Sashe 10
Hangen Dala Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kai tsaye dakin mmn amir din yanufa,ya yaye labulen bakinsa dauke da sallama,amsa masa tayi a sanyaye bayan ta daga kanta da niyyar kallonshi,saidai ta kasa,saboda wani abu daya takore mata wuya,hakanan taji cikinta yasake nauyi
"Sannu da zuwa" ta furta daqyar tana kuda kanta gefe,idanunshi a kanta yana karantarta ya amsa mata
"Kun yini lpy ya yaran duka?"
"Sunyi bacci" ta bashi amsa a taqaice,shuru daiya ratsa tsakaninsu,hakanan yadinga jin nauyinta,yana tuna wancan shekarun da suka shude a rana irib wannan,kusan hakan tayi masa,yaga zallar kishi da bacin rai a fuskarta amma tazabi yin shurun kamar wannan lokacin,duk sai yaji nauyin tashi yafita din,yana ganin kamar ya cutar da ita a rayuwa har sau biyu,cikin son nade tabarnar kunya yace
"Na tsammaci zuwa yanzu kin kwanta,don nasan kunsha kujiba kujiba ko"
"Yanzu nake shirin tashi" ta fada tana yunqurawa da qyar
"Yi a hankali" ya fada sanda tadan koma baya kamar xata zauna sai kuma ta sake miqewa,ledar hannnunshi yamiqa mata ganin tana niyyar shigewa uwar dakinta
"Babu wani abun da kuke da buqata?" Ya tambayeta yana kallon bayanta sanda take dab da shigewa dakin nata
"Babu komai" ta fada bayan ta dakata ba tare data waiwayo ba
"Haka akeso" sai yasake yin shuru na wasu sakanni sannan yace
"Halima.....don Allah ki kwanta kiyi baccinki sosai kodon abinda yake jikinki,karki sakawa ranki damuwa don Allah"kai ta jinjina tana qoqarin hadiye abinda ke taso mata sannan ta sanya kai cikin dakin.
Kusan sakan goma sannan ya taka ya juya yafice yana jin tausayinta sosai cikin ranshi,ta nuna dukkan wata jarumta da haquri,ba shakka haliman baiwa ce da Allah yayi masa na macen da ba kasafai ake samun irinsu ba,maryam kawai ta zame masa ishara.
Daga nan dakin mmn ummin yashiga,itama da sallamar yashiga,tana tsakar falon tana kai kawo goye da ummi a bayanta wanda ta jima dayin bacci,fuskarta kawai zaka kalla kasan bala'i da tashin hankalin da take ciki.
Dauke kanta tayi sanda taga shigowarsa,qirjinta yaci gaba da zafi,ko sallamar ma bata da lokacin amsa mishi
"an yini lpy" ya fada itama yana zama hannun kujera,banza tayi dashi,saima tasoma tattare kayan dake zaune d'ai d'ai tsakar falon kamar batasan Allah yayi ruwanshi ba,qoqarin danne bakinta take ta hana kanta ruga masa ashariyar daketa yawo saman harshenta,data gama saita wuce dakinta tarufe qofar tabarshi nan zaune.
Yasan cewa lallai anzo gabar da duk dauriyarki dole gazawarki ta bayyana,saboda haka baiyi qasa a gwiwa ba yanufi qofar dakin yasoma qwanqwasa mata
"Bude mana maryam"
"In bude inyi uwar meye?,jibril kafice min daga daki wallahil azim idan nafito ba zamu kwasheta da dadi ba,maciyin amana kawai,Allah dai yayimin sakayya" saita rushe da kuka sosai mai fidda sauti,kanshi kawai ya girgixa saiya koma da baya ya aje mata ledar ya juya yafice zuwa sashen rufaida.
Cikin so da qauna ta taryeshi,cike da nuna wayewa da sanin me rayuwa take ciki,hakanan ya biye mata,saidai can qasan ranshi yana mamaki kadan kadan idan tayi wani abun,sabida ko maryam daren farkonsu batayi ba bare halima,daga bisani saiya share shima,komai ya kauce daga ranshi ganin cewa ba wani abu daya tadda tattare da ita wanda ba dai dai ba ko zai saka zuciya ko rai cikin zargi.
Wanka mmn amir tasamu tayi cikin bandakinta sannan tasauya kaya,ganin idanunta yasoye,tunani yana neman hanata bacci,saita dauko qur'aninta da dama kullum bai rabo da gefan gadonta,ta bude wasu shafuka tasoma karantawa,babu jimawa taji bacci yazo mata,idanunta har rurrufewa suke,tasamu ta maida qur'anin batayi wata wata ba taja filo ta kwanta.
Mmn ummi kuwa a iya cewa kwanan zaune tayi,sai zirga zirgan shiga bandaki data sameta saboda tashin hankali,tayi kuka har batasan iyaka ba,haka tazauna tasaka agogo a gaba tana kallo,duk daqiqa daya da zata wuce tana lissafawa gamida qissima yanzu abu kaza baban amir din yake,yanzu yaci ace yayiwa rufaidan abu kaza,saita sake rushewa da kuka,haka takusan kwana,kafin wani lokaci kuwa kanta yadinga ciwo,da qyar gefin asuba tasamu bacci yayi awon gaba da ita cike da tarin baqinciki da quncin zuciya.
Qarfe biyar da rabi yashigo dakin,a lokacin tana zaune saman abun sallarta tana jan carbi,duka yaran sun gama sallarsu sun koma baccin,itama jira take ta gama addu'o'inta takoma ta kwanta din kafin gari ya qarasa wayewa,saboda tasan gidan a kacame yake sosai,gashi yaudin tanason zuwa awo ranar da zata likita ne.
Kallo daya tayi masa ta dauke kai,saidai abun ya bata mamaki,batama tsammaci shigowarsa ba adai dai wannan lokacin,don kuwa zamanin maryam bataga idanunshi ba sai goma na safe.
Shi yasoma gaidata har taji abunma bambarakwai,saita amsa kawai,ya tambayi yaran tace sunyi sallah sun koma
"Sannu da qoqari,Allah yayi albarka"
"Amin" ta amsa tana ci gaba da jan carbinta ba tare data sake tanka masa komai ba,tana kallonshi ya gama kame kamensa sannan ya juya zai fita
"Idan gari ya gama wayewa zanje naga likita" waiwayowa yayi cikin kulawa
"Au...lafiya dai ko?"
"Qalau,lokacin komawa awona ne yayi tun wancan satin ban samu zuwa ba saboda hidima"
"Me yasa zaki fashin zuwa ganin likita?,wannan ai sakaci da lafiya ne,ki shirya da wuri ki barma mmn ummi sauran ayyukan,idan kin gama saiki sanarmin" zataso ya sallameta ne kawai a lokacin basai ta tsaya wani binbinin nemanshi ba,amma batason doguwar magana a yanayin da take ciki,saboda haka tace masa to kawai
Qarfe bakwai ta tashi salima suka shiga gyaran gidan,ita kuma tashiga kitchen tadora abin karin safe,don tasan idan tabiye ta mmn ummi bataqi ranar gidan yakuma yini a haka ba,hakanan uban kowama cikin gidan yawuni da yunwa ba damuwarta bane.
Duk zirga zirgar mmn amir din kan idanun mmn ummi,don tunda tafarka qarfe shida tayi salla bata koma ba,saita koma saman kujerarta dake bakin qofar dakin tazauna ta yaye labulen tana ganin duk wani abu da zai gitta ta tsakar gidan,tunanin abinda zata qirqira kawai take wanda zai fiddo bban amir daga dakin rufaidan da farar safiya,yadda zata cusa mata haushi da takaici.
Ranta a bace takebin mmn amir dake kai kawo tsakar gidan tana hidimominta,ji take kamar ma farinciki mmn amir din keyi da wannan lamarin,qwafa taja haushinta na sake cikata,ita ko wani dan bacin rai bata karanta saman fuskarta ba,kamar ma ba matarshi ba,shine zata wani tashi da sassafe tahau aiki,itakam baiwar Allahn batasan ma tanayi ba,don abinda ta iyakancewa ranta zatayi komaine don saboda yaran da kuma karan kanta.
Sai data gama abun karin yaran sukayi wanka gaba dayansu suka karya,tabar saura a kitchen saboda sauran mutanen gidan,ta kintsa tsaf,tana daga zaune tana karyawa don karta zalunci abinda ke cikin nata,saboda jiya batasamu damar sanya komai a bakinta ba,tunanin yadda zata aika yaran kiran abban nasu take,batason shigarsu dakin
"Amir miqomin wayata" ta fada tana kai kofin tea bakinta,dakinta yashiga yafito mata da wayar ya miqa mata,tasa hannu ta amsa sannan tafara laluben number abban amir din,sau biyu tana kira bata shiga,saita aje wayar taci gaba da karyawarta.
Bayan ta gama ta duba jakarta,taga akwai sauran kudade,saboda haka ta zura hijabinta ta miqe tana duban salima
"Zanje,don Allah ki kula dasu,karki barsu suje ko ina,tunda akwai wuta ga cartoons can dana ware musu wadanda duke kalla ki saka musu,kiyi zamanku a daki,tunda mmn ummi nanan zata kula da sauran komai"
"To saikin dawo" daga haka tamusu sallama tafice ba tare data tsaya neman bbn amir din ba.
Qarfe sha daya nasafe tashiga bandakin dake falonta ta silla wanka,sannan taxauna gaban mudubi ta tsara kwalliya tagani ta fada,ta zabi riga da skert da suka kaamaata cikin kayanta tasanya,ta tura daurin dankwalinta gaba goshi sannan ta dawo falo inda tabar bbn amir zaune yana kallo.
Wani fari ta sakar masa gamida sauya takun tafiyarta,ya buda mata hannayensa yana sakar mata murmushi gamida fasa mata kai kan yadda tayi kyau,ta narke ajikinsa sosai tana zuba mishi shagwaba shi kuma yana tambayarta daren jiya
"Yunwa mafa nakeji dear,su mutanen gidan nan basu iya adana baqonsu ba?"
"A'ah na tabbata akwai abinci a kitchen,may be basason matsa mana shi yasa ba wanda suka aiko,bari naje na duba miki sweet,amma ya kamata ki fita ki gaisa da mutanen gidan"fuska ta yatsine tana jin abun wani banbarakwai,don bata tsammaci zaice haka ba
"amma ai nice baquwa,niya cancanci a gaisar" kai ya kada
"Eh,amma idan kika duba ai kece qarama ko?,keya kamata ki dinga zuwa gaidasu" kan ubancan,yo koshi ita yau bata gaisar ba ballantana wasu gajarabul din matanshi,batason bata plan dinta saboda haka tace mishi
"Ba damuwa,amma yunwa nakeji,bari na qoshi tukunna"
"Karki damu,bari na duba gidan"murmushi ta sakar masa
"kayi sauri kadawo,akwai wani daddadan labari dana tanada maka"
"An gama gimbiya" daga haka ya juya yafice,wani wawan tsaki taja tana yatsuna fuska,gaida matanshi kamar wani a qauye?,koko zamansu take?,itakam ba zata juri wannan iskantar ba wlh,duk wadda ta matsu da ita tashigo ta gaidata.
Dakin mmn ummi yanufa yana don yasan aikin gidan kamata yayi ace yana hannunta,tana zaune tun safe yadda tatashi da kayan jikinta,ita daya cikin dakin daga ita sai ummi itama data gaji da zaman ita daya,tana ta 'yan qananun rigingimu tana neman wanda zai dauketa ya fita da ita.
Aiko yana shigowa tagudu daga wajen uwar tayo wajen,ya dauketa yana cillata sama yana mata wasa,ko ummin ba'a yiwa wanka ba bare uwarta tasamu yi tana zaune tana dacin rai,sosai ta qureshi da idanu kamar zata gani sauyawar wani abu daga jikinsa,sai kuwa taga kamar walwalarsa ta dadu,fuskarsa ta qara kyau,wani abu ya tokare mata wuya,tsantsar tsanarshi da haushinsa kamar tatashi ta rufeshi da duka haka takeji
"An gama abincin kari ne?" Wata uwar harara ta watsa masa,ta masa kallon sama da qasa
"Na maka kama da wadda zata zauna tana muku girki kuna ci?,toni ba jaka bace nasan inda yakemin ciwo" daga haka tashige daki abinta,baiso kulata bare subar wani abun fadan,saboda haka yajuya yafice zuwa dakin mmn amir.
"Sannu da zuwa" ta furta daqyar tana kuda kanta gefe,idanunshi a kanta yana karantarta ya amsa mata
"Kun yini lpy ya yaran duka?"
"Sunyi bacci" ta bashi amsa a taqaice,shuru daiya ratsa tsakaninsu,hakanan yadinga jin nauyinta,yana tuna wancan shekarun da suka shude a rana irib wannan,kusan hakan tayi masa,yaga zallar kishi da bacin rai a fuskarta amma tazabi yin shurun kamar wannan lokacin,duk sai yaji nauyin tashi yafita din,yana ganin kamar ya cutar da ita a rayuwa har sau biyu,cikin son nade tabarnar kunya yace
"Na tsammaci zuwa yanzu kin kwanta,don nasan kunsha kujiba kujiba ko"
"Yanzu nake shirin tashi" ta fada tana yunqurawa da qyar
"Yi a hankali" ya fada sanda tadan koma baya kamar xata zauna sai kuma ta sake miqewa,ledar hannnunshi yamiqa mata ganin tana niyyar shigewa uwar dakinta
"Babu wani abun da kuke da buqata?" Ya tambayeta yana kallon bayanta sanda take dab da shigewa dakin nata
"Babu komai" ta fada bayan ta dakata ba tare data waiwayo ba
"Haka akeso" sai yasake yin shuru na wasu sakanni sannan yace
"Halima.....don Allah ki kwanta kiyi baccinki sosai kodon abinda yake jikinki,karki sakawa ranki damuwa don Allah"kai ta jinjina tana qoqarin hadiye abinda ke taso mata sannan ta sanya kai cikin dakin.
Kusan sakan goma sannan ya taka ya juya yafice yana jin tausayinta sosai cikin ranshi,ta nuna dukkan wata jarumta da haquri,ba shakka haliman baiwa ce da Allah yayi masa na macen da ba kasafai ake samun irinsu ba,maryam kawai ta zame masa ishara.
Daga nan dakin mmn ummin yashiga,itama da sallamar yashiga,tana tsakar falon tana kai kawo goye da ummi a bayanta wanda ta jima dayin bacci,fuskarta kawai zaka kalla kasan bala'i da tashin hankalin da take ciki.
Dauke kanta tayi sanda taga shigowarsa,qirjinta yaci gaba da zafi,ko sallamar ma bata da lokacin amsa mishi
"an yini lpy" ya fada itama yana zama hannun kujera,banza tayi dashi,saima tasoma tattare kayan dake zaune d'ai d'ai tsakar falon kamar batasan Allah yayi ruwanshi ba,qoqarin danne bakinta take ta hana kanta ruga masa ashariyar daketa yawo saman harshenta,data gama saita wuce dakinta tarufe qofar tabarshi nan zaune.
Yasan cewa lallai anzo gabar da duk dauriyarki dole gazawarki ta bayyana,saboda haka baiyi qasa a gwiwa ba yanufi qofar dakin yasoma qwanqwasa mata
"Bude mana maryam"
"In bude inyi uwar meye?,jibril kafice min daga daki wallahil azim idan nafito ba zamu kwasheta da dadi ba,maciyin amana kawai,Allah dai yayimin sakayya" saita rushe da kuka sosai mai fidda sauti,kanshi kawai ya girgixa saiya koma da baya ya aje mata ledar ya juya yafice zuwa sashen rufaida.
Cikin so da qauna ta taryeshi,cike da nuna wayewa da sanin me rayuwa take ciki,hakanan ya biye mata,saidai can qasan ranshi yana mamaki kadan kadan idan tayi wani abun,sabida ko maryam daren farkonsu batayi ba bare halima,daga bisani saiya share shima,komai ya kauce daga ranshi ganin cewa ba wani abu daya tadda tattare da ita wanda ba dai dai ba ko zai saka zuciya ko rai cikin zargi.
Wanka mmn amir tasamu tayi cikin bandakinta sannan tasauya kaya,ganin idanunta yasoye,tunani yana neman hanata bacci,saita dauko qur'aninta da dama kullum bai rabo da gefan gadonta,ta bude wasu shafuka tasoma karantawa,babu jimawa taji bacci yazo mata,idanunta har rurrufewa suke,tasamu ta maida qur'anin batayi wata wata ba taja filo ta kwanta.
Mmn ummi kuwa a iya cewa kwanan zaune tayi,sai zirga zirgan shiga bandaki data sameta saboda tashin hankali,tayi kuka har batasan iyaka ba,haka tazauna tasaka agogo a gaba tana kallo,duk daqiqa daya da zata wuce tana lissafawa gamida qissima yanzu abu kaza baban amir din yake,yanzu yaci ace yayiwa rufaidan abu kaza,saita sake rushewa da kuka,haka takusan kwana,kafin wani lokaci kuwa kanta yadinga ciwo,da qyar gefin asuba tasamu bacci yayi awon gaba da ita cike da tarin baqinciki da quncin zuciya.
Qarfe biyar da rabi yashigo dakin,a lokacin tana zaune saman abun sallarta tana jan carbi,duka yaran sun gama sallarsu sun koma baccin,itama jira take ta gama addu'o'inta takoma ta kwanta din kafin gari ya qarasa wayewa,saboda tasan gidan a kacame yake sosai,gashi yaudin tanason zuwa awo ranar da zata likita ne.
Kallo daya tayi masa ta dauke kai,saidai abun ya bata mamaki,batama tsammaci shigowarsa ba adai dai wannan lokacin,don kuwa zamanin maryam bataga idanunshi ba sai goma na safe.
Shi yasoma gaidata har taji abunma bambarakwai,saita amsa kawai,ya tambayi yaran tace sunyi sallah sun koma
"Sannu da qoqari,Allah yayi albarka"
"Amin" ta amsa tana ci gaba da jan carbinta ba tare data sake tanka masa komai ba,tana kallonshi ya gama kame kamensa sannan ya juya zai fita
"Idan gari ya gama wayewa zanje naga likita" waiwayowa yayi cikin kulawa
"Au...lafiya dai ko?"
"Qalau,lokacin komawa awona ne yayi tun wancan satin ban samu zuwa ba saboda hidima"
"Me yasa zaki fashin zuwa ganin likita?,wannan ai sakaci da lafiya ne,ki shirya da wuri ki barma mmn ummi sauran ayyukan,idan kin gama saiki sanarmin" zataso ya sallameta ne kawai a lokacin basai ta tsaya wani binbinin nemanshi ba,amma batason doguwar magana a yanayin da take ciki,saboda haka tace masa to kawai
Qarfe bakwai ta tashi salima suka shiga gyaran gidan,ita kuma tashiga kitchen tadora abin karin safe,don tasan idan tabiye ta mmn ummi bataqi ranar gidan yakuma yini a haka ba,hakanan uban kowama cikin gidan yawuni da yunwa ba damuwarta bane.
Duk zirga zirgar mmn amir din kan idanun mmn ummi,don tunda tafarka qarfe shida tayi salla bata koma ba,saita koma saman kujerarta dake bakin qofar dakin tazauna ta yaye labulen tana ganin duk wani abu da zai gitta ta tsakar gidan,tunanin abinda zata qirqira kawai take wanda zai fiddo bban amir daga dakin rufaidan da farar safiya,yadda zata cusa mata haushi da takaici.
Ranta a bace takebin mmn amir dake kai kawo tsakar gidan tana hidimominta,ji take kamar ma farinciki mmn amir din keyi da wannan lamarin,qwafa taja haushinta na sake cikata,ita ko wani dan bacin rai bata karanta saman fuskarta ba,kamar ma ba matarshi ba,shine zata wani tashi da sassafe tahau aiki,itakam baiwar Allahn batasan ma tanayi ba,don abinda ta iyakancewa ranta zatayi komaine don saboda yaran da kuma karan kanta.
Sai data gama abun karin yaran sukayi wanka gaba dayansu suka karya,tabar saura a kitchen saboda sauran mutanen gidan,ta kintsa tsaf,tana daga zaune tana karyawa don karta zalunci abinda ke cikin nata,saboda jiya batasamu damar sanya komai a bakinta ba,tunanin yadda zata aika yaran kiran abban nasu take,batason shigarsu dakin
"Amir miqomin wayata" ta fada tana kai kofin tea bakinta,dakinta yashiga yafito mata da wayar ya miqa mata,tasa hannu ta amsa sannan tafara laluben number abban amir din,sau biyu tana kira bata shiga,saita aje wayar taci gaba da karyawarta.
Bayan ta gama ta duba jakarta,taga akwai sauran kudade,saboda haka ta zura hijabinta ta miqe tana duban salima
"Zanje,don Allah ki kula dasu,karki barsu suje ko ina,tunda akwai wuta ga cartoons can dana ware musu wadanda duke kalla ki saka musu,kiyi zamanku a daki,tunda mmn ummi nanan zata kula da sauran komai"
"To saikin dawo" daga haka tamusu sallama tafice ba tare data tsaya neman bbn amir din ba.
Qarfe sha daya nasafe tashiga bandakin dake falonta ta silla wanka,sannan taxauna gaban mudubi ta tsara kwalliya tagani ta fada,ta zabi riga da skert da suka kaamaata cikin kayanta tasanya,ta tura daurin dankwalinta gaba goshi sannan ta dawo falo inda tabar bbn amir zaune yana kallo.
Wani fari ta sakar masa gamida sauya takun tafiyarta,ya buda mata hannayensa yana sakar mata murmushi gamida fasa mata kai kan yadda tayi kyau,ta narke ajikinsa sosai tana zuba mishi shagwaba shi kuma yana tambayarta daren jiya
"Yunwa mafa nakeji dear,su mutanen gidan nan basu iya adana baqonsu ba?"
"A'ah na tabbata akwai abinci a kitchen,may be basason matsa mana shi yasa ba wanda suka aiko,bari naje na duba miki sweet,amma ya kamata ki fita ki gaisa da mutanen gidan"fuska ta yatsine tana jin abun wani banbarakwai,don bata tsammaci zaice haka ba
"amma ai nice baquwa,niya cancanci a gaisar" kai ya kada
"Eh,amma idan kika duba ai kece qarama ko?,keya kamata ki dinga zuwa gaidasu" kan ubancan,yo koshi ita yau bata gaisar ba ballantana wasu gajarabul din matanshi,batason bata plan dinta saboda haka tace mishi
"Ba damuwa,amma yunwa nakeji,bari na qoshi tukunna"
"Karki damu,bari na duba gidan"murmushi ta sakar masa
"kayi sauri kadawo,akwai wani daddadan labari dana tanada maka"
"An gama gimbiya" daga haka ya juya yafice,wani wawan tsaki taja tana yatsuna fuska,gaida matanshi kamar wani a qauye?,koko zamansu take?,itakam ba zata juri wannan iskantar ba wlh,duk wadda ta matsu da ita tashigo ta gaidata.
Dakin mmn ummi yanufa yana don yasan aikin gidan kamata yayi ace yana hannunta,tana zaune tun safe yadda tatashi da kayan jikinta,ita daya cikin dakin daga ita sai ummi itama data gaji da zaman ita daya,tana ta 'yan qananun rigingimu tana neman wanda zai dauketa ya fita da ita.
Aiko yana shigowa tagudu daga wajen uwar tayo wajen,ya dauketa yana cillata sama yana mata wasa,ko ummin ba'a yiwa wanka ba bare uwarta tasamu yi tana zaune tana dacin rai,sosai ta qureshi da idanu kamar zata gani sauyawar wani abu daga jikinsa,sai kuwa taga kamar walwalarsa ta dadu,fuskarsa ta qara kyau,wani abu ya tokare mata wuya,tsantsar tsanarshi da haushinsa kamar tatashi ta rufeshi da duka haka takeji
"An gama abincin kari ne?" Wata uwar harara ta watsa masa,ta masa kallon sama da qasa
"Na maka kama da wadda zata zauna tana muku girki kuna ci?,toni ba jaka bace nasan inda yakemin ciwo" daga haka tashige daki abinta,baiso kulata bare subar wani abun fadan,saboda haka yajuya yafice zuwa dakin mmn amir.