Sashe 7
Hangen Dala Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sanda suka fara tafiya qawar rufaida na gaba,hira suke ita da qawar tata suna kwasar dariya abinsu ganin kamar bbn amir din hankalinsa ya kasu kashi biyu,duk da tayi qoqarin janyr hankalin nasa donta cusawa mmn ummin haushi.
Suna gab da shiga wajen taron mmn ummin ta dora masa ummin datayi bacci saman cinyarsa
"Dan riqemin ita bari naje na kama ruwa nadawo" ta fada tana balle murfin motar tafice abinta,abun ya batawa rufaida rai sosai,don su kawai ake jira aga shigowarsu,ga qawayenta daga can qofa suna tsaye sun shirya kansu suna jiran shigowar tasu,sanda tasoma masa qorafin sunbar mutane na jiransu saiya dubeta
"Komu shiga ta tadda mu"
"Kan ubancan kayyasa" ta fada cikin ranta,a ranar auren nata,ranarta rana ta musamman kawai saiya wani sungumi 'ya su shiga dakin taro da yarinya a kafada,dan hoton da zatayi na amarya a kafadar ango shikenan yasha ruwa yake nufi ko kuwa,sam ba xata lamunta ba.
Wayarta ta dauka ta turawa zahra dake zaune gaban mota tex,ba'afi minti biyar ba zahran ta juyo cikin nuna kulawa
"Ita kanta babyn kidan gurin nan zai tasheta,gashi da alama taji dadin baccin,ko zaka kawota na sami zani na goyata ta kwanta sosai?"hakan sai yaga kamar yafi,hakan ya masa,saboda haka zahra ta zagayo ta amshi ummi,yayin da su kuma sukabi ta cikin ayarin masu tarbar amarya da ango suka dunguma dakin taron.
Sai data tabbatar ta bata lokaci me yawa sannan tafito daga inda take boye,dab da zata wuce securityn dake wajen taji ance
"hajiya,ko wannan diyarki ce?" Da sauri ta waiwayo,saiga ummi kan kafadarsa tanata baccinta,wani irin bacin rai take taji ya sauko mata,ranta yabaci sosai,har wani daci daci takeji saman harshenta,qarasawa tayi ta amsheta tana tambayarsa wanda ya bashi ita
"Watace ina tunanin qawar amarya ce"
"Na gode" tace dashi tana amsar ummi,cikin bacin ta durfafi dakin taron tana qiyasta cin mutuncin da zata yiwa bbn amir da rufaidan ma gaba daya,ita zai wulaqanta?,ya bada 'yarta kuma 'yarsa ajiya?,yana nufin budurwarsa ta fita tafi 'yarsa?,ashe haka bbn amir din yake sai yanzu ainihin kalolinsa suke dake bayyanar mata,lallai da gaske,bataga laifin matan da suke cewa duk wadda ta riqi namiji uba ta mutu marainiya,da gaskene namiji hankakane,gabansa fari bayansa baqi,ko a mafarki bata taba tsammatar haka daga baban amir ba,ta zaci ko a fuska kadai ta nuna batason abu ya barshi kenan har abada,ashe ita biqin jegon jaka takeyi.
Gab da xata shiga hall din daya daga cikin samarin dake gadin qofar yasa mata hannu
"Hajiya ina zuwa?" Daga kai tayi tana dubanshi cikin mamaki
"Ciki mana,ina zan shiga idan ba nan ba"
"Saidai ki koma gaskiya,an hana shiga"
"Kamar yaya?,kasan me kake fada kuwa?,kasan wace ni?" Dariya taga sun sanya gaba dayansu bayan sun hada idanu
"To hajiya ko wacece ke kuwa saidai ki haqura ki koma".
Nan ta tsaya musu bayani amma suka watsar da ita a wajen sukaci gaba da hirarsu,abinda yasake bata haushi yakuma daure mata kai shine bayan ita wasu da yawa sun shige,ta musu magana sukace sudin ai an gayyacesune ansan da zuwansu,wani azababben bacin rai yadinga cinta,kunyar yadda suka tozartata ya kamata,saita koma inda suka aje motarsu,abin takaicin a rufe take,murtala kenan shima yana ciki.
Wayarta taciro a gaggauce tasoma kiran bbn amir,lallai ba shakka dukkansu saisun gane kurensu,da saninsa kenan za'a wulaqantata?,ta kirashi a qalla ya kusa sau ashirin saidai bai daga,kasancewar yawa da qarfin hayaniyar dake wajen ba zata barshi yaji ba.
Kamar zata saki kuka haka ta rungume ummi ta soma takawa zuwa titi donta samu abun hawa ta wuce gida,don ba zata iya zama har sai an tashi ba,bacin ran da takeji ita kadai tasan irinsa,inda Allah ya taimaketa da jakarta ta fita,da a cikin motar aka kulle batasan ya zatayi ba.
Kai tsaye dakinta tawuce ba tare da kowa yasan tashigo ba,yaran duka suna dakin mmn amir sunma yi bacci abinsu,kayanta tasoma cirewa tana watsarwa,jin zuciyarta take kamar anyi gobara,xani tasamu ta daura ta zauna jiran dawowar baban amir.
Awa guda harda rabi wayarra tasoma ruri,data duba saitaga baban amir ne ke kira,wani mugun tsaki taja,tanajin wayar harta gama rurinta ta katse,ya sake kira har sau biyu amma wayar bata isheta kallo ba bare ta daga.
Qarfe sha biyu da rabi na dare yashigo gidan,sanda yarufe qofar tana jinsa,miqewa tsaye tayi tana sauraren qarasowarsa.
A qofar dakinta yaga takalmanta,hakan ya alamta masa ta dawo kenan
Dakin mmn amir yashiga ya taddata sunyi bacci duka ita da yaran,yau duka yaranma na dakin,mazan na falo ita da matan suna uwar dakinta saman gadonta,saiya koma da baya ya rufe musu qofar yadda ya ganta ya durfafi dakinsa.
Yana tsaka da cire shaddar jikinsa ta bankado labulen tashigo,saiya daga kanshi yana dubanta tare da karantar yanayinta,har saman fuskarta takejin zafi saboda bacin rai,ta tsaya gabanshi tana dubanshi.
"Basai kayi haka ba zaka tabbatarmin da cewa kai namiji ne,lallai ka nuna halinku da ainihin kalarku,jibril kai munafiki ne maciyin amana da zakaci mutuncina,ku hada baki da budurwar da zaka aura ku wulaqantani,nayi nadama da danasanin aurenka,ba abinda zance tsakanina dakai sai Allah ya isa!" Ta qarashe fada cikin daga murya da zafin rai,daidai lokacin da wayarshi ta dauki ruri,hannu yakai zai dauka tayi hanzarin rigashi kana ta daga tasa handsfree ganin sunan rufaida
"Dear,na manta kayana dana cire a motarka"
"Allah wadaranki kwarkwasa fidda me giji,baqar daga qarshenki ya kusa zuwa" ta fada tana katse kiran,sannan ta daga wayar zata kwadata d qasa,duk kuwa da cewa tasan tsadarta sarai,da hanzari ya tsaidata
"Karki soma,bani wayata!" Ko kadan bata saurareshi ba ta daga wayar ta makata a qasa,take ta tawarwatse saman tiles din.
Cikin bacin rai ua durfafota,zaginsa da fasa wayar suka hadu suka masa zafi sosai
"Idan ka iso karka barni da raina" ta fada tana tsaye qyam tana jiran qarasowarsa,yana isowar kuwa ya dauketa da wani lafiyayyen mari daya sanyata sakin qara saboda yadda ya ratsata,take rigimar ta sake zama sabuwa,ta soma masa jaye jaye cikin dakin naduk abinda hannunta yakai tahau bannatarwa.
Wannan qarar ita tatashi mmn amir,cikin tashin hankali ta fito daga dakin ta nufi dakin bbn amir din inda tajiyo hayaniyar tana tashi.
Daidai lokacin daya sake daga hannu xaikai mata mari mmn amir tashiga tsakani cikin hanzari,wanda kadan yarage yasameta
"Bban amir,meye haka?,meya sameka?"
"Ki qyaleshi ya aikata abinda yayi niyya,zai auro wata dama babu abinda bazai aikata ba!" Mmn ummi ta fada da madaukakin harshe,fuska jazur,saita waiwaya tana dubanta sanda bbn amir yace
"Idan bata ficemin a daki ba zan aikata duk abinda yazo raina" qin fita tayi sukaci gaba da sa'insa,harsai daya kusa sake kai hannu jikinta sannan mmn amir din tayi nasarar fitar da ita.
Cikin fushi yake furzar da iska me zafi,yasamu gefan gadonshi ya zauna yanajin yadda kanshi ke sake daukar caji.
Gefan gadonta ta zaunar da ita sai kuma mmn ummin ta fashe da kuka tana rufe fuskarta,ji take gaba daya duniya ta mata zafi,kamar duk wata qofar walwalarta da farinciki an tosheta,tsayawa kawai mmn amir tayi tana dubanta,tome xata gayawa maryam?,kome zata gaya mata ta jima da gaya mata shi,ita kanta tagaji da ganin wannan bala'in,tayi a qalla minti ashirin tsaye a kanta kafin tace
"Allah ya kyauta,ya sawwaqe" ta juya tafita daga dakin.👁️🗨️👁️🗨️ *HANGEN DALA*👁️🗨️👁️🗨️
_Ba shiga birni ba_
©️®️ *Safiyya Abdullahi Musa Huguma*
*BABI NA SHIDA*
Tunda safiyar garin asabar ta waye tasake shiga fita hayyacinta,tunda ta idara sallar asuba ta kasa komawa bacci,sai zirga zirga da take tsakanin tsakar gidan soro zuwa nata dakin,idanunta kacokam yana kan dakin baban amir,wani mahaukacin kishi takeji,yanxu nan da wasu awanni kenan yaxama nasu su uku?,tashin hankali,saita dora hannunta aka tana neman inda zata sanya zuciyarta da ranta taji dadi,wani irin radadi da zugi gamida qunci takeji cikin zuciyarta,saita dauki wayarta ta kirayi hafsat.
Bugu hudu ta daga
"Ya akayi mmn ummi,mun tashi lpy"
"Babu batun tambyar lafiya game dani,tunda kin san babu ita,yaushe zaki shigo,wallahi hafsat jin gidan nan nake kamar wata qiyamata ko lahira"
"Karki damu ina sallamar babansu minal zan shirya na taho"
"Don Allah karki dade"
"In sha Allahu" aje wayar tayi tana furxar da iska daga bakinta.
Wayar tatace tasake ruri,data duba sai taga lambar qanwarta ce,ba jinkiri ta daga sai taji muryar mahaifiyarta,kuka ta sanya
"Meye haka maryam?"
"Umma yaune daurin auren fa?"
"Sai kuyi haquri ai,haka Allah ya dora muku"
"Don Allah umma kixo,don Allah"
"A'ah,nikam bazanzo wannan gidan naku ba,zandai turo miki ruqayya da zakiyya,sai yayarku duka zasu taho tare"
"Toh umma"
"Zasu taho miki da saqo,saiki sawa ranki haquri,tunda haka Allah ya dora masa" daga haka sukayi sallama,saita danji sanyi da maganar da sukayi da ummantata.
Qarfe takwas tasoma jin motsin yaran a tsakar gidan,tun cikin satin suma yaran ta sallamasu gaba daya,mmn amir ce keta hidima dasu,hattasu abun ya shafesu,ita kuwa maman amir ko a jikinta,saboda kai kawon yaran da kula dasu da takeyi ya dauke mata hankali gami da debe mata kewa da bacin rai,idan tana tare da yaran sai taji ta manta da wasu abubuwan.
Miqewa tayi ta isa bakin window tana leqen abinda yake faruwa a tsakar gidan,mmn ummin ce zaune saman kujera 'yar tsugunno,gabanta sabbabin shaddodine ruwan omo,saman cinyarta wasu daga wandunan yaranne tana saka musu tazuge,mubarak na tsaye a kanta da alama yayi wanka ya shafa mai yana jiran ta gama saka masa tazugen tabashi ya saka,yayin da mmn amir din ke aikin tana gyarawa hanifa wankan da takewa usman.
Wani baqinciki da bacin rai ya kamata,wato har wani anko ya yiwa yaran na xuwa daurin aurenshi kenan,ita batama sani ba?,kafin tayi kowanne yunquri baban amir din yayi sallama yashigo gidan,hannunshi dauke da wata shaddar kalar ta yaran,da alama tashice ya amso.
Suna gab da shiga wajen taron mmn ummin ta dora masa ummin datayi bacci saman cinyarsa
"Dan riqemin ita bari naje na kama ruwa nadawo" ta fada tana balle murfin motar tafice abinta,abun ya batawa rufaida rai sosai,don su kawai ake jira aga shigowarsu,ga qawayenta daga can qofa suna tsaye sun shirya kansu suna jiran shigowar tasu,sanda tasoma masa qorafin sunbar mutane na jiransu saiya dubeta
"Komu shiga ta tadda mu"
"Kan ubancan kayyasa" ta fada cikin ranta,a ranar auren nata,ranarta rana ta musamman kawai saiya wani sungumi 'ya su shiga dakin taro da yarinya a kafada,dan hoton da zatayi na amarya a kafadar ango shikenan yasha ruwa yake nufi ko kuwa,sam ba xata lamunta ba.
Wayarta ta dauka ta turawa zahra dake zaune gaban mota tex,ba'afi minti biyar ba zahran ta juyo cikin nuna kulawa
"Ita kanta babyn kidan gurin nan zai tasheta,gashi da alama taji dadin baccin,ko zaka kawota na sami zani na goyata ta kwanta sosai?"hakan sai yaga kamar yafi,hakan ya masa,saboda haka zahra ta zagayo ta amshi ummi,yayin da su kuma sukabi ta cikin ayarin masu tarbar amarya da ango suka dunguma dakin taron.
Sai data tabbatar ta bata lokaci me yawa sannan tafito daga inda take boye,dab da zata wuce securityn dake wajen taji ance
"hajiya,ko wannan diyarki ce?" Da sauri ta waiwayo,saiga ummi kan kafadarsa tanata baccinta,wani irin bacin rai take taji ya sauko mata,ranta yabaci sosai,har wani daci daci takeji saman harshenta,qarasawa tayi ta amsheta tana tambayarsa wanda ya bashi ita
"Watace ina tunanin qawar amarya ce"
"Na gode" tace dashi tana amsar ummi,cikin bacin ta durfafi dakin taron tana qiyasta cin mutuncin da zata yiwa bbn amir da rufaidan ma gaba daya,ita zai wulaqanta?,ya bada 'yarta kuma 'yarsa ajiya?,yana nufin budurwarsa ta fita tafi 'yarsa?,ashe haka bbn amir din yake sai yanzu ainihin kalolinsa suke dake bayyanar mata,lallai da gaske,bataga laifin matan da suke cewa duk wadda ta riqi namiji uba ta mutu marainiya,da gaskene namiji hankakane,gabansa fari bayansa baqi,ko a mafarki bata taba tsammatar haka daga baban amir ba,ta zaci ko a fuska kadai ta nuna batason abu ya barshi kenan har abada,ashe ita biqin jegon jaka takeyi.
Gab da xata shiga hall din daya daga cikin samarin dake gadin qofar yasa mata hannu
"Hajiya ina zuwa?" Daga kai tayi tana dubanshi cikin mamaki
"Ciki mana,ina zan shiga idan ba nan ba"
"Saidai ki koma gaskiya,an hana shiga"
"Kamar yaya?,kasan me kake fada kuwa?,kasan wace ni?" Dariya taga sun sanya gaba dayansu bayan sun hada idanu
"To hajiya ko wacece ke kuwa saidai ki haqura ki koma".
Nan ta tsaya musu bayani amma suka watsar da ita a wajen sukaci gaba da hirarsu,abinda yasake bata haushi yakuma daure mata kai shine bayan ita wasu da yawa sun shige,ta musu magana sukace sudin ai an gayyacesune ansan da zuwansu,wani azababben bacin rai yadinga cinta,kunyar yadda suka tozartata ya kamata,saita koma inda suka aje motarsu,abin takaicin a rufe take,murtala kenan shima yana ciki.
Wayarta taciro a gaggauce tasoma kiran bbn amir,lallai ba shakka dukkansu saisun gane kurensu,da saninsa kenan za'a wulaqantata?,ta kirashi a qalla ya kusa sau ashirin saidai bai daga,kasancewar yawa da qarfin hayaniyar dake wajen ba zata barshi yaji ba.
Kamar zata saki kuka haka ta rungume ummi ta soma takawa zuwa titi donta samu abun hawa ta wuce gida,don ba zata iya zama har sai an tashi ba,bacin ran da takeji ita kadai tasan irinsa,inda Allah ya taimaketa da jakarta ta fita,da a cikin motar aka kulle batasan ya zatayi ba.
Kai tsaye dakinta tawuce ba tare da kowa yasan tashigo ba,yaran duka suna dakin mmn amir sunma yi bacci abinsu,kayanta tasoma cirewa tana watsarwa,jin zuciyarta take kamar anyi gobara,xani tasamu ta daura ta zauna jiran dawowar baban amir.
Awa guda harda rabi wayarra tasoma ruri,data duba saitaga baban amir ne ke kira,wani mugun tsaki taja,tanajin wayar harta gama rurinta ta katse,ya sake kira har sau biyu amma wayar bata isheta kallo ba bare ta daga.
Qarfe sha biyu da rabi na dare yashigo gidan,sanda yarufe qofar tana jinsa,miqewa tsaye tayi tana sauraren qarasowarsa.
A qofar dakinta yaga takalmanta,hakan ya alamta masa ta dawo kenan
Dakin mmn amir yashiga ya taddata sunyi bacci duka ita da yaran,yau duka yaranma na dakin,mazan na falo ita da matan suna uwar dakinta saman gadonta,saiya koma da baya ya rufe musu qofar yadda ya ganta ya durfafi dakinsa.
Yana tsaka da cire shaddar jikinsa ta bankado labulen tashigo,saiya daga kanshi yana dubanta tare da karantar yanayinta,har saman fuskarta takejin zafi saboda bacin rai,ta tsaya gabanshi tana dubanshi.
"Basai kayi haka ba zaka tabbatarmin da cewa kai namiji ne,lallai ka nuna halinku da ainihin kalarku,jibril kai munafiki ne maciyin amana da zakaci mutuncina,ku hada baki da budurwar da zaka aura ku wulaqantani,nayi nadama da danasanin aurenka,ba abinda zance tsakanina dakai sai Allah ya isa!" Ta qarashe fada cikin daga murya da zafin rai,daidai lokacin da wayarshi ta dauki ruri,hannu yakai zai dauka tayi hanzarin rigashi kana ta daga tasa handsfree ganin sunan rufaida
"Dear,na manta kayana dana cire a motarka"
"Allah wadaranki kwarkwasa fidda me giji,baqar daga qarshenki ya kusa zuwa" ta fada tana katse kiran,sannan ta daga wayar zata kwadata d qasa,duk kuwa da cewa tasan tsadarta sarai,da hanzari ya tsaidata
"Karki soma,bani wayata!" Ko kadan bata saurareshi ba ta daga wayar ta makata a qasa,take ta tawarwatse saman tiles din.
Cikin bacin rai ua durfafota,zaginsa da fasa wayar suka hadu suka masa zafi sosai
"Idan ka iso karka barni da raina" ta fada tana tsaye qyam tana jiran qarasowarsa,yana isowar kuwa ya dauketa da wani lafiyayyen mari daya sanyata sakin qara saboda yadda ya ratsata,take rigimar ta sake zama sabuwa,ta soma masa jaye jaye cikin dakin naduk abinda hannunta yakai tahau bannatarwa.
Wannan qarar ita tatashi mmn amir,cikin tashin hankali ta fito daga dakin ta nufi dakin bbn amir din inda tajiyo hayaniyar tana tashi.
Daidai lokacin daya sake daga hannu xaikai mata mari mmn amir tashiga tsakani cikin hanzari,wanda kadan yarage yasameta
"Bban amir,meye haka?,meya sameka?"
"Ki qyaleshi ya aikata abinda yayi niyya,zai auro wata dama babu abinda bazai aikata ba!" Mmn ummi ta fada da madaukakin harshe,fuska jazur,saita waiwaya tana dubanta sanda bbn amir yace
"Idan bata ficemin a daki ba zan aikata duk abinda yazo raina" qin fita tayi sukaci gaba da sa'insa,harsai daya kusa sake kai hannu jikinta sannan mmn amir din tayi nasarar fitar da ita.
Cikin fushi yake furzar da iska me zafi,yasamu gefan gadonshi ya zauna yanajin yadda kanshi ke sake daukar caji.
Gefan gadonta ta zaunar da ita sai kuma mmn ummin ta fashe da kuka tana rufe fuskarta,ji take gaba daya duniya ta mata zafi,kamar duk wata qofar walwalarta da farinciki an tosheta,tsayawa kawai mmn amir tayi tana dubanta,tome xata gayawa maryam?,kome zata gaya mata ta jima da gaya mata shi,ita kanta tagaji da ganin wannan bala'in,tayi a qalla minti ashirin tsaye a kanta kafin tace
"Allah ya kyauta,ya sawwaqe" ta juya tafita daga dakin.👁️🗨️👁️🗨️ *HANGEN DALA*👁️🗨️👁️🗨️
_Ba shiga birni ba_
©️®️ *Safiyya Abdullahi Musa Huguma*
*BABI NA SHIDA*
Tunda safiyar garin asabar ta waye tasake shiga fita hayyacinta,tunda ta idara sallar asuba ta kasa komawa bacci,sai zirga zirga da take tsakanin tsakar gidan soro zuwa nata dakin,idanunta kacokam yana kan dakin baban amir,wani mahaukacin kishi takeji,yanxu nan da wasu awanni kenan yaxama nasu su uku?,tashin hankali,saita dora hannunta aka tana neman inda zata sanya zuciyarta da ranta taji dadi,wani irin radadi da zugi gamida qunci takeji cikin zuciyarta,saita dauki wayarta ta kirayi hafsat.
Bugu hudu ta daga
"Ya akayi mmn ummi,mun tashi lpy"
"Babu batun tambyar lafiya game dani,tunda kin san babu ita,yaushe zaki shigo,wallahi hafsat jin gidan nan nake kamar wata qiyamata ko lahira"
"Karki damu ina sallamar babansu minal zan shirya na taho"
"Don Allah karki dade"
"In sha Allahu" aje wayar tayi tana furxar da iska daga bakinta.
Wayar tatace tasake ruri,data duba sai taga lambar qanwarta ce,ba jinkiri ta daga sai taji muryar mahaifiyarta,kuka ta sanya
"Meye haka maryam?"
"Umma yaune daurin auren fa?"
"Sai kuyi haquri ai,haka Allah ya dora muku"
"Don Allah umma kixo,don Allah"
"A'ah,nikam bazanzo wannan gidan naku ba,zandai turo miki ruqayya da zakiyya,sai yayarku duka zasu taho tare"
"Toh umma"
"Zasu taho miki da saqo,saiki sawa ranki haquri,tunda haka Allah ya dora masa" daga haka sukayi sallama,saita danji sanyi da maganar da sukayi da ummantata.
Qarfe takwas tasoma jin motsin yaran a tsakar gidan,tun cikin satin suma yaran ta sallamasu gaba daya,mmn amir ce keta hidima dasu,hattasu abun ya shafesu,ita kuwa maman amir ko a jikinta,saboda kai kawon yaran da kula dasu da takeyi ya dauke mata hankali gami da debe mata kewa da bacin rai,idan tana tare da yaran sai taji ta manta da wasu abubuwan.
Miqewa tayi ta isa bakin window tana leqen abinda yake faruwa a tsakar gidan,mmn ummin ce zaune saman kujera 'yar tsugunno,gabanta sabbabin shaddodine ruwan omo,saman cinyarta wasu daga wandunan yaranne tana saka musu tazuge,mubarak na tsaye a kanta da alama yayi wanka ya shafa mai yana jiran ta gama saka masa tazugen tabashi ya saka,yayin da mmn amir din ke aikin tana gyarawa hanifa wankan da takewa usman.
Wani baqinciki da bacin rai ya kamata,wato har wani anko ya yiwa yaran na xuwa daurin aurenshi kenan,ita batama sani ba?,kafin tayi kowanne yunquri baban amir din yayi sallama yashigo gidan,hannunshi dauke da wata shaddar kalar ta yaran,da alama tashice ya amso.