Sashe 8
Daga Taimako Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abdulmajeed kuwa ana sauke shi ko canji bai tsaya k'arba ba ya nufi gidansu da sauri,a tsakar gida ya tarar da mahaifinsa mallam Isah yana shan koko da kosai,mahaifiyarsa kuma tana kitchen,Mallam Isah mik'ewa yayi da sauri da ya ga yanda Abdulmajeed ya shigo yace "Subhanallahi Abdul lafiya daga ina"? Abdulmajeed zubewa yayi a kasa yana sauke numfashi kamar Wanda yayi gudu,Hafsat Mahaifiyarsa itama lek'owa tayi tana kallonsa,Abdulmajeed bai ce komai ba ya cigaba da sauk'e ajiyar zuciya,Hafsa fitowa tayi daga kitchen d'in tace "Abdul ba tambayarka ake ba daga ina kake da sassafe nan?,ina Muhibbar? Mallam anya lafiya kuwa ka ganshi fa duk a firgice kamar Wanda aka koro" Hafsat tace tana k'ara kallan Abdulmajeed,"kai bana San Shashanci ana tambayarka lafiya kazo mana gida da sasafe ina ka baro iyalin naka?" Mallam isah yace atsawace.
" Abba aljana ce ta sako in agaba ta hanani sakat,wlh jiya ban runtsa ba,yanzu ma Dana taho sai da ta biyoni,watak'ila ma yanzu ta biyoni gidanan"
Mallam Isah da hafsa had'a baki suka yi wajen rafka sallati Mallam isah yace, "Aljana kuma bangane ba kayi min bayani sosai mai ya had'a ka da Aljana ina Muhibbar?share zufa yayi,ya fara basu labari,tundaga lokacin da Muhibba ta taimakawa Aljana ta shigar musu band'aki,zuwa lokacin da Muhibba ta tafi gidansu sabida tsorata ta da aljanar take yi,da yanda shima aljanar ta ringa tsorata shi har a adaidaita sahu,ya k'ara da "gaskiya Abba bazan iya cigaba da zaman gidanan ba Dan aljanar tana gidan,tashi zanyi daga gidan,wlh badan na ga aljanar da idona ba,na d'auka karya Muhibba take yi,Umma wlh baki ga aljanar ba, sallati Hafsa tayi tana tafa hannu tace "Ikon Allah D🅰G🅰 T🅰IM🅰KO kun janyowa kanku masifa,ni Muhibbar ma nafi tausayawa abinda zai firgita namiji kamar Abdulmajeed sabida tsanin firgita da yayi rigar ma abaibai ya sako ta,lailai tashin hankalin da Muhibba tagani ba kadan bane," Mallam Isah cewa yayi "Hafsa ba dole Aljanu su ringa bibiyarsu ba,kin San irin sakacin Abdulmajeed tun Kafin yayi aure, babu irin fad'an da bana mishi,shine wasa da sallah,baya azkar yanda yaga kanensa nayi,kai tsaye zai shiga band'aki batare da yayi add'ua ba,ballantana azo gasu karatun Qurani ,yanzu da zaki tambayeshi yaushe Rabin da ya d'auko Qurani ya karanta wlh bazai iya gaya miki ba,
Abdulmajeed ne zai ga abinda ya tsorata shi amadadin yayi addua sai dai ya kurma ihu,
nan massallaci yaje bazai je ba,sai dai yayi sallar agida,ki gayamin ya aljanu baza su sako shi agaba ,duk wani Abu dazai kareshi daga sharrin aljanu ba yi yake ba,ko karya ne"? Mallam Isah yace yana kallon Abdulmajeed da ya sunkuyar da kai,Dan yasan tabbas duk maganar da mahaifinsa ya fad'a gaskiya ne,Dan Muhibba ma bata fiye sa dankwalli ba kullum gashinta a bud'e yake, tunani ya hau yi, yanzu akan wanan d'an k'aramin dalilin sai Aljana ta sako su agaba,maganar mahaifinsa ne ya katse masa tunanin da yake,Dan haka in zaka gyara halinka ka gyara,matarka ma naji ance zama take babu dankwalli Nura da yaje gidan kwanaki naji yana fad'awa mamanku,duk wata k'ofa abud'e take da aljanu zasa dame ku,da kake cewa zaka tashi kabar gidan kana da kud'in kama wani gidan ne, Dan in kana tunanin ni zan kama maka Nima nan bani da kud'i,gwara ma ka hak'ura da zancen tashi,zan sa mallamai suje suyi sauk'a agidan,kuma sai Ku daina sakaci da addua,insha Allahu zata daina tsorata Ku,gidan ya daina rabo da karatun Qurani,in bazaku iya karantawa ba kuringa kunawa, awaya,"nasiha Mallam Isah yayi mishi sosai ya bashi addu'oi,godiya yayi wa Mahaifinsa ya mik'e ya nufi d'akinsu da samarin gidan ke kwana Dan barcine a idonsa yana kwanciya ya hau tunanin babu yanda zaayi ya cigaba da zama agidan zai nemi kud'i ya kama wani gidan,da wanan tunanin barci yayi awon gaba dashi.
K'arfe hud'u na yamma ya shirya ya nufi gidansu Muhibba a machine d'in kaninsa,yana isa gidan ya samu Mallam Hashimu a k'ofar gida yana zaune shi da wani makocinsu,parking yayi ya tsuguna har kasa ya gaishe su,suka amsa,Mallam Hashimu tambayarsa ya hau yi lafiya suke ta gwada wayarsa yana ringing bai d'auka ba,sai a lokacin ya tuna wayar na gida,karya ya mishi da wayarsa fad'uwa tayi shima yana kira ba a d'aga ba,Malam Hashimu ce masa yayi jiya Muhibba tazo ta fad'a musu abinda ke faruwa dama shi yasa yake neman shi ,anan yake fad'a masa yasa ayi musu sauk'ar Qur'ani a gidan,insha Allahu aljanu zasu daina damunsu,godiya Abdulmajeed yayi mishi,Mallam Hashimu yace ya shiga ciki bari yah kira masa Muhibba,d'akin da suke zance da Muhibba kafin suyi aure ya shiga ya zauna,Muhibba da bata Dade da fitowa daga wanka ba tana zaune agaban mudubi tana so ta shafa mai Abdulmajeed ne ya fado mata arai ta kasa shafa man,tana cikin Tunanin Abdulmajeed Mallam Hashimu ya d'aga labulen d'akin yace mata taje Abdulmajeed na kiranta yana d'akin yayanta,wani irin farinciki ne ya rufe ta,ta mik'e da sauri ta zura doguwar Riga ta fesa turaren Nafeesa tayi waje,tana zuwa k'ofar d'akin gabanta ya hau fad'uwa Dan bata san ya zasu kwashe da Abdulmajeed,sallama tayi ta shiga ahankali,Abdulmajeed kuwa Dama yana Shiga ya had'e rai,Muhibba sunkuyar da kanta tayi sakamakon kallon da yake jifanta dashi,"sannu da zuwa " Muhibba race tana k'ara sunkuyar dakai,Abdulmajeed wani mugun kallo ya mata yace " Muhibba Ashe baki da hankali ni zaki yiwa karya kice min tsohuwa ce tayi bara kika bata abinci Ashe aljana kika bud'ewa k'ofa ta shigar min band'aki,"Muhibba jikinta ne yafara rawa Dan bata tab'a ganin b'acin ran Abdulmajeed haka ba,cikin rawar murya tafara magana " Dan Allah kayi hakuri nayi kuskure wlh bansan aljana na bud'ewa k'ofa ba," Dalla rufemin baki wane irin gargadi ne ban miki ba akan kwashe kwashe ai gashi nan kin janyo wa kanki D🅰G🅰 T🅰IM🅰KO,Dan babu abinda ya shafeni,haka zamu koma gidan ayau duk abinda tayi miki ke kika janyowa kanki,Dan da baki bud'e mata k'ofa ba babu yanda zata shigo gidan,Surayya da ta ganta ta kulle k'ofarta kinga tana can hankalinta kwance,tunda ya fara magana hawaye ke zubo mata,"Abdul wlh bazan iya kwana agidanan ba ni nasan mai nake gani," Abdulmajeed d'aga mata hannu yayi yace " wa ya janyo?babu abinda ya dameni jiya barcina nasha lafiya lau babu komai a gidana ke da kike bud'e mata k'ofa ke kike ganinta dan haka" shiru yayi sakamakon ganin aljanar nan daya yi abayan Muhibba ayanayi na ban tsoro ta gwalalo idonta gabad'aya tana kallonsa,jikinsa ne ya hau rawa ,cikinsa yayi wani irin murd'awa ya saki tusa mai shegen d'oyi ihu ya saki yana " kiyi min rai wlh karya nake jiya ban runtsa ba wayyo Allahna" Muhibba ido ta gwalo tana kallonsa cikin tsananin mamaki Dan ta waiga bata ga komai ba,Abdulmajeed ganin Ajanar ta nufoshi yasa yayi waje dagudu,sabida gigicewar da yayi d'akinsu Muhibba ya shige ya kullo k'ofar.
[9/22, 12:18] Sadnaf: 🙆🙆 *D🅰G🅰 T🅰IM🅰KO*😭😭
*Written by*
💅💅 *SADNAF*💞
PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
_We don't just entertain and educate we touch the heart of the readers_p.m.l
*TRUE LIFE STORY*
🙆🙆 *D🅰G🅰 T🅰IM🅰KO*😭😭
*Written by*
💅💅 *SADNAF*💞
PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
_We don't just entertain and educate we touch the heart of the readers_p.m.l
*TRUE LIFE STORY*
*#[email protected]*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*
PAGE 9
Muhibba itama waje tayo da gudu duk tabi ta rude,kicibis suka yi da Mahaifiyarta Dan itama agigice tafito daga palon data ga shigewar Abdulmajeed abakin k'ofar palon "Muhibba lafiya kuwa mai ya faru naga Abdulmajeed ya Shiga d'akinku da gudu," "wlh umma Nima bansani mai yagani ba muna cikin magana ya fito aguje," Muhibba tace a dai dai lokacin da take kwankwansa k'ofar d'akinsu tana ",Abdul lafiya mai ya faru ne,"? Abdulmajeed da sabida tsabar tsorata da yayi dan ayau Aljanar tafi masifar bashi tsoro,Dan fitsari ya saki ajikinsa,ya had'a gumi in banda rawa babu abinda jikinsa yake,sai da Muhibba ta k'ara kwankwasa k'ofar ya tuna Ashe a gidansu muhibba yake, wani irin kunya da tsoro ne ya k'ara rufeshi,ya kalli jikinsa da ya jike da fitsari,muryar Mallam Hashimu ne ya dawo shi daga tunanin da yake Dan Maryam k'ofar gida ta tafi ta gaya mishi abinda ke faruwa,"Abdulmajeed kunya ce ta k'ara rufeshi ya kasa bud'e k'ofar Dan fararen kaya ne ajikinsa,suna ganinsa zasu San yayi fitsari"Abdulmajeed ka bud'e k'ofar mana mai ya faru ne"? Mallam Hashimu yace yana k'ara buga k'ofar,bud'e k'ofar yayi ahankali yayi waje da gudu,Mallam Hashim ya rufa mishi baya, Muhibba sallati ta saki tana " Umma na shiga uku ko dai Abdul gamo yayi"? Maryam itama bayansu tabi tana sallati Dan itama Abdulmajeed ya tsorata ta Dan ta rasa mai yasa shi gudu, Abdulmajeed na k'ok'arin hawa machine d'insa Mallam Hashimu ya rik'eshi yace" Abdulmajeed lafiyarka kuwa mai yake damunka mai ka gani daya tsorata ka haka" da sauri yace " Wlh wanan aljanar ce ta sako ni agaba duk in da nayi sai na ganta,narasa mai yasa take bibiyata,tun jiya ta hargitsani, ta hanani zaman lafiya duk da ba ni na bud'e mata k'ofa bar,na rasa yanda zanyi,"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun, Aljanar kagani ka gudu kenan" Mallam Hashimu yace atsorace,"eeee wlh yanzu haka ma tana gidanku,yace yana k'ok'arin Tayar da machine d'insa, Muhibba a gigice itama ta fito waje Dan gabad'aya Abdulmajeed ya rudata,hangosu da tayi da Mallam Hashimu ne yasa ta fasa k'arasawa wajensu,Abdulmajeed kuwa hango Muhibbar da yayi a k'ofar gida ne yasa ya ja machine d'insa da gudu yatafi Dan yana jin kunyar karyar da ya mata,binshi su kayi da kallo, Muhibba ta k'arasa gurin Mallam Hashimu da ya daskare a tsaye,"Baba wai mai yace ma ya tsorata shi ne"? Muhibba tace cikin tashin hankali, ajiyar zuciya Mallam Hashimu yayi yace "Muhibba kuna cikin tashin hankali ke da mijinki kuna bukatar taimako,"
"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun Baba wai mai yace ma ko shima aljanar ce take tsorata shi" Muhibba tace hawaye na zubo mata
"Zo mu shiga ciki Muhibba maganar bata tsayuwa bace"
" Abba aljana ce ta sako in agaba ta hanani sakat,wlh jiya ban runtsa ba,yanzu ma Dana taho sai da ta biyoni,watak'ila ma yanzu ta biyoni gidanan"
Mallam Isah da hafsa had'a baki suka yi wajen rafka sallati Mallam isah yace, "Aljana kuma bangane ba kayi min bayani sosai mai ya had'a ka da Aljana ina Muhibbar?share zufa yayi,ya fara basu labari,tundaga lokacin da Muhibba ta taimakawa Aljana ta shigar musu band'aki,zuwa lokacin da Muhibba ta tafi gidansu sabida tsorata ta da aljanar take yi,da yanda shima aljanar ta ringa tsorata shi har a adaidaita sahu,ya k'ara da "gaskiya Abba bazan iya cigaba da zaman gidanan ba Dan aljanar tana gidan,tashi zanyi daga gidan,wlh badan na ga aljanar da idona ba,na d'auka karya Muhibba take yi,Umma wlh baki ga aljanar ba, sallati Hafsa tayi tana tafa hannu tace "Ikon Allah D🅰G🅰 T🅰IM🅰KO kun janyowa kanku masifa,ni Muhibbar ma nafi tausayawa abinda zai firgita namiji kamar Abdulmajeed sabida tsanin firgita da yayi rigar ma abaibai ya sako ta,lailai tashin hankalin da Muhibba tagani ba kadan bane," Mallam Isah cewa yayi "Hafsa ba dole Aljanu su ringa bibiyarsu ba,kin San irin sakacin Abdulmajeed tun Kafin yayi aure, babu irin fad'an da bana mishi,shine wasa da sallah,baya azkar yanda yaga kanensa nayi,kai tsaye zai shiga band'aki batare da yayi add'ua ba,ballantana azo gasu karatun Qurani ,yanzu da zaki tambayeshi yaushe Rabin da ya d'auko Qurani ya karanta wlh bazai iya gaya miki ba,
Abdulmajeed ne zai ga abinda ya tsorata shi amadadin yayi addua sai dai ya kurma ihu,
nan massallaci yaje bazai je ba,sai dai yayi sallar agida,ki gayamin ya aljanu baza su sako shi agaba ,duk wani Abu dazai kareshi daga sharrin aljanu ba yi yake ba,ko karya ne"? Mallam Isah yace yana kallon Abdulmajeed da ya sunkuyar da kai,Dan yasan tabbas duk maganar da mahaifinsa ya fad'a gaskiya ne,Dan Muhibba ma bata fiye sa dankwalli ba kullum gashinta a bud'e yake, tunani ya hau yi, yanzu akan wanan d'an k'aramin dalilin sai Aljana ta sako su agaba,maganar mahaifinsa ne ya katse masa tunanin da yake,Dan haka in zaka gyara halinka ka gyara,matarka ma naji ance zama take babu dankwalli Nura da yaje gidan kwanaki naji yana fad'awa mamanku,duk wata k'ofa abud'e take da aljanu zasa dame ku,da kake cewa zaka tashi kabar gidan kana da kud'in kama wani gidan ne, Dan in kana tunanin ni zan kama maka Nima nan bani da kud'i,gwara ma ka hak'ura da zancen tashi,zan sa mallamai suje suyi sauk'a agidan,kuma sai Ku daina sakaci da addua,insha Allahu zata daina tsorata Ku,gidan ya daina rabo da karatun Qurani,in bazaku iya karantawa ba kuringa kunawa, awaya,"nasiha Mallam Isah yayi mishi sosai ya bashi addu'oi,godiya yayi wa Mahaifinsa ya mik'e ya nufi d'akinsu da samarin gidan ke kwana Dan barcine a idonsa yana kwanciya ya hau tunanin babu yanda zaayi ya cigaba da zama agidan zai nemi kud'i ya kama wani gidan,da wanan tunanin barci yayi awon gaba dashi.
K'arfe hud'u na yamma ya shirya ya nufi gidansu Muhibba a machine d'in kaninsa,yana isa gidan ya samu Mallam Hashimu a k'ofar gida yana zaune shi da wani makocinsu,parking yayi ya tsuguna har kasa ya gaishe su,suka amsa,Mallam Hashimu tambayarsa ya hau yi lafiya suke ta gwada wayarsa yana ringing bai d'auka ba,sai a lokacin ya tuna wayar na gida,karya ya mishi da wayarsa fad'uwa tayi shima yana kira ba a d'aga ba,Malam Hashimu ce masa yayi jiya Muhibba tazo ta fad'a musu abinda ke faruwa dama shi yasa yake neman shi ,anan yake fad'a masa yasa ayi musu sauk'ar Qur'ani a gidan,insha Allahu aljanu zasu daina damunsu,godiya Abdulmajeed yayi mishi,Mallam Hashimu yace ya shiga ciki bari yah kira masa Muhibba,d'akin da suke zance da Muhibba kafin suyi aure ya shiga ya zauna,Muhibba da bata Dade da fitowa daga wanka ba tana zaune agaban mudubi tana so ta shafa mai Abdulmajeed ne ya fado mata arai ta kasa shafa man,tana cikin Tunanin Abdulmajeed Mallam Hashimu ya d'aga labulen d'akin yace mata taje Abdulmajeed na kiranta yana d'akin yayanta,wani irin farinciki ne ya rufe ta,ta mik'e da sauri ta zura doguwar Riga ta fesa turaren Nafeesa tayi waje,tana zuwa k'ofar d'akin gabanta ya hau fad'uwa Dan bata san ya zasu kwashe da Abdulmajeed,sallama tayi ta shiga ahankali,Abdulmajeed kuwa Dama yana Shiga ya had'e rai,Muhibba sunkuyar da kanta tayi sakamakon kallon da yake jifanta dashi,"sannu da zuwa " Muhibba race tana k'ara sunkuyar dakai,Abdulmajeed wani mugun kallo ya mata yace " Muhibba Ashe baki da hankali ni zaki yiwa karya kice min tsohuwa ce tayi bara kika bata abinci Ashe aljana kika bud'ewa k'ofa ta shigar min band'aki,"Muhibba jikinta ne yafara rawa Dan bata tab'a ganin b'acin ran Abdulmajeed haka ba,cikin rawar murya tafara magana " Dan Allah kayi hakuri nayi kuskure wlh bansan aljana na bud'ewa k'ofa ba," Dalla rufemin baki wane irin gargadi ne ban miki ba akan kwashe kwashe ai gashi nan kin janyo wa kanki D🅰G🅰 T🅰IM🅰KO,Dan babu abinda ya shafeni,haka zamu koma gidan ayau duk abinda tayi miki ke kika janyowa kanki,Dan da baki bud'e mata k'ofa ba babu yanda zata shigo gidan,Surayya da ta ganta ta kulle k'ofarta kinga tana can hankalinta kwance,tunda ya fara magana hawaye ke zubo mata,"Abdul wlh bazan iya kwana agidanan ba ni nasan mai nake gani," Abdulmajeed d'aga mata hannu yayi yace " wa ya janyo?babu abinda ya dameni jiya barcina nasha lafiya lau babu komai a gidana ke da kike bud'e mata k'ofa ke kike ganinta dan haka" shiru yayi sakamakon ganin aljanar nan daya yi abayan Muhibba ayanayi na ban tsoro ta gwalalo idonta gabad'aya tana kallonsa,jikinsa ne ya hau rawa ,cikinsa yayi wani irin murd'awa ya saki tusa mai shegen d'oyi ihu ya saki yana " kiyi min rai wlh karya nake jiya ban runtsa ba wayyo Allahna" Muhibba ido ta gwalo tana kallonsa cikin tsananin mamaki Dan ta waiga bata ga komai ba,Abdulmajeed ganin Ajanar ta nufoshi yasa yayi waje dagudu,sabida gigicewar da yayi d'akinsu Muhibba ya shige ya kullo k'ofar.
[9/22, 12:18] Sadnaf: 🙆🙆 *D🅰G🅰 T🅰IM🅰KO*😭😭
*Written by*
💅💅 *SADNAF*💞
PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
_We don't just entertain and educate we touch the heart of the readers_p.m.l
*TRUE LIFE STORY*
🙆🙆 *D🅰G🅰 T🅰IM🅰KO*😭😭
*Written by*
💅💅 *SADNAF*💞
PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
_We don't just entertain and educate we touch the heart of the readers_p.m.l
*TRUE LIFE STORY*
*#[email protected]*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*
PAGE 9
Muhibba itama waje tayo da gudu duk tabi ta rude,kicibis suka yi da Mahaifiyarta Dan itama agigice tafito daga palon data ga shigewar Abdulmajeed abakin k'ofar palon "Muhibba lafiya kuwa mai ya faru naga Abdulmajeed ya Shiga d'akinku da gudu," "wlh umma Nima bansani mai yagani ba muna cikin magana ya fito aguje," Muhibba tace a dai dai lokacin da take kwankwansa k'ofar d'akinsu tana ",Abdul lafiya mai ya faru ne,"? Abdulmajeed da sabida tsabar tsorata da yayi dan ayau Aljanar tafi masifar bashi tsoro,Dan fitsari ya saki ajikinsa,ya had'a gumi in banda rawa babu abinda jikinsa yake,sai da Muhibba ta k'ara kwankwasa k'ofar ya tuna Ashe a gidansu muhibba yake, wani irin kunya da tsoro ne ya k'ara rufeshi,ya kalli jikinsa da ya jike da fitsari,muryar Mallam Hashimu ne ya dawo shi daga tunanin da yake Dan Maryam k'ofar gida ta tafi ta gaya mishi abinda ke faruwa,"Abdulmajeed kunya ce ta k'ara rufeshi ya kasa bud'e k'ofar Dan fararen kaya ne ajikinsa,suna ganinsa zasu San yayi fitsari"Abdulmajeed ka bud'e k'ofar mana mai ya faru ne"? Mallam Hashimu yace yana k'ara buga k'ofar,bud'e k'ofar yayi ahankali yayi waje da gudu,Mallam Hashim ya rufa mishi baya, Muhibba sallati ta saki tana " Umma na shiga uku ko dai Abdul gamo yayi"? Maryam itama bayansu tabi tana sallati Dan itama Abdulmajeed ya tsorata ta Dan ta rasa mai yasa shi gudu, Abdulmajeed na k'ok'arin hawa machine d'insa Mallam Hashimu ya rik'eshi yace" Abdulmajeed lafiyarka kuwa mai yake damunka mai ka gani daya tsorata ka haka" da sauri yace " Wlh wanan aljanar ce ta sako ni agaba duk in da nayi sai na ganta,narasa mai yasa take bibiyata,tun jiya ta hargitsani, ta hanani zaman lafiya duk da ba ni na bud'e mata k'ofa bar,na rasa yanda zanyi,"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun, Aljanar kagani ka gudu kenan" Mallam Hashimu yace atsorace,"eeee wlh yanzu haka ma tana gidanku,yace yana k'ok'arin Tayar da machine d'insa, Muhibba a gigice itama ta fito waje Dan gabad'aya Abdulmajeed ya rudata,hangosu da tayi da Mallam Hashimu ne yasa ta fasa k'arasawa wajensu,Abdulmajeed kuwa hango Muhibbar da yayi a k'ofar gida ne yasa ya ja machine d'insa da gudu yatafi Dan yana jin kunyar karyar da ya mata,binshi su kayi da kallo, Muhibba ta k'arasa gurin Mallam Hashimu da ya daskare a tsaye,"Baba wai mai yace ma ya tsorata shi ne"? Muhibba tace cikin tashin hankali, ajiyar zuciya Mallam Hashimu yayi yace "Muhibba kuna cikin tashin hankali ke da mijinki kuna bukatar taimako,"
"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun Baba wai mai yace ma ko shima aljanar ce take tsorata shi" Muhibba tace hawaye na zubo mata
"Zo mu shiga ciki Muhibba maganar bata tsayuwa bace"