii a iya falon kaɗai na ce zan zauna kwatanta muku yanda yake sai muyi rabin littafin bamuje inda muke so ba ku ƙiyasta da kanku ya wannan Daula za ta Kasance.
Tsit kakejin falon ba motsin komai sai na Ac da kuma TV da ke evening Azhkar an rage volume kaɗan Daddaɗan ƙamshi kawai ke tashi a wajen,
Wata matashiya ce ta shigo ɗakin da gudu kamar wacce aka tunkuɗo cikin tsananin kuke ta ke ƙwala kiran,
“Ummy Ummy”
Ba ta kai ga tsakiyar falon ba wata Kyakyawar farar dattijuwa ta fito sanye cikin wani tsadadden yadin material Ɗinkin bubu da yayi matuƙar mata kyau doguwa ce mai ƙiba irin mutanen nan ne da ƙiba tayi musu bala’in kyau dukda ƙibar na ta ba na tashin Hankali ba ne amma ta na da jiki kallo ɗaya za ka mata kasan hutu sun zauna a wajen Ka na ganinta ka ga tsohuwar ƴar boko domin ilimi ya gama ratsa ta tundaga suffarta,
Hankali tashe ta ƙaraso tsakiyar palon cikin tafiyar kamala ta na kama hannun Matashiyar ta ce”Me ya ke Faruwa Saudat meye kike kuka har haka”
Cikin kuka ta rungumeta ta ce “Ummy Abban Ahmad ne”
“Subhanallah me ya samu Ashraf ɗin ɗazunnan fa yabar nan”
Ta faɗa damuwa ƙarara fuskarta,
Cikin kuka da sangarta ta ce”Ummy haka yace wai sai na tafi gidanmu nace zan tafi da yarana ya amshe su sun tafi wani waje wai ba da su nazo ba wlh ummy bazan iya rayuwa ba yarana ba kuma ya ce ce kar yadawo ya iskeni a gidan “
Hankali tashe Ummy ta ce “Innalillahi wa inna ilaihiraji’un na rasa me ya ke kan Ashraf Mutum sai zafin zuciya na hanasa ba sau ɗaya ba sau biyu ba Akan an samu saɓani kace mace ta tafi gida to babu inda zaki zauna bar kukan bari na kirasa”
Ta na gama faɗa ta zaunar da saudat ta na nufar ɗakin da ta fito minti kaɗan ta fito kunnanta kare da waya ƙirar Iphone 17promax kafin ta katse ta dawo ta zauna idanunta akan Saudat da ke sharar kuka ta ce “Kema bakyajin magana Saudat yanzu haka wani laifin kika masa shi kuma da zafin zuciyar masifa me kika masa“
Batace komai ba sai cigaba da kuka da tayi Ummy ta girgiza kai ta ce “to Allah kyauta ya shiryeku girma kuke amma bakwasanin kun girma kuna da yaron shekara goma amma bakusan me kuke ba kullum kuna rigima yaranku na kallonku”
Minti talatin sai ga Shi ya Iso kallo ɗaya ya yi mata kamar zai bugeta ya ce”ubanme ya kawoki nan gidanku na ce ki tafi ba gidanmu ba “
Ummy na haɗe fuska ta ce “Ohh watau gabana ma zaka maimaita ko Ashraf to babu inda zata ta na da gidan da ya wuce nan marar mutunci sau nawa zan hanaka korar matarka wani irin mutum ne kai Ashraf ka dubi Sadeq da matarsa Ƙaninka ne ya ma rigaka aure amma shekara sha ukku matarsa ko yaji bata taɓa ba amma kai da saudat bazan iya Ƙirga adadin yajinta da faɗanku a gidan nan ba in banda ma yarinyar ta yi hankali yanzu ba ta tafiya ta na zuwa ta sameni me kake tunanin zai faru wallahi da tuni Aurenku ko bai lalace ba ya na gab “
Ya yi shiru ya na huci Ummy ta ce “Me ya Haɗaku yanzu kuma”
Saudat ta sa kuka ta ce “Ummy don Allah ba sai an maimaita ba “
Ya ce “kingani ummy tun a nan ta kama kanta ba ta da gaskiya idan ina faɗa maki rashin mutuncin yarinyar nan bakya yarda “
Ummy ta yi shiru ta na kallonsu har ga Allah Faɗan Saudat da Ashraf abun ya fara damunta ta ma rasa wani irin mataki za ta Ɗauka,
“Assalamu alaikum”
“Wa alaikumussalam Alhamdulillahi gwara da Allah ya kawoka Don gaskiya lamarin nan nema ya ke ya fara fin ƙarfi na gwada maza ku fara shiga”
Ummy ta faɗa idanunta akan Baƙin kamilallen dattijon da ke shigowa tsakiyar palon ya na zama gefen kusa da ita ya ce “To fa irin wannan Hamdala Haka Ummynsu me ya faru”
Ta ce”Ashraf ne bansan me ya haɗasu ba da saudat ya ce ta tafi gidansu na hanasa kalaman nan amma baiji ba”
Abba na cire glass ɗin saman fuskarsa ya mayar da hankalinsa gurin Ashraf ya ce “Ba na buƙatar jin Me ya haɗaku wannan kalamin kaɗai da kayi ya sanya duk gaskiyarka na baka rashin gaskiya lusarin namiji kawai “
Kafin ya maida kallonsa ga Saudat da ke sharar ƙwalla har lokacin ya ce”Kiyi haƙuri ƴata karki sanar da iyayenki ki fara shiri Zanyi muku booking Flight Ki je ki kawomun Passport Ɗinki daman Ranar Friday ni da ummynku zamu wuce umrah ki fara shiri tare zamu wuce sai ki bar masa ƙasar ma baki ɗaya ba ma gida ba”
Lokaci guda saudat ta bar kuka tare da sakin mirmushi ta ce”Nagode Abbanmu passport ɗin ya na part ɗinmu please Abba ya tsaya a nan naje na Ɗauko kar ya biyoni”
Abba ya ce “jeki ɗauko maza sannan ki harhaɗo da kayayyakinki na sakawa”
Cikin sauri ta Miƙe da zata wuce ta faki ido su Abba ya yiwa Ashraf gwalo wanda ya ƙara ƙuluwa akan haushin da Abba ya chusa masa Saudat na barin Wajen ya ce ,
“Haba Abba bakaji me ya faru ba ka Goya mata baya sanadin ta cigaba da Abubuwan da takemun Tsaki fa tayi mun Daga ina mata faɗa ta na latse-latsen wayarta ta bar tasnem na wasan ruwa alhalin Tasan laruranta na Lamonia kunsan ai bata da kunya na faɗa ta faɗa har ta tunzari ni na ce ta tafi gidansu tunda ban isa da ita ba sannan planning take na mata magana ba sau Ɗaya ba sau biyu ba ina buƙatar ƴaƴa tayi burus da ni shine yanzu ta zo angoya mata baya kenan ta cigaba da duk abunda takemun Shikenan nasan maganinta Aure zan ƙara daga chan ma ta tafi bangon duniya”
Abba ya ce “Ashraf to nima ko rashin kunyar zaka mana”
Ya ce “Allah ya huci zuciyarka Abba amma ni gaskiyata na faɗa“
Ummy ta ce “in dai haka ne gaskiya ba ta kyauta ba ƴaƴan da wasu ke nema ruwa jallu shine ita ke gudu wallahi ni duk a zatona Jinkiri ne kawai daga Allah to me yasa tun farko ba ka faɗa mana ba sai ka hau ta kuyi faɗa ina amfanin haka Saudat ba ta da wayau cikin hikima da ruwan sanyi wlh kace tayi abu bari ta ke amma ka hau ta da faɗa wataƙila ma maganganu masu ciwo ka dinga faɗa mata har itama ta biyeka tayi maka tsakin.
Abba ya ce “Ashe kin fahimta wannan masifar da ƴaccewa in banda raini a wajen mace me zata haifar maka “?
Lokaci guda ta sanya kuka ta na maƙale kafaɗa “
Duk sukayi murmushi Aunty salma ta ce “bazaki bi baban naki ba”?
Ta gyaɗa kai ta na hawaye cike da muryar sangarta ta ce “Wajen Ƙawata Afren zan zauna”
Sosai mamaki ya kama Marzouq Tasnem mai masifar rashin son mutane da ƙiyiwa idan ba gidansu ba ko gidan kakanninta ba ta yarda ta zauna itace yau za ta ce zata zauna wajen mutanen da bata sonsu ba”
Ranƙwafowa yayi ya na rage tsawo tare da dafa kanta ya ce”a hanya zan saya miki chochulate sannan gobe da kaina zan kawoki wajen ƙawartaki kinji”
Ta sanya kuka ta ce “a a Daddy a nan zan zauna”……………✍🏽
_*Miss Hajo ce*_🤙🏿
🪅*IBTIHAL*🪅
~MALLAKAR~
*HAJARA L SADEQ*
(miss Hajo)
MARUBUCIYAR👇🏼
Auren wata tara
Ni da yaya arman
Matar uncle
Najmat abiy
Komai mukaddari ne
Khadijatul Sabren
Ribar so
Mata ta ce
*And now*
*IBTIHAL*
*Shafin nan naku ne Hindu Bulama Uwar Lena Tare da Matar Mijinta Allah ƙara muku basirar sabarbaɗo sharhi mai tashin kai Alkhairin Allah yakai muku har gadon baccinku*😘😘
*DEDICATED TO MY HUSBAND*
🅿️…………………………..*10*
Afren ma na ganin ƙawarta za ta tafi ta sanya kuka ,
Kowa ya dinga mamaki wanda daƙyal Safa ta ɗauke afren da ke Haure Haure ita kuma Tasnem Ahmad da ya tsaya tare da security ya na ta game a tab ɗinsa ya ɗauketa wanda kamar zata kada shi don bori Suka yi sallama suna barin wajen wanda har suka tada motocinsu kuka da ihu Tasnem ta ke itama kuma Afren.
*ASOKORO*
Hmmmm Lallai Arziƙi na inda ya ke na faɗa ina ƙarewa wani tsadadden tsararren katafaren wani mentions da ya yi fice a arear kallo,
Tundaga yanayin tsarin gidan kasan turawa suka gina irin gidajen nan ne da idan a hoto ka gani za ka rantse Zane ne Gida har gida tamkar ba a ƙasa nigeria ba,
Ashe banyi kallo ba saida na ƙarasa shiga Cikin compound bayan wuce gate na farko da ya ke shaƙe da security tamkar gidan shugaban ƙasa,
Duk yanda na so irin kwatanta muku yanda Mentions ɗinnan ya ke mai karatu ɓata lokaci ne na ga daular da bantaɓaga irinta ba wanda har saida na yi hawaye da Fatan Allah ya bamu Aljanna,
Ƙaton mention ne da idan ka na son nufar wani ɓangaren na gidan ma idan ba mai jurar doguwar tafiya ba ne to fa to ka na buƙatar Mota amma sauran Ɓangarorin ba shi da tazara sosai,
Ɓangare ne a ƙalla Biyar Wanda kowannensu ya tsaru iya tsaruwa sai Sauran filin gidan da aƙalla za a iya ƙara irin ginin wannan goma a ciki,
Gidan ya tsaru da shuke-shuken zamani tare da decoration masu matuƙar ƙayatarwa.
A wani Ƙaton falo na tsinci Kaina Ashe kalllon waje daban da na ciki,
nidai tsaf da ba da kaina na shigo ba tsintar kaina nayi kawai a wajen to fa zan rantse Ba Ƙasa Nigeria nake ba Dukiya ta yi kuka a palourm Ƙasaitattun Kujeru ne na Alfarma kaiii a iya falon kaɗai na ce zan zauna kwatanta muku yanda yake sai muyi rabin littafin bamuje inda muke so ba ku ƙiyasta da kanku ya wannan Daula za ta Kasance.
Tsit kakejin falon ba motsin komai sai na Ac da kuma TV da ke evening Azhkar an rage volume kaɗan Daddaɗan ƙamshi kawai ke tashi a wajen,
Wata matashiya ce ta shigo ɗakin da gudu kamar wacce aka tunkuɗo cikin tsananin kuke ta ke ƙwala kiran,
“Ummy Ummy”
Ba ta kai ga tsakiyar falon ba wata Kyakyawar farar dattijuwa ta fito sanye cikin wani tsadadden yadin material Ɗinkin bubu da yayi matuƙar mata kyau doguwa ce mai ƙiba irin mutanen nan ne da ƙiba tayi musu bala’in kyau dukda ƙibar na ta ba na tashin Hankali ba ne amma ta na da jiki kallo ɗaya za ka mata kasan hutu sun zauna a wajen Ka na ganinta ka ga tsohuwar ƴar boko domin ilimi ya gama ratsa ta tundaga suffarta,
Hankali tashe ta ƙaraso tsakiyar palon cikin tafiyar kamala ta na kama hannun Matashiyar ta ce”Me ya ke Faruwa Saudat meye kike kuka har haka”
Cikin kuka ta rungumeta ta ce “Ummy Abban Ahmad ne”
“Subhanallah me ya samu Ashraf ɗin ɗazunnan fa yabar nan”
Ta faɗa damuwa ƙarara fuskarta,
Cikin kuka da sangarta ta ce”Ummy haka yace wai sai na tafi gidanmu nace zan tafi da yarana ya amshe su sun tafi wani waje wai ba da su nazo ba wlh ummy bazan iya rayuwa ba yarana ba kuma ya ce ce kar yadawo ya iskeni a gidan “
Hankali tashe Ummy ta ce “Innalillahi wa inna ilaihiraji’un na rasa me ya ke kan Ashraf Mutum sai zafin zuciya na hanasa ba sau ɗaya ba sau biyu ba Akan an samu saɓani kace mace ta tafi gida to babu inda zaki zauna bar kukan bari na kirasa”
Ta na gama faɗa ta zaunar da saudat ta na nufar ɗakin da ta fito minti kaɗan ta fito kunnanta kare da waya ƙirar Iphone 17promax kafin ta katse ta dawo ta zauna idanunta akan Saudat da ke sharar kuka ta ce “Kema bakyajin magana Saudat yanzu haka wani laifin kika masa shi kuma da zafin zuciyar masifa me kika masa“
Batace komai ba sai cigaba da kuka da tayi Ummy ta girgiza kai ta ce “to Allah kyauta ya shiryeku girma kuke amma bakwasanin kun girma kuna da yaron shekara goma amma bakusan me kuke ba kullum kuna rigima yaranku na kallonku”
Minti talatin sai ga Shi ya Iso kallo ɗaya ya yi mata kamar zai bugeta ya ce”ubanme ya kawoki nan gidanku na ce ki tafi ba gidanmu ba “
Ummy na haɗe fuska ta ce “Ohh watau gabana ma zaka maimaita ko Ashraf to babu inda zata ta na da gidan da ya wuce nan marar mutunci sau nawa zan hanaka korar matarka wani irin mutum ne kai Ashraf ka dubi Sadeq da matarsa Ƙaninka ne ya ma rigaka aure amma shekara sha ukku matarsa ko yaji bata taɓa ba amma kai da saudat bazan iya Ƙirga adadin yajinta da faɗanku a gidan nan ba in banda ma yarinyar ta yi hankali yanzu ba ta tafiya ta na zuwa ta sameni me kake tunanin zai faru wallahi da tuni Aurenku ko bai lalace ba ya na gab “
Ya yi shiru ya na huci Ummy ta ce “Me ya Haɗaku yanzu kuma”
Saudat ta sa kuka ta ce “Ummy don Allah ba sai an maimaita ba “
Ya ce “kingani ummy tun a nan ta kama kanta ba ta da gaskiya idan ina faɗa maki rashin mutuncin yarinyar nan bakya yarda “
Ummy ta yi shiru ta na kallonsu har ga Allah Faɗan Saudat da Ashraf abun ya fara damunta ta ma rasa wani irin mataki za ta Ɗauka,
“Assalamu alaikum”
“Wa alaikumussalam Alhamdulillahi gwara da Allah ya kawoka Don gaskiya lamarin nan nema ya ke ya fara fin ƙarfi na gwada maza ku fara shiga”
Ummy ta faɗa idanunta akan Baƙin kamilallen dattijon da ke shigowa tsakiyar palon ya na zama gefen kusa da ita ya ce “To fa irin wannan Hamdala Haka Ummynsu me ya faru”
Ta ce”Ashraf ne bansan me ya haɗasu ba da saudat ya ce ta tafi gidansu na hanasa kalaman nan amma baiji ba”
Abba na cire glass ɗin saman fuskarsa ya mayar da hankalinsa gurin Ashraf ya ce “Ba na buƙatar jin Me ya haɗaku wannan kalamin kaɗai da kayi ya sanya duk gaskiyarka na baka rashin gaskiya lusarin namiji kawai “
Kafin ya maida kallonsa ga Saudat da ke sharar ƙwalla har lokacin ya ce”Kiyi haƙuri ƴata karki sanar da iyayenki ki fara shiri Zanyi muku booking Flight Ki je ki kawomun Passport Ɗinki daman Ranar Friday ni da ummynku zamu wuce umrah ki fara shiri tare zamu wuce sai ki bar masa ƙasar ma baki ɗaya ba ma gida ba”
Lokaci guda saudat ta bar kuka tare da sakin mirmushi ta ce”Nagode Abbanmu passport ɗin ya na part ɗinmu please Abba ya tsaya a nan naje na Ɗauko kar ya biyoni”
Abba ya ce “jeki ɗauko maza sannan ki harhaɗo da kayayyakinki na sakawa”
Cikin sauri ta Miƙe da zata wuce ta faki ido su Abba ya yiwa Ashraf gwalo wanda ya ƙara ƙuluwa akan haushin da Abba ya chusa masa Saudat na barin Wajen ya ce ,
“Haba Abba bakaji me ya faru ba ka Goya mata baya sanadin ta cigaba da Abubuwan da takemun Tsaki fa tayi mun Daga ina mata faɗa ta na latse-latsen wayarta ta bar tasnem na wasan ruwa alhalin Tasan laruranta na Lamonia kunsan ai bata da kunya na faɗa ta faɗa har ta tunzari ni na ce ta tafi gidansu tunda ban isa da ita ba sannan planning take na mata magana ba sau Ɗaya ba sau biyu ba ina buƙatar ƴaƴa tayi burus da ni shine yanzu ta zo angoya mata baya kenan ta cigaba da duk abunda takemun Shikenan nasan maganinta Aure zan ƙara daga chan ma ta tafi bangon duniya”
Abba ya ce “Ashraf to nima ko rashin kunyar zaka mana”
Ya ce “Allah ya huci zuciyarka Abba amma ni gaskiyata na faɗa“
Ummy ta ce “in dai haka ne gaskiya ba ta kyauta ba ƴaƴan da wasu ke nema ruwa jallu shine ita ke gudu wallahi ni duk a zatona Jinkiri ne kawai daga Allah to me yasa tun farko ba ka faɗa mana ba sai ka hau ta kuyi faɗa ina amfanin haka Saudat ba ta da wayau cikin hikima da ruwan sanyi wlh kace tayi abu bari ta ke amma ka hau ta da faɗa wataƙila ma maganganu masu ciwo ka dinga faɗa mata har itama ta biyeka tayi maka tsakin.
Abba ya ce “Ashe kin fahimta wannan masifar da ƴaccewa in banda raini a wajen mace me zata haifar maka “?