← Book details Hangen Dala Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 20

Sashe 19

Hangen Dala Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tana shigowa mmn amir tadauke kai,ta sake maidawa ga tv kamarma bataga shigowarta ba,yayin da mmn ummi tazuba mata ido tacika tayi fam,ta dinga jifanta da harara,ji take kamar ta tashi ta rufeta da duka ko zataji sassauci cikin zuciyarta.

Kai tsaye ta isa inda bbn amir yake,niyyarta tayi hugging nashi duk da ummi dake hannunsa,amma kallo daya tayiwa idanunsa da fuskarsa ta fahimci cikin bacin rai yake,saboda haka ta gimtse,ta isa daura dashi sosao tazauna tana cewa
"Sannu da dawowa sweethert"
"Yauwa" ya amsa a gintse.

Sai daya tabbatar da kowa ya natsu sannan cikin dakakkiyar murya yajehowa rufaida tambaya
"Meya hana ayi girki yau duka a gidan nan?"duk da tasan wannan tambayar dama na iya biyo baya amma ba haka taso ba,taso ace yayi yadda tace ne ba tare daya titsiyeta a gabansu ba.

Ido ta zaro tana dubanshi
"waya gaya maka haka?,to nikam nayi girki don yanzu haka ma nasu yana kitchen,saidai idan basuje sun dauka ba kawai".

Wani abu ya tsayawa mmn ummi iya wuya,harta kasa magana,tazubawa rufaidab idanu tanajin kamar tatashi tayita jibgarta.

Waiwayawa yayi yadubi mmn amir
"Anyi girki yau a gidan nan?"kai ta kada sannan tace
" gaskiya yau gaba day....."bata qarasa ba rufaida ta tari numfashinta
"Banyi ba?,au hade kai xakuyi kuyimin sharri?,to aje a duba kitchen din agani idan banyi ba".
" ya isa"bbn amir ya dakatar da ita,sannan yacewa mmn amir taci gaba,sai data aje numfashi cikin nutsuwa sannan tace
"Daga safe zuwa rana dai babu abinda aka dafa,saidai ban sani ba koda daren nan".

Sake waiwayawa yayi ga rufaida ya kafeta da ido cikin bacin rai
"Kikace kuma kinyi girki" ciki ciki kamar mai guna guni tace
"Girkin dare ba,ai nayi"
"Meya hana ayi na safe da rana"
"Banajin dadine tunda kafita,hasalima ina kwance tunda kafita"
"Qarya take wallahi....dakaina nashiga namata magana ta gaggayamin magana yadda ranta yaso,shine dalilin daya tunzarani nakiraka kai kuma baka daga ba"
"Ha'an....ina ruwankine?,dake nake maganata?,ki bari a kasa dake saiki dauka ko?" Hayaniyace taso barkewa tsakaninsu ya tsawatar musu kafin kowa yakoma taitayinsa.

Fada sosai yarufe ido yayi musi gaba daya saboda barin yaran da yunwa,duk da mmn ummin ta gaya masa mmn amir tadafa musu wani abu,amma saiya hada duka,saboda dagashi har ita sunsan dasu su biyun yake,sai daya gama mai isarsa sannan yace yana duban rufaida
"Allaha yarufamin asiri saboda haka ban lamunci zama da yunwa ba a gidana,koda almajirin gidan nan banyarda a barsu da yunwa ba bare ku iyalina,qa'idane kowaccw mace ta gama abinci akan kari,daga na safe na rana zuwa na dare,idanma kinyi kan rashin sani to daga yau ki gyara kar in sake jin irin hakan takuma faruwa,koda baki da lafiya ki sanar musu,koki nemi daya daga cikinsu ta amsar miki girkin,kina jina ko?".

Tabdijan danqari kan uba?,yau ita jibril yarufe ido yake mata masifa sabida shirgin yaransa da kucakan matansa?,da idanu take kallon mmn amir zuwa mmn ummi,baqinciki fal yacika zuciyarta,matan da take ganin basu kaita komai da komai ba,amma yau yazaunar da ita yana neman daidaita matsayinta da nasu,har yana mata fada a gabansu?.

Sai kawai tamiqe tana cewa
"Naji" sannan tawucw tafice fuu,mazaunanta na juyawa cikin matsatstun kayan jikinta,wanda su kansu sun bata ran bbn amir din,donme zata dinga irin wannam shigar tafito da ita har waje?,bayan tasani yana da yara wadanda suka fara tasawa,kuma kowa yasan yadda yaro yake da saurin fahimta da tsinkaye,dukkaninsu da idanu suka bita harta fice,yayin da gefe guda farinciki yacika zuciyar mmn ummi,tunda ko banza yau rufaidan tasha fada a gabansu,an kuma bata rashin gaskiya.

Waiwayowa yayi yana dubansu su biyun,duk da yadda ranshi ke masa suya tare da sake shiga mamaki kan sabbin halayen da rufaidan ta tsiro dashi,idanunshi akansu yace..👁️‍🗨️👁️‍🗨️ *HANGEN DALA*👁️‍🗨️👁️‍🗨️
_Ba shiga birni ba_

©️®️ *Safiyya Abdullahi Musa Huguma*

Haske Writers asso 💡

*BABI NA SHA UKU*

*ZAKU IYA SAURAREN LITATTAFAINA A TASHATA TA (SAUTIN HIKIMA) DAKE A YOUTUBE,SAUQI GA MUTANEN DA BASU SON KARATU DA KANSU SAIDAI SAURARE,LITATTAFAN NAWA SUNE KAMAR HAKA*

*ALKAWARIN ALLAH*

*DAURIN BOYE*

*KUNDIN KADDARATA*

*MUTUNCIN MACE*

*DANGANTAKAR ZUCI*

_DA WASU SABBIN DA ZASU ZO MUKU NAN GABA KADAN DA YARDAR ALLAH_

13

"Idan ita batasan tsarina ba,batasan qa'idar gidan ba aiku kun sani,saboda haka daga yau koda wata cikinku keda lalura ban yarda abarmin yara da yunwa ba,kada irin hakan tasake faruwa kunajina?" Mmn amir ce tasoma magana,cikin qanqan dakai da tausa murya
"In sha Allah irin hakan ba zata sake faruwa ba", mmn ummi bakinta taja ta tsuke,duk da ranta ya mata dadi na fadan da yayi ma rufaidan,kuma wala'alla yaudin suyi kwanan takaici,daga haka mmn amir ta miqe tafice,mmn ummi ma tarufa mata baya saboda shiga kitchen tadebo abincin.

Shima miqewa yayi yafice da ummi a hannunshi wadda taqi yarda ya ajeta,yunwa yakeji sosai don yau yajima akasuwa,abinci yake da buqatar ci,don haka yawuce dakin rufaidan kai tsaye.

Zaune yasameta a falo,qafarta daya kan daya,kallo daya ta daga kai tayi masa ta watsar dashi taci gaba da kada qafarta.

Falon cike da sautin waqa,baice da ita komai ba yasoma wucewa ya rage waqar sosai ta yadda ko tashinta bakaji kwata kwata sannan yadawo yazauna kan daya daga cikin kujerun falon yana dubanta.

Qwarai take bashi mamaki,batasan idan tayi laifi ta nuna tayi laifi ba bare ta bada haquri,kullum ita keda gaskiya,saita dauki fushi da kumbure kumbure,tsahon zamansu bazai iya tuna sau nawa tace kayi haquri ba,saiya kauda wannan tunanin yace
"Bani abinci" kai ta tada ta dubeshi kana ta dubi yarinyar hannunshi wadda tuni ya direta saman kujera ta kama kujerar tamiqe abinta tana ta tsalle,saikace shi yafi kowa yara a duniya,motsi kadan yaranshi bini bini yadebo mata yara yashigo mata dasu,ba shakka sai tayi maganinsu,ba zata dauki wannan abun ba wlh,a rubar mata da carfet da katifar kujeru tun bata haifi nata ba ina dalili?
"Saikamaida yarinyar tukunna sannan kaxo kaci abincin" ta fada taba gyara xamanta,yabita da kallo mamakinta yana sake kamashi,yana ganin abun kamar almara amma yaga yana neman wuce gona da iri
"Ki bani abinci kawai ba ruwanki da ita" yafada adan kausashe,saita sauko tanufi inda abincin yake tana qunquni qasa qasa,sarai yajita amma saiya danne kamar baiji ba.

Tun a idanun yaga abincin bai masa ba,uban mai saman miya,ga qamshin attaruhu tun baikai gaci ba,abinda sam baicikin tsarinsa,saboda basir da kuma yara da kowa yasan ba kasafai sukeson abincin mai yaji ba,matan gidan sun riga da sun saba ma,kuma itadinma yasan ta jima da sani din tun kafin suyi aure,har sukayi auren ma bai fasa gaya mata ba idan hira tashigo,to amma sai bai tanka ba,harta gama zubawar ta tashi,ya sanya cokali yasoma ci.

Lomar farko yasoma jin matsaloli game da abincin kala kala,na farko miyar tacika gishiri,sannan bata gama soyuwa ba,baya ga uban mai da yayi mata yawa,na biyu kuma ita ka ta shinkafar batayi laushi na,gatanan dai tayi tsage tsage,a haka yadaure yatafi loma ta biyu wanda anan yaji ya kaure kan harshensa,tilas ya dakata ya dubeta
"Bani ruwa" ya buqaceta da hakan,tunda tsurar abinci ta dire babu mahadi,dan qaramin tsaki taja bayan ta aje wayarta data koma charting dinta ta dora daga inda ta tsaya dazun,don a rayuwarta ta tsani adinga tashinta ana aikenta,ta isa qaramin fridge dinta taciro ruwan babu cup ta aje masa takoma tazauna abinta,baice mata komai ba yadauki kofin yabude yasoma sha.

Daga can dakin mmn ummi kuwa usman ne ya wurgar da cokalin hannunsa yana yarfar da hannun gamida dalilen yawu saboda azabar yaji,mubarak kuwa tuni idanunsa sun hada qwalla donshi yafi usman ma qin abinci mai yaji,dai dai sanda mmn ummi tafito ashirye bayan tayi wankan da masifa ta hanatayi daxu ta dubesu
"A'ah,wannan wanne irin iskancine wannan?,me haka?"
"Yaji umma" usman yafada yana shirin fashewa da kuma,saboda yunwar da yakeji yaso yaci abincin sosai amma babu hali
"Wanne irin yaji?" Ta fada tana zama gefansu,gamida daukar cokalin tayi loma daya ta dandana
"Um,um_um,umum" ta fada tana gyada kai
"Tabdi" ta sake furtawa,ita abun ya mata dai dai,domin kuwa tasamu hanyar cin zarafin rufaida a daren nan,zata qarasa huce takaicinta,saita dauki kwanon abincin tace
"Ina zuwa" fuuu tayi dakin rufaida.

"Garin yaya rufaida abincin nan yayi yaji haka?" Ya jefa mata tambayar yana kallonta,sauke wayar tayi ta dubeshi
"Yafi dadi ai,abinci babu yaji kamar na 'yan ruwa?"
"Amma dai nasha gaya miki ba'amin girki mai yaji ko?,saboda ulcer da basir,ga kuma yara"
"To nidai gsky haka na iya girki na" kafin yace komai mmn ummi ta bankado labulen tashigo riqe da kwano a hannu
"Wannan wanne irin abincine haka?,bbn amir kaga muguntar da matarnan tashirya ashe ko?,to gashinan dai yara sun kasa ci,babu abinda suke sai kuka,wannan ai mugunta ce da rashin mutunci".

Da sauri rufaida tamiqe rana aje wayar hannunta
"Ke maryam ki iya bakinki ki kama kanki,kibar ganin ina daga miki qafa wallahi tausayinki nakeji,banason hauka banason dabbanci kinji ko?,banson jahilci da qananun maganganu....."
Sakin farantin mmn ummi tayi ya tarwatsewa rufaida a daki,ta daki qirjinta tana cewa
"Waye jahilin waye dabba?,wallahi yau saikin gayamin...."
Tsawa bbn amir ya daka musu wadda ta tsaidasu daga yunqurin da kowacce takeyi.

"Waiku wadanne irin mutanene da basu qaunar zaman lafiya sai tashin hankali" cikin raunin murya mmn ummi tace
"Nice bana qaunar zaman lafiya ko ita?,kana gani yautun safe da kalar wulaqancin da takeyi cikin gidan nan amma banga wata cikakkiyar tsawatar mata da kayi ba,yanzu wannan zancan danazo dashi shine rashin qaunar zaman lafiyar?"
"Da kika shigo baki ganni ba zaune?,me yasa baki mutuntani ba kin kawomin qara kigani mezanyi akai?"
"Meko zaka iyayi tariga tashanye ka tamallake ka,sai abunda taga dama takeyi"
"Ya isheni maryam,wuce ki koma dakinki" yafada cikin bacin rai yana nuna mata hanya da yatsa,ta fuskanci yana dab da kaiwa maqura,saboda haka ta juya tana cewa
"Ni duk wanda ya cuceni Allah ya isa wlh,kuma kuyi lokacinku ne,akwai ranar qin dillanci ranar da hajar mai gari ta bata" da wadannan qananun maganganun tajuya ta fice.

Tsahon mintina falon yadauki shuru,saiya dauki ummi yafice,ya direta a qofar dakinsu ba tare daya shiga ba yajuya yafice daga gidan.
Chapter 19 · 0% Book details