← Book details auren shehu Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 33 OF 34

Sashe 33

auren shehu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Babu wani abin sasantawa! Da tana so su sasan ta da ba ta shigo ciki ta na mana kuka kamar wacce aka aikowa sakon mutuwa ba! Ke kin san wacece Yakura! Ka sace min diya! Ka kai ta dokar daji! Ka katse mata karatun ta! Sai da ka tabbatar ka bata mata rayuwa sannan ka sako ta mota tsabagen zalinci! Tun da ta dawo ba mu kara gane kan ta ba, ta zame mana tamkar bakuwa, a haka ta yi renon ciki, sai da ta haihu za ka wani kwaso jiki cikin manyan kaya ka zo gare mu? Ka ga mun ma ka kama da matsiya ta? Ko kana tunanin za ka yaudare mu da wayewa ne....?"

Hawaye ke fita daga idanun Usman, cike da nadama ya furta

"Wallahilazim ba haka ba ne Hajiya, ba wannan ba ne munufa ta, na yi kuskure kuma na yi nadama, ku yafe min. A shirye na ke na dau duk wani hukuncin da za ki yanke, Amma kar ku raba ni da Zainab, wallahi ba zan iya rayuwa babu ita ba"

"Toh tantabara! Ai watannin da ka korota ba rayuwa ka ke ba ko? Gawa ne kai duk wannan lokacin hala? Tashi ka fitar min daga gida! Tashi ka fita!"

Cewar Ammy cikin daurewar Fuska. Nan su Halitta ta su ka shiga ba ta baki. Amma Ammy ta juya mu su baya. Haka kuma duk magiyar duniyar nan yayiwa Ammy da ta bari ya gana da Zainab ba, ya kuma dauki Shehu, Amma ina Ammy ta riga ta hau sama. Haka ya karaci hawayen sa ya fito ya tadda Umar jikin mota ya na jiran sa. Yanayin da ya ga Usman ya sa ko tambayar halin da ake ciki be yi ba, kawai mota su ka shiga in da Umar ya tada ya juya kan motar. Bakin gate Jauro ya cigaba da mu su fadanci har sai da Umar ya fito da kudi ya danka masa. Ya na godiya ya daga mu su hannu har su ka fice. Bayan tafiyar su abokin Jauro ke tambayar na shi kason, Jauro ya hana, cewa ya ke

"Kai me ya hana ka zuwa ka karbi na ka? Ka na ganin mota mai numfashi, da kuma irin manyan da ke jan motar amma ka yi fuska! Toh wallahi raban da na ga mota irin wannan ta shigo gidan nan tun Malam na da rai!"

"Yanzu dai ba za ka bani ko sisi ba?"

"Ko asi ban ba ka"

Cewar Jauro yayinda ya wuce abin sa ya na lissafa adadin dadin da zai ci da kudin sa.

*****

Har su ka kai hotel din su babu wanda ya tanka. Bayan sun yi fakin ne za su rabu Umar ya dube shi ya ce

"Kar ka damu Usman, komai zai daidaitu"

Murmushi Usman ya masa, sannan ya wuce ciki ba tare da ya iya ce masa komai ba. Umar ne ya masa order abinci ya sa aka kai masa har daki. Ganin yunwa na neman halaka sa ya sa ya dan caccaki abincin, Amma sam ya kasa sukuni bere ya runtsa, sai juyi ya ke akan gado. Ko da ya duba agogo ya ga sha biyu sai ya ta shi wuf, jallabiya ya sanya saman singiletin jikin sa, dakin Umar ya nufa kai tsaye.

Zainab kuwa tun tafiyar Usman ta shiga wani hali, zuwan shi ya fama mata ciwan da ta ke tunanin da ya fara warkewa. Ammy ce ta yi ta bata baki, ta kuma mata alkawarin kar da ta damu in dai Usman ne ba zai kara saka kafa gidan ba, ta masa korar kare. Maimakon ta ji sanyi cikin ran ta kamar yanda Ammy ke zato, sai ma dada saka ta cikin hali mai wuya ta yi.

Kwance ta ke bisa gadon ta, ta tsurawa Shehu ido amma a zahiri tunanin Baban sa ne ya addabi zuciyar ta. Tambayoyi kala kala ke yawo cikin kan ta, Shin me ya same shi har ya canza haka? Ya aka yi ya iya shiga irin na wayayyu haka? Me ya kawo sa wajan ta? Shin ya zo ya tafi da ita ko kuwa dai ya ji labarin ta haihu shi ne ya zo ya raba ta dan ta?

Tsigar jikin ta ne ya tashi yayinda ta ji makogaran ta ya bushe. Ta tashi ta yi, ta na neman ruwan da ta saba ajewa a dakin ta rasa, dole sai fita ta yi ta nufi kitchen neman ruwan sha.

Tun fitowar ta daga dakin ya lura da ita, yanayin duhun falon be sa ya kasa gane Zainab ba. Ta gaban shi ta gifta amma sam ba ta lura da shi har ta isa kitchen din. Hakan ya bashi damar shigewa dakin da ta fito daga cikin.
Ganin an bar kofar kitchen din wangale ba sakata bare a sa mukulli ya sanya ta jan tsaki. Ta yi saurin karasawa ta ja kofar ta rufe. Sai sannan tsoro ya kamata, ta yi saurin daukar ruwan gora ta shige ciki kamar wacce za ta arta a na kare.

Jin tahowar ta yayi sauri aje Shehu, ya koma bayan kofa ya tsaya. Ko da ta karaso ta ga kofar da ta rufe da hannun ta shi ma wangale, da gudu ta karasa ciki wajan Shehu, daukar shi ta yi ta na mai duba lafiyar sa, ta ga dai lafiya lau ya ke, sannan hankalin ta ya dan kwanta, babu mamaki tsabagen tunanin da ta ke yi ne ya sa ta yi zaton da ta fita ta rufe kofar. Kara aje Shehu ta yi, hannun ta dauke da ruwan da ta dauko ta karasa kofar dakin ta ja ta rufe. Nan su ka hada idanu, ta bude baki za ta saka masa ihu yayi saurin janyo ta jikin sa tare da hade bakin shi da na ta ya fara kissing din ta. Tun ta na kokarin kwacewa har jikin ta yayi sanyi ta yi lamo ta na ganin ikon Allah, kafin daga bisani ita ma din ta fara mayar masa da martani.

Kukan Shehu ne ya dawo da su daga cikin hayyacin su, Usman yayi baya da sauri yayinda ita kuma ta karasa wajan sa, cikin ran ta tana godewa Allah da ya kwace ta daga hannun Usman. Usman jingine jikin bango, cike da so da kauna ya ke duban ta yayinda ta dauki dan sa cikin tattali da rarrashi. Ba ta damu da ya na wajan ba ta sanya masa abin da ya ke bukata a baki, Shehu yayi saurin cafkewa ya shiga zuka dama abin da ya ke jira kenan. Yanda ya ga ta dan runtse idanu alamar ta ji zafi ya sanya shi motsawa kusa da ita da sauri ya na fadin

"Sannu Abu, da zafi ko?"
Sai a sannan ta tuna ashe fa ba mijin ta ba ne, ta yi saurin jan mayafi ta rufe kirjin ta, Manyan idanun ta ta watsa masa cike da harara ta furta

"Malam me ya kawo ka gidan nan tsakar dare haka? Yaushe ka fara haura katanga? Me ya kawo ka daki na?"

Daf da ita ya zauna hakan ya sa ta dada muskutawa domin ba da tazara a tsakanin su. Hakan ya kara sa Usman dada matsawa kusa da ita, ita ma din ta kara matsawa, haka su ka ta yi har ya kure ta jikin bango.

"Wai menene! Zan ma ka ihu wallahi!"

"Toh in kin min ihu an zo an gan ni dakin mata ta sai menene?!"

"Wacece matar ta ka? Idan ma kana shirin dawowa da ni wallahi gwara ma ka fidda rai! Ka riga ka sake ni, I don't care daya ne ko uku, babu ni babu kai"

"Saki kuma? Ni Usmanu na sake ki? Toh abin na ki kuma ya koma sharri ne Abu?"

Takaici ne ya sa ta kasa magana. Ganin ba ta da niyar tanka masa ya sake furta

"Yanzu dai menene shedar sakin da na mi ki fisabilillahi?"
Tashi ta yi a fusace har nono na fita daga bakin Shehu, ya dan saka kuka amma ko ta kan sa ba ta bi ba sai da ta dauko takardar da ya bata, ta aje masa, ya fi takardar da idanu. Cike da tsiwa ta kara da

"idan ka gama dubawa za ka iya fitar min daga daki!"

Takarda ya dauka ya buda, ganin abun da ke ciki ya sa shi dariya, tabbas zatan shi ya tabbata. Ganin yanda ya ke dariya ya sanya ran Zainab kara baci. Musammam da ta ji ya furta

"Shin ko sau daya kin bude takardar nan kuwa Abu, ko kuwa dai tsabagen ba a iya karanta ajami ba ne?"

Ba ta so ya san ba ta taba budewa ba saboda kar ya gane tsabagen tsoran yawan sakin da ya mata ya sa. Dan haka ta ba shi amsa da

"Na karanta mana da ban karanta ba ta ina zan san sakin da ka min?"
Ta karasa maganar tana mai dora Shehu bisa kafadar ta, domin ta samu yayi gyatsa. Idanun shi na mata dariya ya bude ta takardar ya ce

"Toh kuwa Abu sai dai wata takarda ki ka karanta ba wannan ba, dubi wannan da kyau ki gani, ban sani ba ko kin san yanayin rubutun Malam, Allah ya jikan sa da rahama, wannan rubutun shi ne duk da dai jinya ta sa be fita sosai ba"

Hannu na rawa Zainab ta karbi ta kardar, ko shakka babu rubutun ya fi kama da na dan koyo, kalma biyu ne kacal jiki, sai da ta nutsu da kyau ta gane menene ciki

"Zainab...... Amana...."

Fuskar ta cike da hawaye ta dago ta na duban sa. Usman be gushe ba ya furta
Chapter 33 · 0% Book details