Sashe 1
Bakar Akida Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
BAKAR AKIDA🏻
©TASKAR NABEELA DIKKO
®PEN WRITERS ASSOCIATION
GABATARWA_ :"DUKKAN YABO DA GODIYA SUN TABBATA GA ALLAH UBANGIJIN BAYINSA,SALATI MARAS ADADI GA SHUGABAN HALLITA MANZON RAHMA DA ALAYENSA BAKI DAYA."
TSOKACHI: "WANNAN LITTAFI NA BAKAR AKIDA LABARI NE KIRKIRARRE KAGAGGE BANYI DOMIN WANI KO WATA BA."
SADAUKARWA:"GAREKU MASOYA DANGINA DA ABOKAINA INA MAKU FATAN ALKHAIRI😍
Page 1/5
Bismillahir rahmanir rahim
_____________________________
"Billahillazi!Salman kayi kadan ka auro salma ka kawo gidan nan a matsayin surukata!"Can dai inji su gada!"Ga yar arziki wacce ta gado shi tun kaka da kakanni kamar kai!Amma sai ka nacewa waccan mayyar yarinya yar gidan mayu masu shegen shiga ran tsiya!"Na rasa me ka gani ga salma wanda minal batada shi!"Ace karasa abin so sai wannan kodaddiyar yarinya yar matsiyata da kaf danginsu ba wanda ya taba mallakar keke bare babur!"To wallahi idan ni hjia mai gado ce na haife ka!Bazaka auri salma ba kaji na gaya maka!" Minal ce zabina kuma ita ce zaka aura tashi ba fashi kuma ka b'ace min da gani tun ban sassaba maka ba."Kar ka qara yimin zancen ta!"
"Salman dake gurfane gaban mahaifiyarsa ne ya dago kansa idonsa jajir kmr barkono ya ce,Allah ya huci zuciarki Ammina in shaa Allah zan ga nayi kokarin hana zuciata abinda ta ke so zanbi umirniki(Umurnin Uwa)ya qarashe maganar cikin kunar rai!"
"Hanyar waje Hjia mai gado ta nuna masa da hannunta cikin bacin rai ta ce Salman tashi ka tafi ko zan samu nutsuwa wato ni zaka fadawa har ynzu salmar ce aranka ba minal bako!?" get out!'
"Very sorry Hajiya in sha Allah hakan bazai sake faruwa ba!"Inji salman cikin ladabi!"
"Tashi yayi sum-sum ya wuce yabar falon saboda yasan halin Hjiarsa sarai fagen iya masifa ta kwarai sosai!"Dakinsa ya nufa yana mai zubda hawaaye ciwon son salma ne ya addabe sa!" da kuma tsantsar tsanar minal ne dauke a qalbinsa!"A gaskiya shi kam bAzai iyA dAina son salma ba har karshen rayuwar sa!"Dan kuwa ita ce zabinsa ba minal ba marar kunya!"Ya rasa a ina wannan BAK'AR AK'IDA tasamo asali acikin afamly dinsu!"Da har suke cigaba da Assasata!."Fatan shi Allah yasa su gane gaskiya!"
"Zaune ta ke a Dan madaidaicen tsakar gidansu mai kama da kango tana jika gari da suga domin Karin safe."
"A gefen ta wata dattijuwa ce ke daka Tim tin tuuum in banda sautin karar turmi da tabarya ba abinda ke tashi,wurin!"
"Wacce ke shan gari da sugan ce ta taso ta qaraso gurin da matar nan mai dakan ta ke."
"Ta ce Inna kawo in idar da surfen kije ga naki gari can na rage maki."Kinga dakan nan baki ko iya yinsa sosai."
"Matar wacce aka kira da inna ta ce kibarshi kawai salma wannan dakan sai ni naga ke gabaki daya kirarki ta fita daban da takowa agidan nan kamar yanaynki da jikinki basa jure wahala!" Wallahi ina tausayin ki salma!"Inna ta karashe maganar tana mai zubda hawayen da take gogewa da gefen zaninta."
"Murmushi Wanda yafi kuka zafi Salma tayi tace,Haba Inna ki daina damuwa da halin rayuwar mu haka Allah ya so kuma hakan ya ke son ganinmu karfa ki manta kaf danginmu ba mai arziki kedai mu godewa Allah da yayi mana arzikin samun rai da lafiya masu arziki nawane adunia suna da dimbin dukia amma sun rasa rayukansu da lafiyarsu kinga basu da anfani Innata saboda haka Allah yai mana komai arayuwa.!"Kawo tabaryar jeki ki karya zan cigaba!"
Inna miqawa salma tabaryar tayi tana mai tausayawa rayuwar 'yarta!"Wacce aka Haifa acikin talauci ta girma acikinsa fatan ta Allah ya sa ta mutu acikin arziki!"Saboda batason tasha wuya da azabar rayuwa da suka gani!"
"Salma ko cigaba da dakan tayi da kyar take dakawa saboda ita sam bata iyawa karfin haline takeyi domin ta taimakawa innarta da tsufa ya tasowa sanadin talauci domin tuni tabarya ta tsotse mata kurciya takoma tsuhuwa Dan kuwa wannan ce kadai hanyar cin abincinsu wato surfe."
" Zaune take ta daura kafa daya kan daya cikin shigar wasu mugwayen English wears wando da riga Kore, matsatsun gaske, acikin qayataccen falon ta da in ban da qamshi da sanyi A.C ba abinda ke tashi acikin sa," earpiece sanye a kunnenta tana sauraren waqoqin justin bieber."
"Sai wani bin waqar takeyi tana lumshe ido,A gefe 'yan aikinta ne zaune suna kallon t.v a qasan kafet."
"Falmata ta ce,ranki shi dade lokacin sallaah yayi muje muyi sallah!?
"Mtwsssss ke wace irin jaaka ce bazaki bari idn kinje gidan ubanki ba, kiyi sallolinki ko sallah aka kawoki kimin ne?"
"A ah falmata tace, cikin firgici!"Kiyi hakuri Anty minal!"
"Okay!Meye aciki idan kin koma gida saiki kiyi gabadaya mana."Ni kaina ma nafison in hada uku ko hudun inyi at dsame time yafi sauqi ko ba hakaba."In ji Meenal
"Hakane Anty!"Su ka amsa mata dukan su falmata da lami suna duban junan su."
"Am lami je ki part din mum kice ina kiranta."
"To Anty,
Lami ta ce, ta wuce domin Isar da saqon uwar gijiyarta cikin sauri!"
"Meenal jiyowa tayi wurin falmata tace,Ke jaaka awuni sallah nawa ma akeyi na manta nace Hudu uku ne ko?"
"Cikin ladabi falmata ta ce,A'ah Anty,biyar ne awuni."
"To ya akeyi Dan naga ke kin iya ita waccan banzar kmr jahilace!"(Lami)
"Akwai Subhi ana raka'a biyu,Zuhr,Asr raka'a Hudu,sai magrib 3 da isha itama hudu akeyi Anty."In ji falmata cikin nutsuwa saboda ita tanada dama fagen ibadah."
"Okay"Naji abin ashe da yawa nikam biyu nikeyi kowacce."
"Toh!Falmata tace cikin mamaki azuciyrta duk da tasan cewa ita kanta bawani ilimi ne da ita ba Amman tasan ya zatayi sallah amma ita minal din kmr ba diyar musulmai ba koda yake baza tayi mamaki ba tunda ba a nigeria tayi rayuwarta ba duk a London tayi karatunta harta gama cikin yahudawa tasamo dunia kam amma komai bata sani ba ga me da lahirarta."Allah ya shirya tace azuciyarta."
"Minal ko sai waqa takeyi tana shan shishaa tana rausayawa."
BAKAR AKIDA👸🏻👸🏻👸🏻
©TASKAR NABEELA DIKKO
®PEN WRITES ASSOCIATION
Page 6/10
An karbou daga Abih hurarah(R.A) ya ce,"Manzo Allah_ _(SAW) ya ce, "Kashedin ku da zato domin shi zato zance ne na karya."_
_Bukhari da Muslim ne suka ruwaito._
________________________________
ASALIN SU
DR.SALMAN
"Dr.Salman Tahir Galadima yaro ne matashi kyakkyawa wanda ya ke da shekaru 30 cip a dunia."
"Yayi karatu a qasar India inda ya zama babban likita Wanda ayanzu hakan ya na aiki GENERAL HOSPITAL da ke garin ARGUNGU."
"Mahaifinsa Alh Tahir galadima ya rasu tun yana qaramin yaro sunan mahaipiyrsa hajia Bilkisu(Mai gado) sai qañwarsa daya tal adunia wato Rukayya mai sunan kakar su mahaifiyar marigayi tahir wacce sukeyiwa alkunya da (Ilhaam)"
"Salman ya samu so da kauna da duk wani gata awurin iyayen sa,Sai dai hkn baisa shi karya alqawarin da ya daukarwa mafinsa ba na zama yaron kirki kuma da nagari."Saboda mahaifinsu mutumen kirki ne kuma hamshaqen mai kudi Wanda yakeda katafaran gida anan G.R.A ARGUNGU ga shi mutum mai kyauta da ilimi ga taimako da tausayin mutane."Dukkan halayensa na kirki ba Wanda salman bai dauka ba akullum burin shi ya zarce ayyukan alheri da mahaifinsa yayi arayuwarsa."
"Hajia bilkis(mai gado) macece mai son mulki da takama sam batason talaka ya rabeta saboda iyayenta da danginta masu arzikin gaske ne shiysa ita bata son mu'amula da marar shii."Kaf halayenta iri daya daya ne da yarta kuma autarta Ilhaam."Ta gado halayen hajiya mai gado har ta zauce." Shiyasa akullum salman ke kokarin tunatar da su wasiyyar Alh tahir tun kan yavar duniya da su ji tsoron Allah su daina wulaqanta mutane amma ina abin ya riga da ya zame masu jiki."Sai addu'ah."
BARRISTER MINAL
"Minal Maina Sadauki 'yarinya ce mai masifar kyau ga ta da jiki mai kyau sai dai tsabar rama da tayi mata yawa ke sa ta muni."
"Minal 'yar qanwar hjia ce uwa daya uba daya, mama Zainab wacce ke auren Justice Maina sadauki da ke zaune a garin Argungu."
"Barrister Meenal Maina tayi karatun low a london Wanda a yanzu hakan lawyer ce mai zaman kanta da ta ke aiki a high court Argungu."Tana da shekaru 26 a duniya,Sangartacciya ce ta gaske batada ilimin komai da ya danganci addini kasancewar basu wani Dade da dawowa gida Nigeria ba,"Dan tunda aka haifeta suna London har sai da ta kammala karatunta suka dawo."A Yanzu ne ake koya mata abubuwa da dama dangane da addini dan ko sallah bata iya ba!" kuma bata ma wani maida hankali sosai Dan tana ganin tafi karfin malamman na ta."Saboda minal batada kunya ga rashin ji da shigar banza Sam bata da kama da diyan musulmi tun kan halayenta da dabi'arta,suturarta,da maganarta na marasa tarbiya ne komai take so ko ta ga dama shi takeyi kasancewarta 'ya daya da Allah yabawa iyayenta kuma suna sonta sosai shiyasa takeyin duk abinda ranta ke so agidansu da garin Argungu baki daya."
SALMA MAI WALDAH
"Salma Abu sufyan (Mai waldah) yarinya ce Matashiya black beauty ce mai kyaun diri ga ta kamila mai hankali ga ilimin addini da mutunci tasan girma da mutucin manya." kasancewar da kyar ta samu ta kammala karatunta na sakandare dan ko basuda kudi ko kadan bare ta cigaba da karatunta duk da taso hakan amma ba hali!"Ba kowa ba ce,"Ba diyar kowa ba ce face bayin Allah da su ke zaune acikin tufin asirin Allah Sam gidansu salma baiyi kama da in da mutane ke rayuwa ba,tamkar wani kango haka yake kuma a hakan suke tafiyar da rayuwar su da sauran jama'ar gidan saboda lungu biyu ne da na babanta da kanin babanta da iyalensu duka Suna zaune acikin gidan su da ke garin Argungu a unguwar Allugu Wanda idan ba gidan 'yan walda ko surfe akace ba, bama za a gano gidansu salma ba a unguwar.saboda waldah gadon gidan su ne,wanda duk mazan gidan shi ne sana'ar su matan kuwa surfe ne aikin su."
"Malam Abu Sufyan mai walda shi ne babanta sai Innarta Baraka ita kadai ce Allah ya qaddari ta tsaya acikin yaran da suke samu saboda inna baraka wabi takeyi da ta haihu bayan lokaci kadan yaran komawa(rasuwa)sukeyi."A hakan kowa ke tafiyarda rayuwarsa agidan mata suna dakau(Surfe) yara da manya wasu talla,maza ko suna fitaa faci da walda saboda, su ne sana'a ta gadon gidansu salma."
©TASKAR NABEELA DIKKO
®PEN WRITERS ASSOCIATION
GABATARWA_ :"DUKKAN YABO DA GODIYA SUN TABBATA GA ALLAH UBANGIJIN BAYINSA,SALATI MARAS ADADI GA SHUGABAN HALLITA MANZON RAHMA DA ALAYENSA BAKI DAYA."
TSOKACHI: "WANNAN LITTAFI NA BAKAR AKIDA LABARI NE KIRKIRARRE KAGAGGE BANYI DOMIN WANI KO WATA BA."
SADAUKARWA:"GAREKU MASOYA DANGINA DA ABOKAINA INA MAKU FATAN ALKHAIRI😍
Page 1/5
Bismillahir rahmanir rahim
_____________________________
"Billahillazi!Salman kayi kadan ka auro salma ka kawo gidan nan a matsayin surukata!"Can dai inji su gada!"Ga yar arziki wacce ta gado shi tun kaka da kakanni kamar kai!Amma sai ka nacewa waccan mayyar yarinya yar gidan mayu masu shegen shiga ran tsiya!"Na rasa me ka gani ga salma wanda minal batada shi!"Ace karasa abin so sai wannan kodaddiyar yarinya yar matsiyata da kaf danginsu ba wanda ya taba mallakar keke bare babur!"To wallahi idan ni hjia mai gado ce na haife ka!Bazaka auri salma ba kaji na gaya maka!" Minal ce zabina kuma ita ce zaka aura tashi ba fashi kuma ka b'ace min da gani tun ban sassaba maka ba."Kar ka qara yimin zancen ta!"
"Salman dake gurfane gaban mahaifiyarsa ne ya dago kansa idonsa jajir kmr barkono ya ce,Allah ya huci zuciarki Ammina in shaa Allah zan ga nayi kokarin hana zuciata abinda ta ke so zanbi umirniki(Umurnin Uwa)ya qarashe maganar cikin kunar rai!"
"Hanyar waje Hjia mai gado ta nuna masa da hannunta cikin bacin rai ta ce Salman tashi ka tafi ko zan samu nutsuwa wato ni zaka fadawa har ynzu salmar ce aranka ba minal bako!?" get out!'
"Very sorry Hajiya in sha Allah hakan bazai sake faruwa ba!"Inji salman cikin ladabi!"
"Tashi yayi sum-sum ya wuce yabar falon saboda yasan halin Hjiarsa sarai fagen iya masifa ta kwarai sosai!"Dakinsa ya nufa yana mai zubda hawaaye ciwon son salma ne ya addabe sa!" da kuma tsantsar tsanar minal ne dauke a qalbinsa!"A gaskiya shi kam bAzai iyA dAina son salma ba har karshen rayuwar sa!"Dan kuwa ita ce zabinsa ba minal ba marar kunya!"Ya rasa a ina wannan BAK'AR AK'IDA tasamo asali acikin afamly dinsu!"Da har suke cigaba da Assasata!."Fatan shi Allah yasa su gane gaskiya!"
"Zaune ta ke a Dan madaidaicen tsakar gidansu mai kama da kango tana jika gari da suga domin Karin safe."
"A gefen ta wata dattijuwa ce ke daka Tim tin tuuum in banda sautin karar turmi da tabarya ba abinda ke tashi,wurin!"
"Wacce ke shan gari da sugan ce ta taso ta qaraso gurin da matar nan mai dakan ta ke."
"Ta ce Inna kawo in idar da surfen kije ga naki gari can na rage maki."Kinga dakan nan baki ko iya yinsa sosai."
"Matar wacce aka kira da inna ta ce kibarshi kawai salma wannan dakan sai ni naga ke gabaki daya kirarki ta fita daban da takowa agidan nan kamar yanaynki da jikinki basa jure wahala!" Wallahi ina tausayin ki salma!"Inna ta karashe maganar tana mai zubda hawayen da take gogewa da gefen zaninta."
"Murmushi Wanda yafi kuka zafi Salma tayi tace,Haba Inna ki daina damuwa da halin rayuwar mu haka Allah ya so kuma hakan ya ke son ganinmu karfa ki manta kaf danginmu ba mai arziki kedai mu godewa Allah da yayi mana arzikin samun rai da lafiya masu arziki nawane adunia suna da dimbin dukia amma sun rasa rayukansu da lafiyarsu kinga basu da anfani Innata saboda haka Allah yai mana komai arayuwa.!"Kawo tabaryar jeki ki karya zan cigaba!"
Inna miqawa salma tabaryar tayi tana mai tausayawa rayuwar 'yarta!"Wacce aka Haifa acikin talauci ta girma acikinsa fatan ta Allah ya sa ta mutu acikin arziki!"Saboda batason tasha wuya da azabar rayuwa da suka gani!"
"Salma ko cigaba da dakan tayi da kyar take dakawa saboda ita sam bata iyawa karfin haline takeyi domin ta taimakawa innarta da tsufa ya tasowa sanadin talauci domin tuni tabarya ta tsotse mata kurciya takoma tsuhuwa Dan kuwa wannan ce kadai hanyar cin abincinsu wato surfe."
" Zaune take ta daura kafa daya kan daya cikin shigar wasu mugwayen English wears wando da riga Kore, matsatsun gaske, acikin qayataccen falon ta da in ban da qamshi da sanyi A.C ba abinda ke tashi acikin sa," earpiece sanye a kunnenta tana sauraren waqoqin justin bieber."
"Sai wani bin waqar takeyi tana lumshe ido,A gefe 'yan aikinta ne zaune suna kallon t.v a qasan kafet."
"Falmata ta ce,ranki shi dade lokacin sallaah yayi muje muyi sallah!?
"Mtwsssss ke wace irin jaaka ce bazaki bari idn kinje gidan ubanki ba, kiyi sallolinki ko sallah aka kawoki kimin ne?"
"A ah falmata tace, cikin firgici!"Kiyi hakuri Anty minal!"
"Okay!Meye aciki idan kin koma gida saiki kiyi gabadaya mana."Ni kaina ma nafison in hada uku ko hudun inyi at dsame time yafi sauqi ko ba hakaba."In ji Meenal
"Hakane Anty!"Su ka amsa mata dukan su falmata da lami suna duban junan su."
"Am lami je ki part din mum kice ina kiranta."
"To Anty,
Lami ta ce, ta wuce domin Isar da saqon uwar gijiyarta cikin sauri!"
"Meenal jiyowa tayi wurin falmata tace,Ke jaaka awuni sallah nawa ma akeyi na manta nace Hudu uku ne ko?"
"Cikin ladabi falmata ta ce,A'ah Anty,biyar ne awuni."
"To ya akeyi Dan naga ke kin iya ita waccan banzar kmr jahilace!"(Lami)
"Akwai Subhi ana raka'a biyu,Zuhr,Asr raka'a Hudu,sai magrib 3 da isha itama hudu akeyi Anty."In ji falmata cikin nutsuwa saboda ita tanada dama fagen ibadah."
"Okay"Naji abin ashe da yawa nikam biyu nikeyi kowacce."
"Toh!Falmata tace cikin mamaki azuciyrta duk da tasan cewa ita kanta bawani ilimi ne da ita ba Amman tasan ya zatayi sallah amma ita minal din kmr ba diyar musulmai ba koda yake baza tayi mamaki ba tunda ba a nigeria tayi rayuwarta ba duk a London tayi karatunta harta gama cikin yahudawa tasamo dunia kam amma komai bata sani ba ga me da lahirarta."Allah ya shirya tace azuciyarta."
"Minal ko sai waqa takeyi tana shan shishaa tana rausayawa."
BAKAR AKIDA👸🏻👸🏻👸🏻
©TASKAR NABEELA DIKKO
®PEN WRITES ASSOCIATION
Page 6/10
An karbou daga Abih hurarah(R.A) ya ce,"Manzo Allah_ _(SAW) ya ce, "Kashedin ku da zato domin shi zato zance ne na karya."_
_Bukhari da Muslim ne suka ruwaito._
________________________________
ASALIN SU
DR.SALMAN
"Dr.Salman Tahir Galadima yaro ne matashi kyakkyawa wanda ya ke da shekaru 30 cip a dunia."
"Yayi karatu a qasar India inda ya zama babban likita Wanda ayanzu hakan ya na aiki GENERAL HOSPITAL da ke garin ARGUNGU."
"Mahaifinsa Alh Tahir galadima ya rasu tun yana qaramin yaro sunan mahaipiyrsa hajia Bilkisu(Mai gado) sai qañwarsa daya tal adunia wato Rukayya mai sunan kakar su mahaifiyar marigayi tahir wacce sukeyiwa alkunya da (Ilhaam)"
"Salman ya samu so da kauna da duk wani gata awurin iyayen sa,Sai dai hkn baisa shi karya alqawarin da ya daukarwa mafinsa ba na zama yaron kirki kuma da nagari."Saboda mahaifinsu mutumen kirki ne kuma hamshaqen mai kudi Wanda yakeda katafaran gida anan G.R.A ARGUNGU ga shi mutum mai kyauta da ilimi ga taimako da tausayin mutane."Dukkan halayensa na kirki ba Wanda salman bai dauka ba akullum burin shi ya zarce ayyukan alheri da mahaifinsa yayi arayuwarsa."
"Hajia bilkis(mai gado) macece mai son mulki da takama sam batason talaka ya rabeta saboda iyayenta da danginta masu arzikin gaske ne shiysa ita bata son mu'amula da marar shii."Kaf halayenta iri daya daya ne da yarta kuma autarta Ilhaam."Ta gado halayen hajiya mai gado har ta zauce." Shiyasa akullum salman ke kokarin tunatar da su wasiyyar Alh tahir tun kan yavar duniya da su ji tsoron Allah su daina wulaqanta mutane amma ina abin ya riga da ya zame masu jiki."Sai addu'ah."
BARRISTER MINAL
"Minal Maina Sadauki 'yarinya ce mai masifar kyau ga ta da jiki mai kyau sai dai tsabar rama da tayi mata yawa ke sa ta muni."
"Minal 'yar qanwar hjia ce uwa daya uba daya, mama Zainab wacce ke auren Justice Maina sadauki da ke zaune a garin Argungu."
"Barrister Meenal Maina tayi karatun low a london Wanda a yanzu hakan lawyer ce mai zaman kanta da ta ke aiki a high court Argungu."Tana da shekaru 26 a duniya,Sangartacciya ce ta gaske batada ilimin komai da ya danganci addini kasancewar basu wani Dade da dawowa gida Nigeria ba,"Dan tunda aka haifeta suna London har sai da ta kammala karatunta suka dawo."A Yanzu ne ake koya mata abubuwa da dama dangane da addini dan ko sallah bata iya ba!" kuma bata ma wani maida hankali sosai Dan tana ganin tafi karfin malamman na ta."Saboda minal batada kunya ga rashin ji da shigar banza Sam bata da kama da diyan musulmi tun kan halayenta da dabi'arta,suturarta,da maganarta na marasa tarbiya ne komai take so ko ta ga dama shi takeyi kasancewarta 'ya daya da Allah yabawa iyayenta kuma suna sonta sosai shiyasa takeyin duk abinda ranta ke so agidansu da garin Argungu baki daya."
SALMA MAI WALDAH
"Salma Abu sufyan (Mai waldah) yarinya ce Matashiya black beauty ce mai kyaun diri ga ta kamila mai hankali ga ilimin addini da mutunci tasan girma da mutucin manya." kasancewar da kyar ta samu ta kammala karatunta na sakandare dan ko basuda kudi ko kadan bare ta cigaba da karatunta duk da taso hakan amma ba hali!"Ba kowa ba ce,"Ba diyar kowa ba ce face bayin Allah da su ke zaune acikin tufin asirin Allah Sam gidansu salma baiyi kama da in da mutane ke rayuwa ba,tamkar wani kango haka yake kuma a hakan suke tafiyar da rayuwar su da sauran jama'ar gidan saboda lungu biyu ne da na babanta da kanin babanta da iyalensu duka Suna zaune acikin gidan su da ke garin Argungu a unguwar Allugu Wanda idan ba gidan 'yan walda ko surfe akace ba, bama za a gano gidansu salma ba a unguwar.saboda waldah gadon gidan su ne,wanda duk mazan gidan shi ne sana'ar su matan kuwa surfe ne aikin su."
"Malam Abu Sufyan mai walda shi ne babanta sai Innarta Baraka ita kadai ce Allah ya qaddari ta tsaya acikin yaran da suke samu saboda inna baraka wabi takeyi da ta haihu bayan lokaci kadan yaran komawa(rasuwa)sukeyi."A hakan kowa ke tafiyarda rayuwarsa agidan mata suna dakau(Surfe) yara da manya wasu talla,maza ko suna fitaa faci da walda saboda, su ne sana'a ta gadon gidansu salma."