Sashe 20
Hangen Dala Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da sauri rufaidan ta qarasa gaban kwanon abincin daya tashi akai tadauki cokalin tayi loma daya,saita hau zaro idanuwa saboda yaji da gishiri,itakanta batasan yajin da gishirin sunkai har haka ba,yaron daya kai mata markden dai yace tarage attaruhun tace haka takeso,yakai mata haka,saita koma tazauna tana jin yadda shinkafar ta tsaitsaya mata a maqogaro tana raba idanu,tare da da tunanin yadda zata nade tabarmar kunyarta.
Can bayan layinsu ya zagaya wajen wani maisaida fura da noni,gefansa kawai mai balangu,ya siya leda daya mmn ummin da yaranta,leda daya mmn amir don yasan bazata iyaci ba itama don bata qaunar yaji,leda daya tashi,yadawo gidan yashiga dakin mmn ummin,tana zaune ita daya,yana iya jiyo motsin yaran cikin dakinta,ya aje ledar yana dubanta
"Maryam,ki fita daga idanuna,banason fitina banason tashin hankali,ki kiyaye tun baki kaini bango ba" daga haka bai saurareta ba yafice yashiga dakin mmn amir.
Fuskarta ba yabo ba fallasa ta amsa sallamarshi,itama yamiqa mata ledar idanunshi nakan farantin dake aje gefanta tarufeshi da wani farantin,da alama itama tadebone ta kasa ci,ya tsammaci zatace wani abu,saidai batace komai ba har ya mata sallama yafito.
Cikin ranshi yadinga ganin qima da martabarta,har kullum kunya sake kamashi take idan yatuna abinda ya aikata mata a baya,sanda yana kan ganiyar neman aure da aurenshi da maryam,yakanji kamar yajawo baya yagoge duk abinda yafarun a baya,saidai babu damar haka,saidai danasani da hausawa ke cewa qeyace.
A baya idan tayi kawaici irin wannan yace munafuncine dason goga masa baqinjini wajen mutane,idan tayi magana yace tacika qorafi duk da ba maganar takeyi ba,duk wanda tayi bata tsira ba,sai a yanxu martabarta take sake fitowa muraran,darajarta take sake yauqaqa a idanunsa.
Wannan karon dakinsa yakoma,yayi shirin kwanciya abinsa kana ybude gurasa balangu da furar yasoma ci.
Baiyi nisa ba taturo qofar dakin cikin kayan barcinta tashigo dauke dai da kwanukan abincin,donta tsara abinda zatayi,dubanta kawai yake takaici yasauko masa,rigar barci ce transparent ana iya ganin pant da bressier dinta,amma ace haka ta ratso cikin gidan zuwa dakunanshi?,yanzu idan wani cikin yaran yaganta fa?.
Sai data aje abincin sannan ta bata rai sosai tana dubanshi,baqinciki biyu,yasiyo abinsa yanaci ba tare daya bata nata ba,sannan ga girkin datasha wahala akanshi baici ba
"Yanzu haka xakamin dear,wallahi na fuskanci an riga da an gama shiga tsakaninmu,randa nasoma girkina na farko ace kaqici ka bige dacin abincin kan titi?"saita fashe da kukan kissa wanda yadinga jinsa har saman kanshi,wannan matsaloli da yawa suke,daga ka toshe matsalar waccar saita waccar ta danno kai?,daga wannan sai wancan?.
Ganin kukan nata nayin yawa yasa dole bayan ya kammala cin abincin yakira sunanta,tadago da hawayen qarya tana dubanshi.
"Gaba daya rufaida kin bani mamaki,yadda na tsammata gaba daya ban tadda haka daga gareki ba,na zaci cewa zan sake samun wani nutsuwar da kwanciyar hankaline daga gareki,sai gashi kina neman bani mamaki,ina shirin ganin abinda ba haka ba daga gareki" fuska tadan yamutsa,saboda babu abinda zancan nasa suke mata sai bata mata rai,itafa arayuwa babu wanda ya taba mata kwatankwacin abinda jibril din yake mata yanzu,donko saurayi magana daya zai gaya mata yanzu ta sauyashi,bata lamunci a dinga gaya mata magaba kai tsaye ba
"Kaman yaya?"
"Kamar yadda nake gani" ya bata amsa shima kai tsaye
"Yanxu duk qoqarin da nakeyi kai baka gani,baka yabamin saima kusheni da kawo matsalolina,duk yadda nake haquri a gidan nan baka gani ba?" Ta fada cikin kuka,don ita harga Allah bata gano laifinta ko daya ba,sai tarin laifinsa dana matansa
"Tunda hakane saika fadi dame dame nake maka".
Tiryan tiryan ya lissafo mata komai,saidai cikin zuciyarta tsaki take ja kawai,tanason maida masa wata zuciyar na kwabarta,saboda tana lissafe nan da rana ita yau zata amshi kudin ankon bikin qawarta,kuma taji daga bakin qawayenta masu aure,idan kika sake wani abun ya hadaku yana iya hanaki kema abinda kike buqata,saboda haka ta faki idanunshi ta yatsina fuska sannan tace
"Shikenan naji,xan gyara"
"Da dai yafi,saboda na auroki ne don dukkaninmu munason juna,na auroki don dukkaninmu muyi farinciki datarayyarmu da juna har lahira,abu nabiyu,irin wadan nan kayan banaso kina yawo dasu cikin gida haka,saboda yarana da sauran masu shigowa wadanda suke ba hurammanki bane,a qa'ida ta addini bai kamaci ace suna ganinki haka na,bugu da qari tarbiyyar yaran gidan,kinsan yaro da riqe abu da fahimta,bare kusan dukkaninsu sun riga dasun tasa,balaifi zaki iyamin ado dasu sanda muke daga ni saike,don Allah ki lura ki kuma gyara" wani abune yasake tsaye mata a wuya,kusun uba,waime jibril yake nufi ne?,kwalliyarma da zata ringa da qananun kayan zai hanata,abinda taci vuri ta kashewa kudi,aqalla ita kanta batasan nawa ta kashe wajen siyan kayayyakin ba,gaskiya ba zata sabu ba wai bindiga a ruwa,bataga uban wanda ya isa ya hanata shigar datayi niyya ba cikin gidan,wannan shine babban abinda zata daina suyi galaba muraran a kanta,ba shakka dole ta rage mishi son yaran nan ba,idan ba haka ba ita za'a cutar da yawa,kuma akwai dambarwa ba 'yar qarama ba,amma a fili saita cuno baki
"To naji" kai ya girgixa cikin mamaki,wasu lokutan halayanta kanyi kamanceceniya dana mmn ummi,mmn amir ce mace daya tak dakan saka gwiwoyinta a qasa ta bashi haquri a duk sanda tayi masa laifi.
Da wannan tasamu tasha kanshi,komai yawuce,don dama shi bamai daukar dogon fushi bane ko a baya,idan yayi dogon fushi to tabbas ka qureshi ne.
**** **** ****** *****
Washegari hakanan badon taso ba tatashi da wuri ta dafa mishi shayi da chips,kamar xata fadi haka ta dinga ji saboda tashin wurin datayi,haka ta dinga aikin takaici nacin ranta,saboda tariga ta saba a gida bata tashi a irin wannan lokacin,suma sun sani ba'a tashinta sai sanda taci baccinta ta gyatse,ko aiki zaiwa mamanta kanta kuwa ba ruwanta,idan ta tashinma batason aikin wahala,zata karbi aikin da zatayi daga zaune ne,shima idan yadauki lokaci saita kawo wani uzurin da zata aje aikin ta barshi.
Bayan ta sallameshi saida ta koma takwanta din kuwa,bata tashi ba sai bayan goma na safe,yara tuni sun soma jin yunwa,tadora shayi a gurguje ta dora musu indomie,ta jibagata ta sauke sannan tashiga sharan gidan,wanda kafin tagama ta jigata ainun,haka ta dinga qorafi da surutai ita kadai,yaran kuwa duk wanda yayi kuskuren yin wani abu ba dai dai ba zaici gyatumarsa.
Mmn amir ce data fuskanta tayi hikimar tattare yaran a dakinta,don tasan tabbas idan mmn ummi ta fuska ta to yauma sai an raba abun fada,itakuwa sam batason tashin hankali,uwa uba kuma tasan hankalin jibril xai tashi fiye da jiya,abinda ita kuma bata fata kenan.
Haka taci gaba da karbar aikinta harna tsayin kwana biyu,wanda kafin sannan ta jigata qwarai,ta zaci abun akwai sauqi bata tsammaci haka ba,randa zata sauke girki tanason ta huta amma tana tsananin kishin miqawa mmn ummi jibril,babu yadda ta iya haka tasaki mmn ummi ta kama,saidai taci alwashi itama kafin mmn ummin tafita saita baro musu bacin rai.
Tunda gari ya waye ranar da zata karbi girkin take cikin walwala da farinciki,bini bini minti daya biyu kaji ta saki waqa wadda ke cike da habaici da baqar magana,sosai ran rufaida yabaci don ta gama yankewa da ita mmn ummi take,tayi qwafa ta quduri abinda zata mata ta huce yakai sau shurin masaki.
Mmn amir kuwa batasan ma me suke ba,tana kwance abinta tana duba wasu daga cikin litattafan marubuta masu ma'ana,sosai takejin dadin karatun,don tana qaruwa da abubuwa a ciki ba kadan ba.
Bayan yagama shirin fitarsa daga dakin rufaidan,yasoma leqa mmn amir din,tana zaune tafito da duka kayanta tana gyarawa da safen kasancewar bata da wani aikin yi,lemon siyarwar ma ta dakata dayi harsai ta sauka,sai ruwan pure water kawai da take saidawa yanzu,tanason bayan tasauka dinne tasake fadada sana'artata,ta qara wasu kalolin lemon da sauran abubuwan sanyi nasha.
Jin shigowarshi yasanyata fitowa falon nata
Kamar koyaushe suka gaisa ya tattambayeta jiki tace alhmdlh
"Idan nadawo ku shirya zamuje mu dubo hajiya bata jin dadi"
"Ashasha,me ya sameta?" Ta tambaya cikin nuna damuwa
"Ciwon qafarta ne yatashi"
"Ayyah,Allah ya sawwaqe ya bata lafiya"
"Amin ya rabbi" ya amsa yana sanya hannunshi cikin aljihunsa.
Dubu guda yaciro
"Kekam kawaicinki kamar yaso yayi yawa"batasan sanda murmushi ya subuce mata ba,kana tace
"Name fa?"
"Indai ba asibiti zakije ba,ko kin qure da yawa bazaki bude baki kice bbbn amir bani kaza ba,yanzu yadda baki girkin nan baki samun 'yar biyar da 'yar naira goma ya kenan?" Murmushi tasaki kawai ta kada kai,babu mutumin da zaice baison ace mishi ungo,to amma idan ya kasance bake daya bace wajen miji,sa'annan bani baninki tayi yawa to babu shakka zakifi kowa baqinji ne a cikinsu,bugu da qari Allah S W T ne kadai baya gajiya da roqo,wannan shine cikakken alfanun sana'a a wajen diya mace.
"Baka ganin ina saida ruwa da lemo?" Ta fada a tausashe
"Ah,kice hajjaju ce nan a gabana" yadda yayi maganar saiya bata dariya
"Duk da hajjajun ce dai ungo amshi wannan ki riqe,don nasan lalurorinku na masu ciki,kar a je a rugurguje ribar da jarin duka" hannu biyu ta amsa zata karba tana godiya saiga rufaida tashigo.
"Idan kagama inada magana" ta fada idanunta akan kudin hannun mmn amir da take niyyar ajewa,wani takaici ya kamata,ai ita datake kan ganiya ita yafi cancanta yadauki kyauta irin haka ya bata,wayasanima ko kullum sai ya bata?,shi yasa baya fashin shiga,kuma dakinta kullum yake fara shiga
"Ganinan zuwa muje" ya fada yana nuna mata hanya,yadda bata kula mmm amir din ba itama saita sake tsumewa,tayi kamar nata ganta ba,tunda aqa'idance ita yakamata tasoma gaidata,na farko ta girmemata a wajen miji,nabiyu kuma har dakinta ta taddata
"Shikenan saina dawo"
"Allah yatsare" ya amsa mata kana yafita.
Yana fitowa sukayi kacibus da mmn ummi wadda aketa gyare gyare tun safe za'a karbi miji,yayin da rufaida ke daga kitchen tana diban abincin kari,saidai duka kunnuwanta na tsakar gidan,gaisawa sukayi itama sannan yamiqa mata kudin cefane,ta amshe cikin walwala ta rakashi da addu'o'i,kana itama yashaida mata zasu duba hajiyan idan yadawo,wani murmushi rufaida tasaki,anzo wajen,plan dinta zai tafi dai dai kenan
"To Allah yakaimu" ta amsa ba tare data tambayi me zasuje yi din ba.
Fitowa rufaidan tayi daga kitchen din,itama gaya mata yayi
"To" tace kawai itama tayi gaba,ganin batayi magana kan nemanshin da tace tanayi ba saiya sanya kai yafice daga gidan,yayin da rufaidan tawuce dakinta tana waqar
"Ahayye sama ruwa qasa ruwa..." Tana wassafa tsiyar da zata tsula anjima.
*kuci gaba da haquri dai,duk sanda kukaji shuru ba shakka wani babban uzuri ne ya kawo tsaikon,sannu sannu bata hana zuwa,jigon ko manufar labarin dai daukar darasi da koyi da kyawawan halayen ciki*.....
Can bayan layinsu ya zagaya wajen wani maisaida fura da noni,gefansa kawai mai balangu,ya siya leda daya mmn ummin da yaranta,leda daya mmn amir don yasan bazata iyaci ba itama don bata qaunar yaji,leda daya tashi,yadawo gidan yashiga dakin mmn ummin,tana zaune ita daya,yana iya jiyo motsin yaran cikin dakinta,ya aje ledar yana dubanta
"Maryam,ki fita daga idanuna,banason fitina banason tashin hankali,ki kiyaye tun baki kaini bango ba" daga haka bai saurareta ba yafice yashiga dakin mmn amir.
Fuskarta ba yabo ba fallasa ta amsa sallamarshi,itama yamiqa mata ledar idanunshi nakan farantin dake aje gefanta tarufeshi da wani farantin,da alama itama tadebone ta kasa ci,ya tsammaci zatace wani abu,saidai batace komai ba har ya mata sallama yafito.
Cikin ranshi yadinga ganin qima da martabarta,har kullum kunya sake kamashi take idan yatuna abinda ya aikata mata a baya,sanda yana kan ganiyar neman aure da aurenshi da maryam,yakanji kamar yajawo baya yagoge duk abinda yafarun a baya,saidai babu damar haka,saidai danasani da hausawa ke cewa qeyace.
A baya idan tayi kawaici irin wannan yace munafuncine dason goga masa baqinjini wajen mutane,idan tayi magana yace tacika qorafi duk da ba maganar takeyi ba,duk wanda tayi bata tsira ba,sai a yanxu martabarta take sake fitowa muraran,darajarta take sake yauqaqa a idanunsa.
Wannan karon dakinsa yakoma,yayi shirin kwanciya abinsa kana ybude gurasa balangu da furar yasoma ci.
Baiyi nisa ba taturo qofar dakin cikin kayan barcinta tashigo dauke dai da kwanukan abincin,donta tsara abinda zatayi,dubanta kawai yake takaici yasauko masa,rigar barci ce transparent ana iya ganin pant da bressier dinta,amma ace haka ta ratso cikin gidan zuwa dakunanshi?,yanzu idan wani cikin yaran yaganta fa?.
Sai data aje abincin sannan ta bata rai sosai tana dubanshi,baqinciki biyu,yasiyo abinsa yanaci ba tare daya bata nata ba,sannan ga girkin datasha wahala akanshi baici ba
"Yanzu haka xakamin dear,wallahi na fuskanci an riga da an gama shiga tsakaninmu,randa nasoma girkina na farko ace kaqici ka bige dacin abincin kan titi?"saita fashe da kukan kissa wanda yadinga jinsa har saman kanshi,wannan matsaloli da yawa suke,daga ka toshe matsalar waccar saita waccar ta danno kai?,daga wannan sai wancan?.
Ganin kukan nata nayin yawa yasa dole bayan ya kammala cin abincin yakira sunanta,tadago da hawayen qarya tana dubanshi.
"Gaba daya rufaida kin bani mamaki,yadda na tsammata gaba daya ban tadda haka daga gareki ba,na zaci cewa zan sake samun wani nutsuwar da kwanciyar hankaline daga gareki,sai gashi kina neman bani mamaki,ina shirin ganin abinda ba haka ba daga gareki" fuska tadan yamutsa,saboda babu abinda zancan nasa suke mata sai bata mata rai,itafa arayuwa babu wanda ya taba mata kwatankwacin abinda jibril din yake mata yanzu,donko saurayi magana daya zai gaya mata yanzu ta sauyashi,bata lamunci a dinga gaya mata magaba kai tsaye ba
"Kaman yaya?"
"Kamar yadda nake gani" ya bata amsa shima kai tsaye
"Yanxu duk qoqarin da nakeyi kai baka gani,baka yabamin saima kusheni da kawo matsalolina,duk yadda nake haquri a gidan nan baka gani ba?" Ta fada cikin kuka,don ita harga Allah bata gano laifinta ko daya ba,sai tarin laifinsa dana matansa
"Tunda hakane saika fadi dame dame nake maka".
Tiryan tiryan ya lissafo mata komai,saidai cikin zuciyarta tsaki take ja kawai,tanason maida masa wata zuciyar na kwabarta,saboda tana lissafe nan da rana ita yau zata amshi kudin ankon bikin qawarta,kuma taji daga bakin qawayenta masu aure,idan kika sake wani abun ya hadaku yana iya hanaki kema abinda kike buqata,saboda haka ta faki idanunshi ta yatsina fuska sannan tace
"Shikenan naji,xan gyara"
"Da dai yafi,saboda na auroki ne don dukkaninmu munason juna,na auroki don dukkaninmu muyi farinciki datarayyarmu da juna har lahira,abu nabiyu,irin wadan nan kayan banaso kina yawo dasu cikin gida haka,saboda yarana da sauran masu shigowa wadanda suke ba hurammanki bane,a qa'ida ta addini bai kamaci ace suna ganinki haka na,bugu da qari tarbiyyar yaran gidan,kinsan yaro da riqe abu da fahimta,bare kusan dukkaninsu sun riga dasun tasa,balaifi zaki iyamin ado dasu sanda muke daga ni saike,don Allah ki lura ki kuma gyara" wani abune yasake tsaye mata a wuya,kusun uba,waime jibril yake nufi ne?,kwalliyarma da zata ringa da qananun kayan zai hanata,abinda taci vuri ta kashewa kudi,aqalla ita kanta batasan nawa ta kashe wajen siyan kayayyakin ba,gaskiya ba zata sabu ba wai bindiga a ruwa,bataga uban wanda ya isa ya hanata shigar datayi niyya ba cikin gidan,wannan shine babban abinda zata daina suyi galaba muraran a kanta,ba shakka dole ta rage mishi son yaran nan ba,idan ba haka ba ita za'a cutar da yawa,kuma akwai dambarwa ba 'yar qarama ba,amma a fili saita cuno baki
"To naji" kai ya girgixa cikin mamaki,wasu lokutan halayanta kanyi kamanceceniya dana mmn ummi,mmn amir ce mace daya tak dakan saka gwiwoyinta a qasa ta bashi haquri a duk sanda tayi masa laifi.
Da wannan tasamu tasha kanshi,komai yawuce,don dama shi bamai daukar dogon fushi bane ko a baya,idan yayi dogon fushi to tabbas ka qureshi ne.
**** **** ****** *****
Washegari hakanan badon taso ba tatashi da wuri ta dafa mishi shayi da chips,kamar xata fadi haka ta dinga ji saboda tashin wurin datayi,haka ta dinga aikin takaici nacin ranta,saboda tariga ta saba a gida bata tashi a irin wannan lokacin,suma sun sani ba'a tashinta sai sanda taci baccinta ta gyatse,ko aiki zaiwa mamanta kanta kuwa ba ruwanta,idan ta tashinma batason aikin wahala,zata karbi aikin da zatayi daga zaune ne,shima idan yadauki lokaci saita kawo wani uzurin da zata aje aikin ta barshi.
Bayan ta sallameshi saida ta koma takwanta din kuwa,bata tashi ba sai bayan goma na safe,yara tuni sun soma jin yunwa,tadora shayi a gurguje ta dora musu indomie,ta jibagata ta sauke sannan tashiga sharan gidan,wanda kafin tagama ta jigata ainun,haka ta dinga qorafi da surutai ita kadai,yaran kuwa duk wanda yayi kuskuren yin wani abu ba dai dai ba zaici gyatumarsa.
Mmn amir ce data fuskanta tayi hikimar tattare yaran a dakinta,don tasan tabbas idan mmn ummi ta fuska ta to yauma sai an raba abun fada,itakuwa sam batason tashin hankali,uwa uba kuma tasan hankalin jibril xai tashi fiye da jiya,abinda ita kuma bata fata kenan.
Haka taci gaba da karbar aikinta harna tsayin kwana biyu,wanda kafin sannan ta jigata qwarai,ta zaci abun akwai sauqi bata tsammaci haka ba,randa zata sauke girki tanason ta huta amma tana tsananin kishin miqawa mmn ummi jibril,babu yadda ta iya haka tasaki mmn ummi ta kama,saidai taci alwashi itama kafin mmn ummin tafita saita baro musu bacin rai.
Tunda gari ya waye ranar da zata karbi girkin take cikin walwala da farinciki,bini bini minti daya biyu kaji ta saki waqa wadda ke cike da habaici da baqar magana,sosai ran rufaida yabaci don ta gama yankewa da ita mmn ummi take,tayi qwafa ta quduri abinda zata mata ta huce yakai sau shurin masaki.
Mmn amir kuwa batasan ma me suke ba,tana kwance abinta tana duba wasu daga cikin litattafan marubuta masu ma'ana,sosai takejin dadin karatun,don tana qaruwa da abubuwa a ciki ba kadan ba.
Bayan yagama shirin fitarsa daga dakin rufaidan,yasoma leqa mmn amir din,tana zaune tafito da duka kayanta tana gyarawa da safen kasancewar bata da wani aikin yi,lemon siyarwar ma ta dakata dayi harsai ta sauka,sai ruwan pure water kawai da take saidawa yanzu,tanason bayan tasauka dinne tasake fadada sana'artata,ta qara wasu kalolin lemon da sauran abubuwan sanyi nasha.
Jin shigowarshi yasanyata fitowa falon nata
Kamar koyaushe suka gaisa ya tattambayeta jiki tace alhmdlh
"Idan nadawo ku shirya zamuje mu dubo hajiya bata jin dadi"
"Ashasha,me ya sameta?" Ta tambaya cikin nuna damuwa
"Ciwon qafarta ne yatashi"
"Ayyah,Allah ya sawwaqe ya bata lafiya"
"Amin ya rabbi" ya amsa yana sanya hannunshi cikin aljihunsa.
Dubu guda yaciro
"Kekam kawaicinki kamar yaso yayi yawa"batasan sanda murmushi ya subuce mata ba,kana tace
"Name fa?"
"Indai ba asibiti zakije ba,ko kin qure da yawa bazaki bude baki kice bbbn amir bani kaza ba,yanzu yadda baki girkin nan baki samun 'yar biyar da 'yar naira goma ya kenan?" Murmushi tasaki kawai ta kada kai,babu mutumin da zaice baison ace mishi ungo,to amma idan ya kasance bake daya bace wajen miji,sa'annan bani baninki tayi yawa to babu shakka zakifi kowa baqinji ne a cikinsu,bugu da qari Allah S W T ne kadai baya gajiya da roqo,wannan shine cikakken alfanun sana'a a wajen diya mace.
"Baka ganin ina saida ruwa da lemo?" Ta fada a tausashe
"Ah,kice hajjaju ce nan a gabana" yadda yayi maganar saiya bata dariya
"Duk da hajjajun ce dai ungo amshi wannan ki riqe,don nasan lalurorinku na masu ciki,kar a je a rugurguje ribar da jarin duka" hannu biyu ta amsa zata karba tana godiya saiga rufaida tashigo.
"Idan kagama inada magana" ta fada idanunta akan kudin hannun mmn amir da take niyyar ajewa,wani takaici ya kamata,ai ita datake kan ganiya ita yafi cancanta yadauki kyauta irin haka ya bata,wayasanima ko kullum sai ya bata?,shi yasa baya fashin shiga,kuma dakinta kullum yake fara shiga
"Ganinan zuwa muje" ya fada yana nuna mata hanya,yadda bata kula mmm amir din ba itama saita sake tsumewa,tayi kamar nata ganta ba,tunda aqa'idance ita yakamata tasoma gaidata,na farko ta girmemata a wajen miji,nabiyu kuma har dakinta ta taddata
"Shikenan saina dawo"
"Allah yatsare" ya amsa mata kana yafita.
Yana fitowa sukayi kacibus da mmn ummi wadda aketa gyare gyare tun safe za'a karbi miji,yayin da rufaida ke daga kitchen tana diban abincin kari,saidai duka kunnuwanta na tsakar gidan,gaisawa sukayi itama sannan yamiqa mata kudin cefane,ta amshe cikin walwala ta rakashi da addu'o'i,kana itama yashaida mata zasu duba hajiyan idan yadawo,wani murmushi rufaida tasaki,anzo wajen,plan dinta zai tafi dai dai kenan
"To Allah yakaimu" ta amsa ba tare data tambayi me zasuje yi din ba.
Fitowa rufaidan tayi daga kitchen din,itama gaya mata yayi
"To" tace kawai itama tayi gaba,ganin batayi magana kan nemanshin da tace tanayi ba saiya sanya kai yafice daga gidan,yayin da rufaidan tawuce dakinta tana waqar
"Ahayye sama ruwa qasa ruwa..." Tana wassafa tsiyar da zata tsula anjima.
*kuci gaba da haquri dai,duk sanda kukaji shuru ba shakka wani babban uzuri ne ya kawo tsaikon,sannu sannu bata hana zuwa,jigon ko manufar labarin dai daukar darasi da koyi da kyawawan halayen ciki*.....