Sashe 11
Bakar Akida Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Inna amsa mata tayi kana ta tashi ta fice daga dakin tana cewa yau dai yayarki ta kawo maki ziyara tunda ke baki shiga sashen su, ai idan abu ya wuce barinsa akeyi!"Inna Baraka tace tare da wucewa zuwa aikinta."
"Salma da murmushi ta kalli karime ta ce"Sannu karime yau kece asashen namu?"
"Ni ce Salma dan Allah kiyi hakuri sai yanzu na gane hassada ga mai rabo taki ce!"Wallahi ina sonki salma Innata ce ke ta kitsa min komai duk abinda nikeyi miki ita ke sakani!"Ko yanzu aboye ne na shigo inda kuke,"Amma yanzu nasan cewa "Karya fure takeyi bata 'ya'ya!"kiyi hakuri!Bamu kyauta muku ba ni da iyayena kuna zaune da mu da zuciya daya mu kuma muna jin haushinku!"Salma ki yafe mana"Kinji 'yar uwata!"
"Hannunta ta kamo ta hade da nata, tace babu komai karime na yafe miki komai ya wuce duk abinda kike min ban taba kallonki da ko daya ba!Harma su inna da baba"Nasan Sharrin zuciya ne!"
"Karime murmushi tayi jikinta asanyaye tare da jin kunyar salma ta ce nagode 'Yar uwata!"
"Babanmu ya ce min aurenki za'ayi makon nan mai zuwa?"
"Eh in shaa Allah karime,"Ki tayani addu'ah domin ni har yanzu ina jin tsoro da fargabar shiga gidan Dr.Salman saboda *BAK'AR AK'IDA* Irin ta danginsa kinsan sun tsani talaka ya rabe su!"
"Babu abinda zai faru da ke Salma sai alheri da jin dadin rayuwa."
Allah ya sanya alheri ina tayaki murna domin salman mutumen kirki ne, Allah ya sa ayida mu"
"Ameen,Karime nagode Allah ya nuna mana naku!"Shin Ina Dan ummarunki ne?Ko yayi tafiya ne? na daina ganinsa!""
"Mtwssssa dan Allah ki daina min zancen sa!" Yanzun nan ma na koreshi! domin ni nagaji da gafara sa banga qaho ba!"Mutum kullum ta-tau kamar jijiya!"Nikam gaskiya nagaji bazan iya rayuwa da shi ba ahakan!"baya iya tabuka min komai!"Kinga fa ko irin... !"
"Haba karime!"Salma tace tare da dakatar da ita!"Meye aibun shi!?Sai naga yana da mutunci kirki ilimi da addini!"
"Aibun shi matsiyaci ne!"Salma.''Me akeyi da talauci ai ko mu da ke zaune acikinsa kullum muna addu'ar Allah ya fidda mu daga cuta ya bamu lafiya!"Ke kinyi arziki Allah yayi maki gyadar dogo saura ni da sauran!"Kin isa barkah shiyasa nazo in tayaki murnar barka da arziki salma!"
"Menene na barkah kuma aciki Karime?"Dama ace kin min barka ne kan nasamu miji nagari zanyi aure in tufawa kaina asiri da nafi jin dadin hakan!"Amma ace barka kike min ta samun mai arziki!?Nikam wannan baya cikin tsarina!"Ya kamata Ki gane shi samu da rashi duk na Allah ne!"Yaushe kika koyi wannan *BAK'AR AK'IDA* ta banzah!"Kina yar talaka kice ke sai mai kudi kike so karime!?"To wallahi kinyi babban kuskure dan ba'ayiwa Allah wayo masani ne akan dukkan komai!"Kuma shi ne mai bayarda mulki da arziki ga wanda yaso!"Idan Allah ya tashi jarabtarki sai yabaki mai kudin karshe kisha wuya!"Ni kaina da kike gani wai zan auri salman wallahi Allah ne shaidata ni kudin shi baya agabana!Kuma naso ace a talauce zan aure shi daga baya muyi arziki atare nafi son hakan!"Kuma ko yanzu Allah na iya maida shi talaka kamar mu!"Dan haka kiji tsoron Allah ki so mai sonki da zuciya daya karime!"Salma tace fuskarta a daure cikin rashin jin dadin abinda karime tayiwa Dan ummaru!"
"Cikin yanayin nadama ta dago kanta zuwa gareta tace na fahimceki salma Allah ya yafe min nasan nayi kuskure abaya kudi ne kawai agabana,Tare da rudi na innata,Hakika ta daurani akan tafarki marar kyau!" sai yanzu na gane da kika fargar da ni gaskiya!"Kuma in shaa Allahu zan nemo shi in bashi hakuri!"Amma salma duk da hakan Danummaru ya cika matse hannu sosai ya kamata ace dan mayukan nan su turare da sauran yan kayan nan na makwalashen kanti da naga ana kasowa abokaina nima yayi min inji dadi komai dai rashinsa yafi karfin su dan iya kudin ka iya shagalinka ne karfi baifi jiki ba!"Ai wannan ma wani abu ne!"saboda rayuwa ce da zamani yazo mana da ita salma!"
"Hmnnnn karime kenan awani wurin kina da gaskiya amma ki qara yin hakuri watarana sai labari."Yanzu kiyi kokari ki bashi hakuri saboda baki kyauta ba kuma shawarata ita ce ki damu da wanda ya damu da ke!"Ki roki Allah ya hada arzikin ku."
"To salma zanyi kokarin yin hakan nagode zan wuce kada inna ta nemeni, amma salma nifa kallonki nike tayi tun dazu naga sai wani sheqi kikeyi kinyi kyau hakan...kamar wata sabuwa ba ke ba?"Ko duk amarchin ne wallahi ba karya kin canja sai haske kikeyi kamar tauraruwa?"Karime ta ce harda shafa fuskar salma da ke walwalniya kamar madubi tayi (smooth)"
"Murmushi tayi tare da duban karime ta ce baki rabo da abin dariya ki wani ce kamar bani ba,Nice dai salmarki...."To daman Hajiya Raliya qawar Maman salman ce ta kaini gidan wata Aminiyar su hamshaqiya kuma kwararriya Mai sayarda komai da ya shafi jiki wato Hajiya Amina Na'amore duka yau kwana na Hudu ne ina zuwa amma ni kaina naga canji wato ita aikinta yana kyau, sha yanzu magani yanzu ne"
"Haba gaske dai kice naira ce kwance a fuskar ki."Ke kam kin fara komawa kalar masu kudi!"Yanzu nima ina so in gyara tawa fuskar ko zan haska ranar aurenki!"Zatayi min?"
"Eh mana ai matar batada matsala!"Ga kayanta da sauki da rahusa, ga aiki kuma ko'ina tana tura kayanta, kedai bari gobe zamuje tare idan aka qare min sai tayi miki ni zan biya kudin naki"
"Yawwa salma nagode."Bari inyi hanzari n shiga gida nabaro inna zata daura sanwa."Niema muje in taya Inna aiki ta fita da jimawa!"To muje sai gobe idan nazo!"To yayi Allah ya kai mu."In ji salma.
"Amin karime tace Nagode Sannan tayi sallama da Inna Baraka ta wuce sashen su cikin jin dadi."
"Bari kawai Abban minal yaya mai gado ta nuna min bani kowa!"Kuma bani bakin komai ni da 'yata a rayuwarta!"Duk fa abinda na labarta maka shi ne ya faru!"Babu abinda bata ce mana ba!"Akan salman ai d'a baifi d'a ba!"Saboda wata can talakar banza marar gata!"Za'a wulaqanta min minal!"Abinda bazai taba yuyuwa ba ne domin bazan dauki raini!"Ba awurin kowa wallahi!"
"Numfasawa yayi bayan zurfin tunanin da yayi akan zantukan Hajiya zainab din."sannan ya ce"Naji kuma dukkan abinda ya faru!" Gaskiya abin ba dadi amma kisani yadda muke kare lafiyar Minal, haka itama kariyar lafiyar salman takeyi!"Ya kamata muyi musu uzuri zainab!Da salman da minal duk daya ne ya kamata abasu abinda suke so aimasu adalci!"Kada zuciya da saurin fushi yasa muyi da na sani...!"
"Haba!Abban minal wane Dana sani kuma!? Ai ana yinsa ne idan ana tare!Kuma ni minal nasani kamar yadda itama da d'anta tafi damuwa!"Na riga na fada mata wallahi bani ba ita kuma minal bazata taba auren d'anta ba"Domin bazata taba zama da ' Yar matsiyatah amatsayin kishiyarta ba!"Dan haka dole ne a fasa zancen auren.....!"
"Dakatah zainab...Bana son shirmen banza!"A fasa auren fa kinka ce!?To Saboda me!? Salman ne ya ce yafasa!?Ko ita minal din tace maki tafasa!?"
"Ai Ko basu fada ba ni na fada!"saboda ance labarin zuciya a tambayi fuska na hango farinciki kwance a fuskar salman Kasan daman shi ba so yakeyi ba!"Kuma yanzu mahaifiyar sa ta goya masa baya!"Maganin kar ayi kar afara!"Dan haka muma zamu ba minal hakuri ta tsaya jiran mai sonta ba wanda ita ke son sa ba!"Yanzu haka da kyar ni da Nidal,muka samu ta kwanta bacci ko zata samu sassauci!"
"Yanzu zainab meye zamu cewa mutanen da da muka gayyata!?Yanzu duk shirin mu ya zama na banza kenan!"A gaskiya dole ne mu samu mafita...........!"
🏻👸🏻
BAKAR AKIDA
©TASKAR NABEELA DIKKO
®PEN WRITERS ASSOCIATION
Page 81/85
_Dedicated to my little princess Mufeeda Ameenu😍 Allah ya nuna min ranar aurenki Amin._
________________________________
"Gidan malam Abu Sufyan ne cike da jama'ar binni da na qauye."
Ba kowa bane face Hajiya Raliya da jama'arta ta arziki da ta gayyato domin kawo kayan lefen salma saboda duk dangi Hajiya mai gado sunce su bazasu iya shiga wannan unguwa ta qauyawa talakawan da wasun su duk mayu ne!"A cewar su wai duk garin cin maganin arzikine talakawan ke komawa mayu!"Dalilin da yasa hajia Raliya ta nemo mutanen arziki suka kawo kayan da yawan su har baya faduwa babu kawai ce a ba'a saka aciki ba!"Dozin akwatuna biyu kalolin kayan sunfi dari su sarka jaka gyale da sauran su tamkar wani kanti har su gwala gwalai ba'a barsu abaya ba!"Kaya dai na arziki."Sai masha Allah."
"Tarba ta arziki da mutunci dangin Inna baraka sukayiwa su Hajiya Raliya."
"Yan uwan malam duk sun zou auren kowa sai murna yakeyi da farin ciki domin salma ta zama tauraruwa acikin yaransu ita kadai ce ta auri mai arziki kaf dangin su!"Domin haka ne sukaji dadi sosai komai an gudanar na al'ada wanda karfi bai fi jiki ba."Da hakan aka kammala komai su Hajiya Raliya su ka koma."
"Yayin da karime da sauran sa'ointa ke ta kaiwa da komowa sai murna sukeyi suna duban kayan na arziki da basu da adadi."A gefe ko Baba larai sai faman cika takeyi tana batsewa tana hararen karime da bata ma san masarda innarta ke toyawa ba dan tuni ta kama salma ta rike gam.''Da dai larai ta fahimci karime bata kulata ficewa tayi daga sashen zuciyarta cike da bakinciki da takaicin wannan kayan da aka kawo ga karime sai wani rawar kai!"takeyi domin rashin sanin ciwon kai!"Amma zata dawo ta sameta sai ta ci mutuncinta.!"
"Salma ko tun safe tabar gidan taje gidan wata qawarta Zara'u, Saboda kada masu kawo lefen su sameta."
"Dr.Salman da jameel da sauran abokan su ne zaune amajalisa yayin da suke ta masa tsiya domin yaki ya amince suyi pre-wedding pics."Sam yaki ya amince saboda yace haram ne ba kyau kuma baya son ya tallata matan sa aduniya yana kishin su!"Da hakan dai suka gama cike ciken Wedding I.v din su suka wuce domin aiwatar da wasu lamurra nasu shi da jameel."
"A gefen minal ko da lauje acikin nadi domin ita kam gaskiya tana son Dr.salman matuka amma *BAK'AR AK'IDA* ta tsanar talaka tayi mata tsirou a zuciya da take ganin bazata iya zama da salma a matsayin kishiyarta!"Ai wannan wulaqanci ne domin tafi karfin tayi kishi da 'yar talakawa!"Domin wannan babban ci baya ne agareta kuma abin kunya ne da fad'a familynsu."
"Salma da murmushi ta kalli karime ta ce"Sannu karime yau kece asashen namu?"
"Ni ce Salma dan Allah kiyi hakuri sai yanzu na gane hassada ga mai rabo taki ce!"Wallahi ina sonki salma Innata ce ke ta kitsa min komai duk abinda nikeyi miki ita ke sakani!"Ko yanzu aboye ne na shigo inda kuke,"Amma yanzu nasan cewa "Karya fure takeyi bata 'ya'ya!"kiyi hakuri!Bamu kyauta muku ba ni da iyayena kuna zaune da mu da zuciya daya mu kuma muna jin haushinku!"Salma ki yafe mana"Kinji 'yar uwata!"
"Hannunta ta kamo ta hade da nata, tace babu komai karime na yafe miki komai ya wuce duk abinda kike min ban taba kallonki da ko daya ba!Harma su inna da baba"Nasan Sharrin zuciya ne!"
"Karime murmushi tayi jikinta asanyaye tare da jin kunyar salma ta ce nagode 'Yar uwata!"
"Babanmu ya ce min aurenki za'ayi makon nan mai zuwa?"
"Eh in shaa Allah karime,"Ki tayani addu'ah domin ni har yanzu ina jin tsoro da fargabar shiga gidan Dr.Salman saboda *BAK'AR AK'IDA* Irin ta danginsa kinsan sun tsani talaka ya rabe su!"
"Babu abinda zai faru da ke Salma sai alheri da jin dadin rayuwa."
Allah ya sanya alheri ina tayaki murna domin salman mutumen kirki ne, Allah ya sa ayida mu"
"Ameen,Karime nagode Allah ya nuna mana naku!"Shin Ina Dan ummarunki ne?Ko yayi tafiya ne? na daina ganinsa!""
"Mtwssssa dan Allah ki daina min zancen sa!" Yanzun nan ma na koreshi! domin ni nagaji da gafara sa banga qaho ba!"Mutum kullum ta-tau kamar jijiya!"Nikam gaskiya nagaji bazan iya rayuwa da shi ba ahakan!"baya iya tabuka min komai!"Kinga fa ko irin... !"
"Haba karime!"Salma tace tare da dakatar da ita!"Meye aibun shi!?Sai naga yana da mutunci kirki ilimi da addini!"
"Aibun shi matsiyaci ne!"Salma.''Me akeyi da talauci ai ko mu da ke zaune acikinsa kullum muna addu'ar Allah ya fidda mu daga cuta ya bamu lafiya!"Ke kinyi arziki Allah yayi maki gyadar dogo saura ni da sauran!"Kin isa barkah shiyasa nazo in tayaki murnar barka da arziki salma!"
"Menene na barkah kuma aciki Karime?"Dama ace kin min barka ne kan nasamu miji nagari zanyi aure in tufawa kaina asiri da nafi jin dadin hakan!"Amma ace barka kike min ta samun mai arziki!?Nikam wannan baya cikin tsarina!"Ya kamata Ki gane shi samu da rashi duk na Allah ne!"Yaushe kika koyi wannan *BAK'AR AK'IDA* ta banzah!"Kina yar talaka kice ke sai mai kudi kike so karime!?"To wallahi kinyi babban kuskure dan ba'ayiwa Allah wayo masani ne akan dukkan komai!"Kuma shi ne mai bayarda mulki da arziki ga wanda yaso!"Idan Allah ya tashi jarabtarki sai yabaki mai kudin karshe kisha wuya!"Ni kaina da kike gani wai zan auri salman wallahi Allah ne shaidata ni kudin shi baya agabana!Kuma naso ace a talauce zan aure shi daga baya muyi arziki atare nafi son hakan!"Kuma ko yanzu Allah na iya maida shi talaka kamar mu!"Dan haka kiji tsoron Allah ki so mai sonki da zuciya daya karime!"Salma tace fuskarta a daure cikin rashin jin dadin abinda karime tayiwa Dan ummaru!"
"Cikin yanayin nadama ta dago kanta zuwa gareta tace na fahimceki salma Allah ya yafe min nasan nayi kuskure abaya kudi ne kawai agabana,Tare da rudi na innata,Hakika ta daurani akan tafarki marar kyau!" sai yanzu na gane da kika fargar da ni gaskiya!"Kuma in shaa Allahu zan nemo shi in bashi hakuri!"Amma salma duk da hakan Danummaru ya cika matse hannu sosai ya kamata ace dan mayukan nan su turare da sauran yan kayan nan na makwalashen kanti da naga ana kasowa abokaina nima yayi min inji dadi komai dai rashinsa yafi karfin su dan iya kudin ka iya shagalinka ne karfi baifi jiki ba!"Ai wannan ma wani abu ne!"saboda rayuwa ce da zamani yazo mana da ita salma!"
"Hmnnnn karime kenan awani wurin kina da gaskiya amma ki qara yin hakuri watarana sai labari."Yanzu kiyi kokari ki bashi hakuri saboda baki kyauta ba kuma shawarata ita ce ki damu da wanda ya damu da ke!"Ki roki Allah ya hada arzikin ku."
"To salma zanyi kokarin yin hakan nagode zan wuce kada inna ta nemeni, amma salma nifa kallonki nike tayi tun dazu naga sai wani sheqi kikeyi kinyi kyau hakan...kamar wata sabuwa ba ke ba?"Ko duk amarchin ne wallahi ba karya kin canja sai haske kikeyi kamar tauraruwa?"Karime ta ce harda shafa fuskar salma da ke walwalniya kamar madubi tayi (smooth)"
"Murmushi tayi tare da duban karime ta ce baki rabo da abin dariya ki wani ce kamar bani ba,Nice dai salmarki...."To daman Hajiya Raliya qawar Maman salman ce ta kaini gidan wata Aminiyar su hamshaqiya kuma kwararriya Mai sayarda komai da ya shafi jiki wato Hajiya Amina Na'amore duka yau kwana na Hudu ne ina zuwa amma ni kaina naga canji wato ita aikinta yana kyau, sha yanzu magani yanzu ne"
"Haba gaske dai kice naira ce kwance a fuskar ki."Ke kam kin fara komawa kalar masu kudi!"Yanzu nima ina so in gyara tawa fuskar ko zan haska ranar aurenki!"Zatayi min?"
"Eh mana ai matar batada matsala!"Ga kayanta da sauki da rahusa, ga aiki kuma ko'ina tana tura kayanta, kedai bari gobe zamuje tare idan aka qare min sai tayi miki ni zan biya kudin naki"
"Yawwa salma nagode."Bari inyi hanzari n shiga gida nabaro inna zata daura sanwa."Niema muje in taya Inna aiki ta fita da jimawa!"To muje sai gobe idan nazo!"To yayi Allah ya kai mu."In ji salma.
"Amin karime tace Nagode Sannan tayi sallama da Inna Baraka ta wuce sashen su cikin jin dadi."
"Bari kawai Abban minal yaya mai gado ta nuna min bani kowa!"Kuma bani bakin komai ni da 'yata a rayuwarta!"Duk fa abinda na labarta maka shi ne ya faru!"Babu abinda bata ce mana ba!"Akan salman ai d'a baifi d'a ba!"Saboda wata can talakar banza marar gata!"Za'a wulaqanta min minal!"Abinda bazai taba yuyuwa ba ne domin bazan dauki raini!"Ba awurin kowa wallahi!"
"Numfasawa yayi bayan zurfin tunanin da yayi akan zantukan Hajiya zainab din."sannan ya ce"Naji kuma dukkan abinda ya faru!" Gaskiya abin ba dadi amma kisani yadda muke kare lafiyar Minal, haka itama kariyar lafiyar salman takeyi!"Ya kamata muyi musu uzuri zainab!Da salman da minal duk daya ne ya kamata abasu abinda suke so aimasu adalci!"Kada zuciya da saurin fushi yasa muyi da na sani...!"
"Haba!Abban minal wane Dana sani kuma!? Ai ana yinsa ne idan ana tare!Kuma ni minal nasani kamar yadda itama da d'anta tafi damuwa!"Na riga na fada mata wallahi bani ba ita kuma minal bazata taba auren d'anta ba"Domin bazata taba zama da ' Yar matsiyatah amatsayin kishiyarta ba!"Dan haka dole ne a fasa zancen auren.....!"
"Dakatah zainab...Bana son shirmen banza!"A fasa auren fa kinka ce!?To Saboda me!? Salman ne ya ce yafasa!?Ko ita minal din tace maki tafasa!?"
"Ai Ko basu fada ba ni na fada!"saboda ance labarin zuciya a tambayi fuska na hango farinciki kwance a fuskar salman Kasan daman shi ba so yakeyi ba!"Kuma yanzu mahaifiyar sa ta goya masa baya!"Maganin kar ayi kar afara!"Dan haka muma zamu ba minal hakuri ta tsaya jiran mai sonta ba wanda ita ke son sa ba!"Yanzu haka da kyar ni da Nidal,muka samu ta kwanta bacci ko zata samu sassauci!"
"Yanzu zainab meye zamu cewa mutanen da da muka gayyata!?Yanzu duk shirin mu ya zama na banza kenan!"A gaskiya dole ne mu samu mafita...........!"
🏻👸🏻
BAKAR AKIDA
©TASKAR NABEELA DIKKO
®PEN WRITERS ASSOCIATION
Page 81/85
_Dedicated to my little princess Mufeeda Ameenu😍 Allah ya nuna min ranar aurenki Amin._
________________________________
"Gidan malam Abu Sufyan ne cike da jama'ar binni da na qauye."
Ba kowa bane face Hajiya Raliya da jama'arta ta arziki da ta gayyato domin kawo kayan lefen salma saboda duk dangi Hajiya mai gado sunce su bazasu iya shiga wannan unguwa ta qauyawa talakawan da wasun su duk mayu ne!"A cewar su wai duk garin cin maganin arzikine talakawan ke komawa mayu!"Dalilin da yasa hajia Raliya ta nemo mutanen arziki suka kawo kayan da yawan su har baya faduwa babu kawai ce a ba'a saka aciki ba!"Dozin akwatuna biyu kalolin kayan sunfi dari su sarka jaka gyale da sauran su tamkar wani kanti har su gwala gwalai ba'a barsu abaya ba!"Kaya dai na arziki."Sai masha Allah."
"Tarba ta arziki da mutunci dangin Inna baraka sukayiwa su Hajiya Raliya."
"Yan uwan malam duk sun zou auren kowa sai murna yakeyi da farin ciki domin salma ta zama tauraruwa acikin yaransu ita kadai ce ta auri mai arziki kaf dangin su!"Domin haka ne sukaji dadi sosai komai an gudanar na al'ada wanda karfi bai fi jiki ba."Da hakan aka kammala komai su Hajiya Raliya su ka koma."
"Yayin da karime da sauran sa'ointa ke ta kaiwa da komowa sai murna sukeyi suna duban kayan na arziki da basu da adadi."A gefe ko Baba larai sai faman cika takeyi tana batsewa tana hararen karime da bata ma san masarda innarta ke toyawa ba dan tuni ta kama salma ta rike gam.''Da dai larai ta fahimci karime bata kulata ficewa tayi daga sashen zuciyarta cike da bakinciki da takaicin wannan kayan da aka kawo ga karime sai wani rawar kai!"takeyi domin rashin sanin ciwon kai!"Amma zata dawo ta sameta sai ta ci mutuncinta.!"
"Salma ko tun safe tabar gidan taje gidan wata qawarta Zara'u, Saboda kada masu kawo lefen su sameta."
"Dr.Salman da jameel da sauran abokan su ne zaune amajalisa yayin da suke ta masa tsiya domin yaki ya amince suyi pre-wedding pics."Sam yaki ya amince saboda yace haram ne ba kyau kuma baya son ya tallata matan sa aduniya yana kishin su!"Da hakan dai suka gama cike ciken Wedding I.v din su suka wuce domin aiwatar da wasu lamurra nasu shi da jameel."
"A gefen minal ko da lauje acikin nadi domin ita kam gaskiya tana son Dr.salman matuka amma *BAK'AR AK'IDA* ta tsanar talaka tayi mata tsirou a zuciya da take ganin bazata iya zama da salma a matsayin kishiyarta!"Ai wannan wulaqanci ne domin tafi karfin tayi kishi da 'yar talakawa!"Domin wannan babban ci baya ne agareta kuma abin kunya ne da fad'a familynsu."